← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 61 OF 100

Sashe 61

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

ahankali ta juya ta nufi kofar fita cikin bacin rai sannan sauran yanuwanta suka biyo bayanta "amman ai ya kamata ka amsawa gimbiyata ya sake yin mgn can qasa"gsky hisham baka da hankali km kana bani kunya yanzu kai da gaske sonta kake "?sosai ma kuwa ina sonta sai dai ita bata sona ..""what ?" Wallahi haka ta fad'a ai naso bikin a hadashi da naka amman ya zanyi tunda tace bata só na hakura amman nasan sonta ne zai kasheni "amman shine ka kyaleta baka ci ubanta ba?
aa babu wannan ai kai ma kasan yadda soyayya take ka duba yadda baka son mrym kake son yarinyar mafarkinka "ka daina kawo wannan misalin ni bana son wannan yarinyar ita ma kuma bata sona kaga akwai matsala wajen namu hadin ko ka fahimceni ."?

"Misali ina sonta to ya zama dole dan ubanta ta soni sannan misali da'ace tana sona nima bazan dinga jin tsanarta haka ba duk da nasan nawa rashin son ne babban matsala dan ita prentending ne kawai nasan babu macen da zata kalleni tace wai bata sona dama ne kawai bata samu ba ,ya fad'a yana jan tsaki ka kira min auta  "me zata maka  ?Kai dai kira min ita kawai   yau  yarinyar nan zataci ubanta da me  tafika da zata ce  bata sonka ?shiru hisham yayi yana kallonsa a she haka ata yake sonshi jiki a sanyaye ya dauki wayarsa ya kira nana hauwa'u cikin kankanin lokaci ta bayyana a falon "yaya gani "je kizo min da nuzla yanzu yanzu kafarta kafarki "okay yaya ta juya da sauri ."su kuma suka cigaba da tautaunawa ."

Bayan mintuna goma sai gasu sun shigo nana hauwa'u ta  kama  gabanta  ta bar nuzla tsaye cike da fargaba  ta dan saci kallon hisham dake zaune taga ya sakar mata murmushi  ta kalli mr ata taga ya hade rai sai kafarsa daya yake girgizawa har  kusan mintuna  shabiyar tana tsaye sannan tace "yaya gani wai ..."da sauri ya dakata daita ta hanyar daga mata "waye wannan ?ya nuna mata hisham dake zaune "yaya hisham ".

"Very good meye a tsakaninku ?nothing ta bashi amsa atakaice ba hisham ba hatta mr ata sai daya dago tsumammun idanunshi ya tsura mata yana kallonta "kika ce nothing kenan baki san yana sonki ba ?nasani but na fad'a masa gaskiya ni bana son shi dan ..."enough ! bana  bukatar  jin  maganarki ko wani abu  kije ki fara shirin aurensa nan da kwanaki  goma  ." cikin firgici da tashin hankali ta shiga d'aga kafafunta zuwa inda yake zaune  "me yasa  yaya ?" dan Allah kayi hakuri karka min haka  wallahi ni bana son shi a matukar tsawace yace "nace karki sake fad'ar wata  magana anan , karki   sake kula kowa  acikin masu sonki shima wanda kike so ki kashe  soyayyarsa  acikin zuciyarki ki so wanda yake sonki  .."

Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan  09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

           Page 20

jikinta  na  wani  irin  rawa  ta k'araso ta  durkushe a gabansa har  bata  san  sanda  ta d'aura hannuwanta  duka bisa cinyoyinsa  tana  kallon  cikin   kwayar  idanunsa da  suka  rikid'e  suka  canza   kala   a wulakance  ya   zame   jikinsa  yana  mai  kawar  da   fuskarsa   gefen  hisham  dake  zaune   tmkr   mutun  mutumi  yana   kallonsu   cike  da  matsanancin  tashin   hankali   ,shi   kuwa  mr  ata  alamun  baya  son  kallon  fuskarta  ne   yasa   shi    maida  idanunshi  kan  hisham  ".

"dan  allah   dan  Allah !!  yaya  adam  kayi   hakuri    ta  kai  hanuta  tana  qoqarin   juyo  da  fuskarsa  gareta  domin  su  fuskanci  juna , zuciyarta  na  wani  irin    bugawa  da  karfin  gaske  take  kallonsa haka  ma  hisham  zuciyarsa ce take ta bugawa fiyye da   kaida   ya  soma jin  wani sauyi na   daban  a gabadaya  ilahirin   jikinsa   wanda  ke  gauraye da tsantsar   tashin  hankali,  shi  kuwa  mr  ata  mamakinta   yasa   gbdy   ya qasa   magana   duk da maganar   yake  son  yi .

Kwayar   idanunta  suka   cicciko  da  ruwan   hawaye muryarta a sarke  tace "dan   Allah  yaya   kayi   hakuri   karka  bari  wannan  auren  ya  kasance  domin   zuciyata   bazata  iya d'aukar wannan  nauyin  ba,   wata razananniyar  tsawa  ya buga  mata  wanda  ya  kamata  ace ta  tsorata   ta dawo da  hankalinta   jikinta   amman   ina  sai  ma  sake  narkewa  tayi  a wajen  zuciyarta  babu  tsoron  komai  acikinta , muryarsa  a kausashe   yace " tashi   ki   bar  nan  ki   kuma  fara  shirinki   kamar  yadda   na  fad'a  miki   oya  leave ."

"dan  Allah  ka  saurareni  yaya  "ya  girgiza  mata  kai   yana   cewa "   I don't  want  to listing anything  from   you  just  leave  now "dan   allah  yaya  adam  kayi   hakuri  ka  saurareni    akwai  maganar  da  idan  na  fad'a  maka   nasan   zaka   fahimceni "ata dan  Allah  ka  barta  ta  fad'i  abinda  ke zuciyarta    Hisham  yayi  maganar   yana  qarewa  jikin nuzla  dake  rawa  tmkr   mazari  da   kallo  , yadda  take  cikin   tashin  hankali  haka  shima  ya  tsinci  kanshi  cikin   tashin  hankali  mai  tsanani  har  yana  jin  ma  kamar  ya  cire   mata  nata  damuwar  ya  qarawa   kanshi "

Hisham  yayi  tsuru   tsuru  yana  jira  yaji  abinda zata  fad'a  ,yayinda  mr  ata  bai  ce  uffan  ba  ya yunkura  ya  mike  tsaye  ya  kwashi  wayoyinsa  ya  fara   taka  kafafunsa  da   kyar   zai  bar  wajen kasancewar  bai  son  yawon   magiya  bare irin nata dake   hargitsa   kwakwaluwa  nuzla  tayi   saurin  shan   gabansa  tana   fad'in  "yaya  karka  wuce  ka  bar  zuciyata  cikin   maseefa  tayi  maganar  cike  da  tausayawa  ,bai  yi  mata  magana   ba  ya  cigaba  da tafiya  yana  mata  gargadi  da  hannunsa  alamun ta shiga  hankalinta , bata  daddara  ba ta sake  shan   gabansa  dan   gbdy  zuciyarta  ta  rigada  ta bushe  babu  abinda  take  qoqarin  aikatawa  face  ta  bayyana    masa  ciwon  dake  cikin  zuciyarta ."

Ya  tsaya   kawai   yana   mata   wani  mugun   kallo
yana  furzar  da  iska   mai   zafi   daga  bakinsa muryarta  cike  da  rauni  da  buqatar  atausaya  mata  ta  fara  magana  "bazan  iya  jure  ciwon  rabuwa  da  wanda  nake  só  na  auri  wanda  kake  só  ba ta  karasa  mgnr   tana   rungumeshi  ajikita   tana  kuka a matukar   zuciye  ya  fixgeta  daga   jikinsa   yana  sake  furzar da  iske  "are you out of  your sense ?ni sa'anki   ne  da  kike  shiga  gabana? "  ko  ina  wasa dake   ne  da  ina   magana  kina   magana ? ya fad'a yana   kawar  da  fuskarsa   akanta  domin  dai zuciyarsa  ta  fara  tausaya  mata  tausayawar  da  bata  da   wani  amfani  dan  bazai  ta'ba  iya  mata taimakon  da  take  nema  daga   garesa  ba ."

Hisham  ya  rasa   meke   faruwa   atsakaninsu  babu  abinda  zuciyarsa  bata  kissa  masa  ba  a zaune  da  yake  tmkr an  dasashi  irin  kallon da take  ata  da  rungumar da  tayi  masa  ya  fara  gasgata  zuciyarsa  akan  abinda  bai  niyyar  yarda  dashi  ba  yaso ya  mike  ya  qarasa  zuwa inda  suke  tsaye  yasan ko akan  me  take  masa  magiya   har  da  runguma amman  hakan  nan  yaji  gara  ya  cigaba  da  zama a  inda  yake  zai  fiyye  masa  alkhairi   kuma  bugu da qari    yayi  imani  ata  bazai  ta'ba  aikata  komai  ba face  abinda  yasan  zai  zamewa  rayuwarsa  farinciki   he really  trust  him  mutun  ne  shi  mai  kyakkyawar zuciya   akanshi ."

Hawaye  na  gangaro  mata  bisa  kuncinta  yayinda  magana  ya  fara  fitowa   daga  bakinta  "ina qaunar ka  yaya  ? bai  yi  mamakin    jin  fitowar  hakan  daga  bakinta  ba  domin  ya  rigada  ya  gama karantata  tsab  "na sani  sai  akayi  yaya  ?ya  fad'a yana   kallonta  yana  jin  kamar  ya  soma  yar yarfa mata  maruka  ta  dawo haiyacinta  "dan  Allah  yaya karka  ce  min  a'a !   a kowani  hali  zan kasance  tare  da  kai "  ta  maimaita  hkn  a fili   yafi  sau   goma tana  mai kai  hannu ta shafa  kasumbar  dake   kwance a  fuskarsa  ji  yayi  kamar  ta  shafa  masa garwashin  wuta ,shi  fa  duk  duniya  babu  macen da  yake  jin  zata  ta'ba  shi   yaji  wani  abu  ajikinsa sai princess  ita ma  din   yanzu  ya  soma  gogeta a zuciyarsa  da  rayuwarsa ."cikin  fita  haiyacinta
  ta riko  fuskarsa  sosai  ta  sanya  kwayar  idanunta  dake  tsiyaya  ruwan  hawaye  acikin nasa " ban  san  hka  soyayyarka  tayi  tasiri  acikin  zuciyata ba  sai  dana  qasa  amsar  soyayyar  kowa ."

"Ban  san  tasirin  soyayyarka  ta  kai  mizanin  da  zan  iya  rasa  rayuwata  ba  sai  da  naji   zaka  min  nisa  , yaya   kaine  duniyata ruhina  yana  tare  da  kai  ako   da  yaushe , nayi  yunkurin   bayyana  maka soyayyata a tun  lokacin  da  mubina Ke mutuwar  sonka   amman  na  gaza  aikata  hakan  ina  ganin  cewar   zan  iya   cire   soyayyarka  na cigaba  da  rayuwata  amman   still  na  qasa  domin  kuwa  every  each  second   nake  jin  sonka na  qaruwa a cikin  zuciyata ,  ina  ta  qoqarin  sheida  maka  halin  da  zuciyata  take  ciki  kwatsam  kuma  sai   ga  batun   aurenka  da  marsi  bance  ka bar  marsi  ba  amman dan  allah  ka  had'amu  ka auremu " rokonki bai  kar'bu   ba   bare   wata   alfarmar  ya kamata ku koyi  yadda  ake  iya  control  din  zuciya  "ka taimakeni  ban  san  ya  zanyi  ba  " kar    allah  yasa ki   sani   ya  fad'a  yana  jan   tsaki   ."

kuka   take  sosai   tana   kallonsa   tmkr  ranar   ta  fara  ganinsa  shi   kuwa  haushi  ne ya turnikesa  a  wajen  zuciyarsa   banda  tuttukin  bakinciki  babu  abinda  yake , a  ganinsa  ma  ta  balain  rainashi
shi  zata  kalla  tace   tana so  alhalin  ga hisham dake  mutuwar  sonta?  "kayi  hakuri  dan  girman Allah  nasan zakayi  tunanin  komai  akaina   wallahi  haka  ne , dan  na rigada na   haukace  akanka  bazan  iya jurar  abinda   nake  ji  akanka   ba  sannan  bazan iya amsar    soyayyar   yaya  hisham  ba  ,dan  kona auresa  gangar  jikina  ya  aura  zuciyata  da  komai nawa  yana  gareka   da  kawai  zan  iya  rayuwa ..."
Chapter 61 · 0% Book details