← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 42 OF 100

Sashe 42

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Soyayya ta sake yin karfi a tsakanin ussein da bilkisu dan babu abinda barinsa gidansu bilkisu ya janyo sai tabarbarewar rayuwar bilkisu dan a tunanina ussein ya fara saduwa da bilkisu batare da aure ba ni kaina alokacin naso ace iyayenta sun barta ta aureshi tunda ita taji kuma tagani amman mutanen nan suka ki saboda kyamar talaka , dan da irin rayuwar da suke gara ace aure sukayi, bazan ta'ba mantawa ba wata rana bilkisu ta sameni tana kuka na tmbyeta bata boye min ba ta fada min ciki gareta nan take na shiga damuwa mai tsanani nace "haba bilkisu me yasa zaki sakewa nmj jiki haka ?bakya jin tausayin iyayenki da yan'uwanki bakya gudun ranar da ussein zai juya miki baya ?ina ta mata fad'a Kmr kanwata ta jini ita km tana kuka tace ."na taimaketa acire mata cikin nace babu ruwana bazan saka hannu a kashe rai ba ,muna cikin wannan halin hjy ta shigo ashe taji duk mgnr mu itama cewa tayi abarshi kar acire taje gida zata samu iyayenta sai ayi mgnr aure kawai abu ya bani mamaki kamar wasu yoroba tunda sune ake irin wannan rayuwar dasu sai kayi ciki zaa yi aure km su yin ciki ba wani aibu bane a wajensu murna ma zaayi da samunsa tun daga nan na fahimci duk abinda ussein yake da saka hannun hjy ciki ."

Tô tun daga ranar ban sake saka bilkisu acikin idanuna ba a she byn ta bar wajena ussein ya bata maganin zubar da ciki ta sha koda ta koma gida sai ciwon ciki kwana tayi tana murkususu ciwo har garin allah ya waye ,cikin yaki fita ga ciki yaki daina ciwo iyayenta dai suka gaji suka kira doctor ya dubata byn ya gama dubata ya rubuta mata scan tô a wajen scan ne likita yaga ciki a mahaifarta tunda likita ya soma bayani mahaifiyarta ta rikice ta dimauce ta kasa gane takamaiman abinda yake fada ganin ta rude yace mata wani abu ya gani me kama da gas a mahaifarta amman ta kira wani daga gida yazo nan ta kira Aisha yayar bilkisu hankalinta a tashe  tazo ta samu hjy rahma a reception zaune tayi  tagumi bilkisu zaune a gefenta cikin tsoro da fargaba scan taso cikin ya fita cikin sauki batare da kowa yasani ba hjy rahma  tace Aisha tashiga taji me doctor yake nufi da gas din da ya gani a mahaifar bilkisu ta shiga nan likita ya fad'a mata komai itama tashin hankali tashiga mai tsanani amman sai ta boye ta fito tana cewa uwar ulcer ke damunta nan hankalin mahaifiyarsu ya dan kwanta suka koma gida ."

Aisha ta kira bilkisu zuwa gidanta tana qarasowa bata tsaya wata wata ba ta rufeta da duka sai datayi mata mai isarta kamar zata kasheta sannan ta barta byn ta gama dukanta ta kira kaf yan dakinsu ta sheida  masu sannan  tasa akayi mata wankin ciki aka cire cikin lokacin da hjytr ussein taji babu cikin Kmr ta mutu dan bakinciki har da kuka tayi an cire mata jikanta dan karfin halin irin nata har da tmbyr bilkisu tayi  wa ya cire  mata jikanta  ita km kuruciya  ta fad'a mata tun daga lokacin hjy ta tsani Aisha da yan gidansu bilkisu amman km tana son bilkisu ace warta bazata tsaneta ba dan tana son danta."

Hajiya rahma ta lura tun da bilkisu ta dawo daga gidan Aisha ta  warke sumul babu kwana ciwon ciki ta cigaba  da abubuwanta sai dai Aisha ta kira hjy rahma tace  kar a sake barin bilkisu fito koina  har sanda mubarak zai dawo a daura masu aure abinda bilkisu ta tsani ji kenan dan ta tsani mubarak tsana mai girma bata ma son ana yi mata maganarsa karki ce shima mubarak din mummuna ne dogo ne sosai Kmr ussein sai dai shi baki ne kyakkyawan gaske dan sai dana sa ta nuna min hotonsa a istagram
an kafa wa  bilkisu  takunkunmi rashin fita koina hatta islamiyya ta daina zuwa alokacin sai datayi wata uku babu shiga babu fita kawai tana gida zaune km babu  waya a hannunta an kwace da  wayar hjy rahma take mgn da mubarak ."

Ganin Kmr ta kwantar da kai suna soyayya da mubarak  Kmr gske yasa mahaifiyarta ta dauka ta cire komai aranta  kuma taji dadin hk kulawa da soyayyarta ya qaru ta  zaunar daita tayita nuna mata illar ussein tana qawata mata mubarak zataji dadin rayuwa agidan mubarak alokacin ta tmbayeta ta yarda zata auri mubarak tace eh ta amince wanda ba haka bane acikin ranta  wata rana yan'uwanta gbdy suka zo gidan suna zaune a falon mahaifiyarsu  yayanta abubakar wanda ya kasance first born  a dakinsu yace a barta ta cigaba da rayuwata ta koma islamiyya Kmr kowa dan lokacin saukar alqurninsu ya kusa duk da bata   zuwa baa cire sunanta acikin yan walima ba ba dan me ma zaa hanata rayuwa sbd wani matsiyacin banza  Aisha da sauran yanuwata mata sukace  a'a basu  yarda da fitarta  koina ba shi  km yace abashi dalili gbdy suka kasa sheida masa dalili su dan haka yace dole ta koma islamiyya nasan kuna tunani ko zata hadu da wannan yaron ne yace su barta dashi   idan ta isa tayi Kuskuren haduwa da ussein nan  take uwar  tace "ai bilkisunta ta canza bama zata kunyatata ba yanzu mubarak ne agabanta ."

Cikin satin aka dinka mata sabon uniform ta fara zuwa  islamiyya  Kmr  abun  arziki  sai dai aranar ta samu waya ta kirasa bai shiga ba sai ta kirani nan na tmbyeta kwana biyu da halin da take ciki ,bata boye min komai ba a karshe tace na fadawa ussein ya kunna wayarsa nace mata  "to! na qara da yi mata fad'a kar ta sake yarda dashi  tace taji nan fa suka sake din kewa da ussein soyayya  ta  sake karfi   har tafi nada da zara ta fito daga gida  suke haduwa dashi  km ni na tabbatarwa kaina  bazasu ga junansu su bar junansu  hk ba  tunda sun dandani juna dole sai sunyi wani abu duk da  shiedar zina tana da wahala  "to ! bazan manta ba ranar wata asabar da safe ta fito daga gidansu da nufin zuwa islamiyya kai tsaye dakin ussein ta zarto ashe ana biye daita abaya batasani ba har ta shiga dakinsa  tana shiga suka fara abinda suka saba suna cikin wannan halin sai shigowar mutanen gidansu  sukaji  tana rungume ajikinsa  aiko ranar munga tashin hankalin da bamu ta'ba gani ba ."

Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number  din 1438775094 Aishat abdullahi access idan  an tura sai a turawa wannan  09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

               Page 18

"wato  afa  akan dai  yarinyar nan ce  da  nazo  akanta  yar  kanin mijina  daya  mutu ya barmana amatsayin  riko  to malam  kamar yadda kasani  banason  yarinyar nan na  tsani  na  ganta  dan  ina ji ajikina  akwai  nasarori  da  anan  gaba  zata  iya  samu  domin soyayyar  da  mutane  suke  nuna mata  kamar  ma aikinka  na  farko bai  ci  ba, yanzu  haka samari  sunfi  biyar  da  suka  nuna suna sonta  sai  dai  dadin  abun  da zarar  sun  zo  lokaci  kad'an   sai su  gudu ."

    "to  ga  aikin  nan  yaci  zaki  ce kamar  aiki  bai ci ba , ai  haka  zasu dinga  zuwa  suna  'bata  mata lokaci  suna  wucewa  batare  da tasamu  wanda  zai  aureta  ba babu  fa  wanda  zai  like  mata acikinsu  sai  matsiyaci da  zarar masu  arziki  sunzo  zasu  gudu ."

"Ai  ni  ba  abinda nake só kenan ba ,ai  bana  son  ko  matsiyaci  ma yazo  wajenta   nafi  son  ta  qare  rayuwarta  a kaskance  a bauta  da  wahala , sai  tawa  yar  saurayin da  yake  sonta  mutun d'aya  ne kuma  ba  wani mai abun  kirki bane  gashi  kace  yarinyata  zata  samu   farinjin  samari  masu  kyau  da kudi sai gashi  sa'banin  haka  nake  gani  madadin  maryama  tayi  bakin jini  acikin  mutane  da samari  duk  banga haka ba ."

"kullum  farinjinta  sake  qaruwa yake  jamaa  suna  matukar  qaunarta  basa  son  kula ya'yana koina  akaje  sai  dai  ace a  gaishe da  maryama  amman  banda ya'yana , wani  abun  bakinciki afa  har  yaran  nawa  suma kullum maryama , suna  matukar  sonta  sunki  su  gane ita din  matsalarsu ce,  ko  wani  abu  nayi  mata  sai dai  kaji  suna  min  fad'a  suna nuna  min  rashin  daidai  nan  ta tsaya  ta  sauke  numfashi da ajiyar zuciya  ,afa  yace  "to  yanzu ki takaita  matsalarki  me  kike son ayi ?

Aunty  salma  ta  gyara  zama  tace "ina  son  a fara  rabata  da ya'yana ina  son  naji  sun  tsaneta  fiyye  da  yadda  nake  jin  tsanarta  acikin  raina  wannan  shine  kawai muradina  kafin  nazo  neman wani bukatar  ."afa  yayi  murmushi yace "ai  wannan  shi  yafi  komai  sauki ki  tafi  gida  kawai  zaki  ga aiki da cikawa  cikin  sati  biyu  masu zuwa , amman  ina  son  ki  dawo kafin  kwanakin su cika  akwai abinda  zan  baki  indai  har  na baki  ki  kai   amfani  dashi  magana  ta  qare  amman  yanzu zan  fara  jaraba  'yan  abinda bazaa  rasa ba ."

aunty  salma  tayi  godiya  ta  ajiye masa  kudi  ta  fice  tana  faman zuba  godiya  tana  cigaba da zagi da  maseefar  kiyayyarta  da maryama  har  ta  fice  daga  gidan afa  ta  dawo  gida  tana saka da warwara  dan ita ko kashe maryama afa  zai  yi  tana só saboda  tsanar  datai  mata  yarinya sai kace lu'u lu'u ai muddin tana  cikin  gidan  sai  ya'yanta  sun  rigata  samun  gidan  aure kafin  tayi  ,idan  kuma  har  zata yi auren  zata sa afa  yayi  mata aikin  da zata  auri  matsiyacin  daya fi ubanta  talauci ."
Chapter 42 · 0% Book details