Sashe 54
Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
bata kulani ba har na dasa aya ta fuskanci bilkisu yayinda gabadaya yanuwanta kacokan suka maida hankalinsu Kan ussein duk sun qagu suga hukunci mahamud akan ussein kasancewarsa soja , hjy rahma ta matso sosai kusa da bilkisu tana cewa "ba dai ni zaki wulakanta akan namiji ba ? ."babu irin rarrashin da ban miki ba ,babu irin hakurin da ban baki ba ,me kike son dani ? "wallahi zanyi dake bilkisu , yau zaki ga tozarci ganin idanunki tunda kika nemi ki wulakantani akan wani banza can wanda ba kowan kowa bane shi ,ba kowa bane iyayensa a duk fadin garin nan hasalima rayuwarsa a banza take ."
"zaki wulakantani akan wani nmj banza da wofi wallahi zanyi dake muddin kika ce shi zaki aura sai na tsine miki na tsinewa auren ,wallahi auren bazai ta'ba yin albarka tana mgn tana zabga mata mari a fuskarta da bayan hannunta , yayinda azaba tasa bilkisu ta shiga karewa dan kar marin yayi mata illa amman matar nan sai zabga mata maruka take kuma a fuska na rantse miki da girman allah maryama tayi mata mari yafi guda tara ajere ana goma ne bilkisu ta rike mata hannu kuma nasan azaba ce tasa tayi haka ,aiko matar nan ta danneta da iyakacin karfinta ta dinga dukanta tana cewa ni zaki rikewa hannu in sha allahu kema sai ya'yanki sun miki abinda kika min ,sai sun hanaki kwanciyar hankali kamar yadda kika hanani kwanciyar hankali a karshe kafa mata hakori a damtsen hannunta."
"wani irin gigitaccen qara bilkisu ta saki mai ban tausayi tana kuka tana neman d'auki gashi babu wanda ya kwaceta daga hannun mahaifiyarta sai dukanta take tana hadawa da zagi ganin haka yasa ussein ya nufi hjy rahma cikin tsananin fushi kamar mayunwanci zaki idanunshi sun kad'a sunyi jajur yasa duka hannunsa zai d'agata daga Kan bilkisu ai ganin ya ta'ba mahaifiyarsu gbdy yan'uwanta suka yo Kanshi shi da bilkisu cike da jin haushi suka dinga dukan su kamar zasu kashesu suna furta mahaifiyarmu zaka duka ? azahiri gaskiya ba wai dukanta yayi ba kawai ceton bilkisu zai yi daga dukanta, ina kuka ina basu hakuri ina qoqarin kwatarsa daga hannunsu amman ina sarkin yawo yafi sarkin karfi dan sai suka daina dukan bilkisu suka cigaba da dukansa shi kad'ai har sanda hjy ta shigo zubewa tayi kasa tana kuka tana cewa "zaku kashemun d'a ne to wallahi idan kuka kasheshi hukuma ce zata rabamu daku dan wallahil azim bazan ta'ba yarda ba ".
"kar Allah yasa ki yarda daman kece uwar matsiyaci ? "nice uwarsa kuma gatansa kuma ni d'ana ba matsiyaci bane dan me zaku masa haka ?
"ai yarku zaku jawa kunne ta daina zuwa inda yake shi meye laifinsa ? "laifinsa kulata da yake yi idan baya kulata bazata zo inda yake ba ,idan yace baya sonta karta sake zuwa inda yake ni nasan bilkisu bazata zo inda yake ba ki fad'a masa da babban murya ya rabu da kanwarmu ya zauna lafiya idan ba haka ba zamu 'batar dashi agarin nan ,kina ji kina gani zaki rasa d'anki har abada "hjy na fad'a 'yanuwan bilkisu na maida mata martani kuma basu daina dukansa ba ."
"neman layin 'yanuwasa mata na sake yi saadatu na d'auka na saka mata kuka ina cewa "bazaku zo ba sai an kashe maku da'nuwa ?dan girman allah kuzo ku hanzarta karku bari su illatashi "bilkisu cikin kuka ta rarrafa ta rike kafafun mahamud domin duk yafi dukan ussein cikin kuka tace "yaya dan girman allah kayi hakuri ka barshi karku kashe min rayuwata sannna karku rabani da dashi wallahi bashi da laifi nice mai laifi" .
"ya salam! ya furta a matukar fusace "wai bilkisu me ke damunki ne "?ta girgiza masa kai idanunta na zubar da ruwan hawaye kuyi hakuri nayi maku alkwarin bazan sake zuwa inda yake ba "muryar hjy rahma ta sake karade d'akin Aisha riko hannun makaryaciya karta gudu shi kuma sheidani ku fito min dashi yau zan nuna masa koni wacece agarin nan zanga uban da ya isa ya kwaceka Aisha ta riko hannun bilkisu gam bisa umarnin mahaifiyarsu sai dai bilkisu ta dinga turjewa nan ma wani marin aisha ta kai mata tuni daman fuskarta ta canza jini ya kwanta a duka idanunta ."
Mahamud kuwa qarasawa yayi inda ussein yake yace ya kama kunnensa ussein ya kama kunensa cikin kaduwa dan gbdy bai fahimci abinda yake nufi ba mahamud yace "you're very stupid I mean kayi frog jump Aishat ashe ma illiterate ne wallahi ko da wasa naji ka qara shiga harkar bilkisu zan mugun baka mamaki "mugun ma illiterate katon jahili liability kawai a haka zamu bashi aurenta sai kace kwakwaluwarmu ta juye ai har abada ,ka wuce dashi kaci ubansa ta yadda ko mai kama daita ya gani da mugun mugu zai arce ."
bilkisu na kuka ussein na frog jump nima ina biye dasu ina basu hakuri haka hjy hakuri take basu hankalinta a tashe muna fitowa kofar gida sai ga saadatu da fatima a rude basu tsaya neman baasi ba dan na rigada na fad'a masu komai sausauci suke neman masa amman mutanen nan suka ki banda cin mutunci babu abinda suke zubawa unguwa kuwa ya cika makil da jama'a yan kallo kowa na fadin albakacin bakinsu wasu suna ganin daidai ne matakin da suka dauka dayawa kuma laifin bilkisu suke gani ."
wani abu mai daci yan'uwansa suka hadiye tare da matsowa inda mahamud yake yana laftawa ussein belt a gadon bayansa "yanzu ina zaku dashi ?In ji cewar fatima tayi maganar cikin tsananin fushi "zamu tafi dashi inda zamu sake koya masa hankali," ya fad'a cike da gadara da isa "amman yana da kyau mu san inda zaku da d'anuwanmu kafin ku wuce dashi? Eh ! yana da kyau sai dai bani da wannan lokacin 'batawa idan aka koya masa hankali zaa iya sanar daku kuzo ku d'auki abinda ya saura ajikinsa "
Hjy kuka saadatu kuka haka ma fatima muna cikin wannan halin sai ga gali yace shine yayansa suyi hakuri su bar komai a hannunsa zai sa ya rabu daita rabuwa ta har abada ,mahamud yace "da dai ya fiyye masa kwanciyar hankali dan wallahi na sake dawowa akan case din nan sai dai ku dauki gawarsa" gali yace "to mun gode komai yazo karshe bilkisu ta bude idanunta da suka mata nauyi wani marayan kuka ta fashe dashi tana shesheka tana kallon kowa wanda ni nasan kukan da take alokacin bai wuce na rabuwa da ussein ba ."
fatima ta watsa mata harara hade da kallon banza tana cewa "kukan uwar me zakiyi wa mutane duk bake kika jawo masa matsala ba yana zaman zamansa muguwa azzaluma kin janyo yanuwanki sun wulakanta mana d'anuwan an tozarshi, tunda muke anan unguwar aka haifemu muka girma mukayi aure baa ta'ba wulakantamu ba sai yau kuma duk akanki ,kinsa ana dukansa kamar an samu ganga na rantse da girman allah matukar ussein..."
saurin toshe mata baki nayi ina cewa fatima karki rantse ,cikin fushi ta cire min hannu "ki barni aunty nayi magana kalli yadda fuskarsa tayi duk jini saboda Allah yau ayita ta qare ta kama kanta ta daina zuwa inda yake ,yanzu da suka zo suna hargagin banza da wofi da wulakanci shi meye laifinsa? yarinyarsu ya dace suyi wa magana ta daina zuwa inda yake dan muddin ta sake zuwa inda yake kafin ku dauki mataki mu zamu dauka dan ba daga sama ya fado ba azzaluman banza kawai kuma allah ya isa tsakaninmu daku tana fad'a aisha na fad'a."dan girman allah fatima karki sake cewa komai zo muyi magana na janyo hannunta " babu inda zani aunty ayita ta qare gwama su san muma bama son wannan diyar tasu kuma komai zai faru ..."
na sake toshe mata baki "dan Allah ki bar mgnr nan sulhu ake nema ."
Cikin ko in kula hjy rahma tace da wa zakuyi sulhu ?"kema Kinsan ruwa ba sa,an kwado bane baku kai wannan matsayin ba yanzu ma wannan maganar da nake duk sai na fashesa akan wannan matsiyacin "nayi tsuru tsuru ina dubanta "tsayuwar me kukeyi ku taho min dashi da sauri gali ya qaraso inda take hjy ai mun gama magana da yaronki, dan allah hjy kiyi hakuri ,in sha allahu tunda muka shiga cikin zance komai yazo karshe zanyi magana dashi "babu irin hakurin da baa bawa hajiya rahma ba amman tace sam sai an tafi dashi haka muna ji muna gani aka watsa useein abayan boot din mota aka wuce da
ussein ."
Kuka sosai maryama take kamar alokacin komai ya faru Kwantar da kanta umma tayi akan cinyarta tana rarrashinta "tabbas Aunty masoyiya ce ta gaskiya ,ta so mahaifinmu a halin babu ,ta zauna dashi har karshen rayuwarsa wallahi ba kowani d'an mai kudi bane mutumin kirki kamarta ,ta tsaya ta dubi mahaifinmu da kalmar so ta gaskiya
sai dai akwai illa umma Aunty ta jefa rayuwarta cikin matsala wanda a yanzu take shan wahala ".
" tabbas shine gskiyar dana dade ina nuna mata "baa jayayya da iyaye data yi hakuri tabi umarnin iyayenta tabbas zasu sauko dan kansu kasancewar akwai rabo a tsakaninta da mahaifinku ,cikin muryar kuka tace "mune silar jefa rayuwar mahaifiyarmu cikin wahala ko ? ta fad'a tana sheshekar kuka "karki ce haka maryama haka tata qaddarar take ,ita qaddara gata ko arziki ko nasaba bai isa ya canza maka ba ."umma ta numfasa sannan ta cigaba da magana ".
Bangaren su bilkisu kuwa tunda suka dauki hanya yan'uwanta suke magana suna zagin ussein cikin kuka bilkisu Ke rikon su "ku sani ussein bai muku laifin komai ba dan allah karku hukuntashi akan abinda bai yi ba" mari mahaifiyarta ta kifa mata haka ma aisha dan ubanki ki kama mana baki har suka kai gida zaginta suke direba na ajiyesu ya wuce da mahamud da ussein ."
"zaki wulakantani akan wani nmj banza da wofi wallahi zanyi dake muddin kika ce shi zaki aura sai na tsine miki na tsinewa auren ,wallahi auren bazai ta'ba yin albarka tana mgn tana zabga mata mari a fuskarta da bayan hannunta , yayinda azaba tasa bilkisu ta shiga karewa dan kar marin yayi mata illa amman matar nan sai zabga mata maruka take kuma a fuska na rantse miki da girman allah maryama tayi mata mari yafi guda tara ajere ana goma ne bilkisu ta rike mata hannu kuma nasan azaba ce tasa tayi haka ,aiko matar nan ta danneta da iyakacin karfinta ta dinga dukanta tana cewa ni zaki rikewa hannu in sha allahu kema sai ya'yanki sun miki abinda kika min ,sai sun hanaki kwanciyar hankali kamar yadda kika hanani kwanciyar hankali a karshe kafa mata hakori a damtsen hannunta."
"wani irin gigitaccen qara bilkisu ta saki mai ban tausayi tana kuka tana neman d'auki gashi babu wanda ya kwaceta daga hannun mahaifiyarta sai dukanta take tana hadawa da zagi ganin haka yasa ussein ya nufi hjy rahma cikin tsananin fushi kamar mayunwanci zaki idanunshi sun kad'a sunyi jajur yasa duka hannunsa zai d'agata daga Kan bilkisu ai ganin ya ta'ba mahaifiyarsu gbdy yan'uwanta suka yo Kanshi shi da bilkisu cike da jin haushi suka dinga dukan su kamar zasu kashesu suna furta mahaifiyarmu zaka duka ? azahiri gaskiya ba wai dukanta yayi ba kawai ceton bilkisu zai yi daga dukanta, ina kuka ina basu hakuri ina qoqarin kwatarsa daga hannunsu amman ina sarkin yawo yafi sarkin karfi dan sai suka daina dukan bilkisu suka cigaba da dukansa shi kad'ai har sanda hjy ta shigo zubewa tayi kasa tana kuka tana cewa "zaku kashemun d'a ne to wallahi idan kuka kasheshi hukuma ce zata rabamu daku dan wallahil azim bazan ta'ba yarda ba ".
"kar Allah yasa ki yarda daman kece uwar matsiyaci ? "nice uwarsa kuma gatansa kuma ni d'ana ba matsiyaci bane dan me zaku masa haka ?
"ai yarku zaku jawa kunne ta daina zuwa inda yake shi meye laifinsa ? "laifinsa kulata da yake yi idan baya kulata bazata zo inda yake ba ,idan yace baya sonta karta sake zuwa inda yake ni nasan bilkisu bazata zo inda yake ba ki fad'a masa da babban murya ya rabu da kanwarmu ya zauna lafiya idan ba haka ba zamu 'batar dashi agarin nan ,kina ji kina gani zaki rasa d'anki har abada "hjy na fad'a 'yanuwan bilkisu na maida mata martani kuma basu daina dukansa ba ."
"neman layin 'yanuwasa mata na sake yi saadatu na d'auka na saka mata kuka ina cewa "bazaku zo ba sai an kashe maku da'nuwa ?dan girman allah kuzo ku hanzarta karku bari su illatashi "bilkisu cikin kuka ta rarrafa ta rike kafafun mahamud domin duk yafi dukan ussein cikin kuka tace "yaya dan girman allah kayi hakuri ka barshi karku kashe min rayuwata sannna karku rabani da dashi wallahi bashi da laifi nice mai laifi" .
"ya salam! ya furta a matukar fusace "wai bilkisu me ke damunki ne "?ta girgiza masa kai idanunta na zubar da ruwan hawaye kuyi hakuri nayi maku alkwarin bazan sake zuwa inda yake ba "muryar hjy rahma ta sake karade d'akin Aisha riko hannun makaryaciya karta gudu shi kuma sheidani ku fito min dashi yau zan nuna masa koni wacece agarin nan zanga uban da ya isa ya kwaceka Aisha ta riko hannun bilkisu gam bisa umarnin mahaifiyarsu sai dai bilkisu ta dinga turjewa nan ma wani marin aisha ta kai mata tuni daman fuskarta ta canza jini ya kwanta a duka idanunta ."
Mahamud kuwa qarasawa yayi inda ussein yake yace ya kama kunnensa ussein ya kama kunensa cikin kaduwa dan gbdy bai fahimci abinda yake nufi ba mahamud yace "you're very stupid I mean kayi frog jump Aishat ashe ma illiterate ne wallahi ko da wasa naji ka qara shiga harkar bilkisu zan mugun baka mamaki "mugun ma illiterate katon jahili liability kawai a haka zamu bashi aurenta sai kace kwakwaluwarmu ta juye ai har abada ,ka wuce dashi kaci ubansa ta yadda ko mai kama daita ya gani da mugun mugu zai arce ."
bilkisu na kuka ussein na frog jump nima ina biye dasu ina basu hakuri haka hjy hakuri take basu hankalinta a tashe muna fitowa kofar gida sai ga saadatu da fatima a rude basu tsaya neman baasi ba dan na rigada na fad'a masu komai sausauci suke neman masa amman mutanen nan suka ki banda cin mutunci babu abinda suke zubawa unguwa kuwa ya cika makil da jama'a yan kallo kowa na fadin albakacin bakinsu wasu suna ganin daidai ne matakin da suka dauka dayawa kuma laifin bilkisu suke gani ."
wani abu mai daci yan'uwansa suka hadiye tare da matsowa inda mahamud yake yana laftawa ussein belt a gadon bayansa "yanzu ina zaku dashi ?In ji cewar fatima tayi maganar cikin tsananin fushi "zamu tafi dashi inda zamu sake koya masa hankali," ya fad'a cike da gadara da isa "amman yana da kyau mu san inda zaku da d'anuwanmu kafin ku wuce dashi? Eh ! yana da kyau sai dai bani da wannan lokacin 'batawa idan aka koya masa hankali zaa iya sanar daku kuzo ku d'auki abinda ya saura ajikinsa "
Hjy kuka saadatu kuka haka ma fatima muna cikin wannan halin sai ga gali yace shine yayansa suyi hakuri su bar komai a hannunsa zai sa ya rabu daita rabuwa ta har abada ,mahamud yace "da dai ya fiyye masa kwanciyar hankali dan wallahi na sake dawowa akan case din nan sai dai ku dauki gawarsa" gali yace "to mun gode komai yazo karshe bilkisu ta bude idanunta da suka mata nauyi wani marayan kuka ta fashe dashi tana shesheka tana kallon kowa wanda ni nasan kukan da take alokacin bai wuce na rabuwa da ussein ba ."
fatima ta watsa mata harara hade da kallon banza tana cewa "kukan uwar me zakiyi wa mutane duk bake kika jawo masa matsala ba yana zaman zamansa muguwa azzaluma kin janyo yanuwanki sun wulakanta mana d'anuwan an tozarshi, tunda muke anan unguwar aka haifemu muka girma mukayi aure baa ta'ba wulakantamu ba sai yau kuma duk akanki ,kinsa ana dukansa kamar an samu ganga na rantse da girman allah matukar ussein..."
saurin toshe mata baki nayi ina cewa fatima karki rantse ,cikin fushi ta cire min hannu "ki barni aunty nayi magana kalli yadda fuskarsa tayi duk jini saboda Allah yau ayita ta qare ta kama kanta ta daina zuwa inda yake ,yanzu da suka zo suna hargagin banza da wofi da wulakanci shi meye laifinsa? yarinyarsu ya dace suyi wa magana ta daina zuwa inda yake dan muddin ta sake zuwa inda yake kafin ku dauki mataki mu zamu dauka dan ba daga sama ya fado ba azzaluman banza kawai kuma allah ya isa tsakaninmu daku tana fad'a aisha na fad'a."dan girman allah fatima karki sake cewa komai zo muyi magana na janyo hannunta " babu inda zani aunty ayita ta qare gwama su san muma bama son wannan diyar tasu kuma komai zai faru ..."
na sake toshe mata baki "dan Allah ki bar mgnr nan sulhu ake nema ."
Cikin ko in kula hjy rahma tace da wa zakuyi sulhu ?"kema Kinsan ruwa ba sa,an kwado bane baku kai wannan matsayin ba yanzu ma wannan maganar da nake duk sai na fashesa akan wannan matsiyacin "nayi tsuru tsuru ina dubanta "tsayuwar me kukeyi ku taho min dashi da sauri gali ya qaraso inda take hjy ai mun gama magana da yaronki, dan allah hjy kiyi hakuri ,in sha allahu tunda muka shiga cikin zance komai yazo karshe zanyi magana dashi "babu irin hakurin da baa bawa hajiya rahma ba amman tace sam sai an tafi dashi haka muna ji muna gani aka watsa useein abayan boot din mota aka wuce da
ussein ."
Kuka sosai maryama take kamar alokacin komai ya faru Kwantar da kanta umma tayi akan cinyarta tana rarrashinta "tabbas Aunty masoyiya ce ta gaskiya ,ta so mahaifinmu a halin babu ,ta zauna dashi har karshen rayuwarsa wallahi ba kowani d'an mai kudi bane mutumin kirki kamarta ,ta tsaya ta dubi mahaifinmu da kalmar so ta gaskiya
sai dai akwai illa umma Aunty ta jefa rayuwarta cikin matsala wanda a yanzu take shan wahala ".
" tabbas shine gskiyar dana dade ina nuna mata "baa jayayya da iyaye data yi hakuri tabi umarnin iyayenta tabbas zasu sauko dan kansu kasancewar akwai rabo a tsakaninta da mahaifinku ,cikin muryar kuka tace "mune silar jefa rayuwar mahaifiyarmu cikin wahala ko ? ta fad'a tana sheshekar kuka "karki ce haka maryama haka tata qaddarar take ,ita qaddara gata ko arziki ko nasaba bai isa ya canza maka ba ."umma ta numfasa sannan ta cigaba da magana ".
Bangaren su bilkisu kuwa tunda suka dauki hanya yan'uwanta suke magana suna zagin ussein cikin kuka bilkisu Ke rikon su "ku sani ussein bai muku laifin komai ba dan allah karku hukuntashi akan abinda bai yi ba" mari mahaifiyarta ta kifa mata haka ma aisha dan ubanki ki kama mana baki har suka kai gida zaginta suke direba na ajiyesu ya wuce da mahamud da ussein ."