← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 36 OF 100

Sashe 36

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Washegari  da   misalin  karfe  goma na   safiya  a kofar  shiga  bangaren  hjy  zulaiheart  tayi masu  kai tsaye a babban  falon  gidan suka  iske  mami zaune  yayinda  d'aya  daga  cikin  masu aikinta ke zaune   tana  mammatsa  mata  yatsun  kafafunta sallamarsu baba  qarami tasa mami  dauke idanunta  daga  Kan tv ta maida kansu  tana  sakin fuska  sai  dai kallo d'aya tayi  masa  ta  fahimci  akwai damuwa  atattare  dashi  ,aranta tayi addua  allah yasa ba wata matsalar  bace  ta taso , ta amsa sallamarsu  tana cewa "sannuku  da zuwa !" baba  qarami  ya samu waje ya  zauna akan kujerar  dake  fuskantarta yayinda  hindatu  ta zauna a kasa kan kafet  a gaban mami ta  sunkuyar da kanta  kasa  tmkr mai neman  gafara  tare da gaishe da mami cike da ladabi  ta amsa  tana  mami  ta maida hankalinta ga baba qarami   tana   nazarin fuskarsa sannan ta kalli yarinyar  dake zaune a gabanta tace "salaha tashi kije   Ki  bamu  guri  cikin  sauri  yarinyar  ta mike tare da fadin  "tô !"

       Mami  ta sake maida hankalinta sosai  garesu sannan ta fara magana a natse "baba qarami fatan dai lafiya  dan naga yanayinka  ba kamar yadda na saba ganinka ba  yace "lafiyar dai da sauki "ta gyara zamanta cikin tsananin damuwa "daman dai na lura da hakan dan ba haka yanayinka yake ba kai din mutun ne mai faram faram duk sanda za'a ga fuskarka cikin murmushi take tô ina jinka fad'a abinda ke  tafe da kai ."

Naunayen ajiyar  zuciya ya sauke yana sake gyara zama  yace "zulai  jiya baba babba yazo min da wata magana akan hukuncinki akan Adam"  ta gyada kai tana  sauke  numfashi "haka ne nasan zaka fi kowa jin dadi "tabbas  naji  dadi  sai  dai   wani  hanzari ba gudu  ba nima na dade ina son had'asu  aure da hindatu   "mami tayi shiru tana dubansa da hindu dake   zaune  tana  nazarinta tana son gano wani abu atattare  da hindu domin dai ita din macece mai tsananin  baseera tare da saurin karantar mutun sai data  numfasa sannan tace "ita hindatu tana son shi ne ?

"tabbas  tana tsananin sonshi na tsawon shekaru tunda tashi da soyayyarsa ta tashi ni ne mutun na farko data fara sheidawa da fari na nuna mata illar rayuwar data jefa kanta na afkawa soyayya da qarancin shekarunta  alokacin na tmbyeta meye dalilinta  na son shi  ? me  ya  dauki hankalinta akanshi  ? tace ba dan yana dukiya  da kyau ba ,yau da  zai  wayi  gari  bashi da  komai  bashi da hannu bashi da kafa  koda akan titi zasu rayu zatai  rayuwa dashi kawai son shi ta keyi dan  Allah alokacin shekarunta shashida né  kawai  wanda ni nake ganin bata san  ma me take ba bama tasan meye soyayyar ba yasa take fadin haka ahankali baba qarami ya fayyacewa  mami komai akan soyayyar da hindu ke ma ATA  babu abinda ya rage numfashi mami tayi ta saukewa tana girgiza kai cikin tausayawa tana kallon hindu data sake dukar da kanta kasa sosai ."

"Masha allah naji dadin wannan abu sosai soyayya mai hade da zumunci allah ya bamu ikon sada zumunci dan allah ba dan kwadayin ko neman wata biyan bukata ba ". ta sake numfasawa ta cigaba da magana  "nima daman tun farko burina kenan adamcy  yayi aure biyu"  ahankali baba qarami ya kalli inda hindu take wacce mgnr mami yasa ta dan dago kanta mami ta cigaba da magana "zan yi iya  kokarina hindu na kawo karshen damuwarki duk da adamcy baya da raayin ajiye mata biyu amman zanyi convincing   dinsa  domin  kawo farinciki arayuwarki da  yarda  allah ."

    da  sauri  hindu ta kalli mahaifinta shima din ita yake  kallo domin dai yasan diyarsa da tsananin kishi zata fi bukatar ganin ita kadai ta mallakesa Kmr yadda ta sheida masa kallon da takewa mahaifinta só take yace a fasa auren da mrym gbdy ya aureta  shi kuwa baba qarami a hakan ma maganar tayi  masa dadi "fatana  mu hadu muyi addua akan lamari sannan mu nemi zabin allah allah kuma yasa  gogan naka ya yarda ya amince ya  hadasu su biyu din , ku bani lokaci kadan zan yi magana dashi duk abinda mukayi dashi zan nemeka da  wannan maganar suka kawo karshen zance sukayi  mata sallama ."

   Suna shiga  dakin baba qarami   hindu ta fara zubar da hawaye acikin slow voice tace " baba ina ji ajikina ya adam bazai aureni ba dan dai idan amincewarsa zaa tsaya nema wallahi bazai ta'ba amincewa ba bugu da qari ni banason sharing dinsa da kowa nafi son ni kadai dan sam ban dace da zama da  wata aba kishiya ba zan só mu rayu dagani sai shi  ta karashe mgnr tana shesheka murmushi baba qarami yayi tare da fadin "hindu kalleni nan " ta tsura masa  idanunta Kmr yadda ya bukata "ki kwantar da hankali babu wani abu acikin ya haduku biyu din amincewarsa shine abinda muka fi bukata a yanzu dan zaki iya kawar daita byn auren ki zauna ke kadai keda kike da baiwa iri iri nasan zaki bawa babanki mamaki haka dai baba qarami ya tasa hindu a gaba yana kwantar mata da hankali babu laifi hindu ta saki jikinta  tare da  karfafa zuciyarta sai dai ta rantse muddin bata samesa babu wata mace da zata mallakesa tana raye ."

****
Sanye  ATA  yake  cikin  farin yadin vol  mai shegen haske da tsada  a hankali yake  taku yana gyara  zaman  hullarsa  baki  haka zali takalmin dake sanye da kafafunsa black cover shoes ne tsintsiyar hannunsa daure  da  agogon rolex   yana dumfaro falon kamshi turarensa ya mamaye koina Kmr  shagon turare yana gama qarasowa yace wa hisham "muje ko ".kai me yasa bakasan ka bawa mutun rai ka bashi hakuri ba duk lokacin dana bata ina zaman jiranka da muje ko  zai qare  " ina laifin kace hisham Afuwa kayi hakuri muje abokina km danuwana."
Dogon tsaki yaja kawai batare dayace uffan ba .

"matsalata da kai kenan ka gama bata lokaci amman zaka wani jawa mutane tsaki still bai ce komai ba 
ya nufi hanyar dakin mami tana zaune ya shigo ta  dago a natse tana duban kofar ganin shine cikin shigar da tafi qauna ta saki fuska cikin tsananin farinciki  tace "Masha allah adamcy nah kayi kyau sosai allah yayi maka albarka  ,sai dai wannan uban wanka  da kashi haka kmr yau  daurin aurenka,  ai ko yau né daurin aurenka sai  iyakarka hk kai  ni kamar ma har da hoda ka shafa ko? Tsuke bakinsa yayi  dan tsokanar sweetheart dinsa na yau yazo da wani salo ana zaman lfy me zai yi da wani hoda shi ba mace ba  ."

"sweetheart ni zan fita amman zan dan jima ban dawo ba dan yau zaa bude kamfanin tace mai petir da sinadarin gas "Alhamdulillah masha ,allah allah yasa albarka  arayuwarka data kasuwancinka allah ya  tsare  min  kai  ,yadda zaka fita lafiya allah ya dawo da kai lafiya  sharrin mutun da aljani Allah rabaka  dashi  yace "Ameen !atakaice  ya juya a natse yana taku  tmkr wani jinin saurata "sai na dawo sweetheart  ." a dawo lafiya adamcy nah ta fad'a tana cigaba da kallon bayansa "yau  tsawon  kwana uku kenan tana   son sheida masa bukatar baba qarami amman ta kasa, ita  kanta tana jin tsoron tunkararsa , tayi  dukkanin tunaninta ta rasa ta ina zata fara  shigo  masa da maganar , auren mrym ma  da yaya ya amince yanzu  kuma ta sake kawo masa mgnr wata tasan tattara wa  kawai zai yi ya gudu ya barta dasu  ."

har ya kai bakin kofa yana shirin d'aura hannunsa akan handling din kofar ya  tsaya cak  ya waigo
bayansa adaidai lokacin  da mami ta sauke numfashi  da  girasa ya tambayeta  ,ta girgiza masa kai kawai tamkr   wata   marainiya "ko akwai damuwa ne ?ta sake numfasa wa kana tace " babu  komai  adamcy nah  ina dai kallonka ne kayi min kyau sosai shigar ta amshi jikinka "me  yasa  bazanyi amfani da wannan damar  na fad'a masa  bukatar kanin mahaifinsa ba ? tayi mgnr acikin ranta  da sauri zuciyarta ta gargadeta "karki soma yace ya fasa auren  gbdy gashi goben  nan zaa je neman masa auren mrym  numfashi ya fesar "saboda Ke nayi shigar dan nasan zaki ji dadi gaahi yau  juma'at  "ai kuwa naji dadi kwarai da gaske na kuma  gode sosai allah ya baka zuria masu  albarka yadda kake ji dani kake min biyayya Allah baka masu yi maka bai amsa ba ya sa kai ya fice daga dakin  zama ta cigaba da yi tana tunanin  mafuta zata jajurce da tsayuwar dare domin neman zabin allah  dan shine kawai mafuta agareta."

Aunty  abinda  na gama  jin bayanin  ibrahim  taji kafafunta suna  barazanar kasa daukarta lokaci  daya  zuciyarta na barazanar  tarwatsewa Ibraheem ya matso yana girgiza Aunty abinda wacce ta dawo tmkr mutun mutumi "abida abida!! lafiyarki what's wrong abida?abida tayi shiru kawai tana sauke numfashi batare data amsa ba " baba babba zasuje nemawa ATA auren maryam  gobe goben nan idan dai ba karya kunnuwanta suka jiye  mata ba haka taji ya fito daga bakinsa  " ibrahim me naji kace ? tana bukatar ya sake maimaitawa babu bata lokaci ya sake maimaita mata " wai tukunna wace maryam zai aura ?"maryam dai wacce Ke zaune a gidan mami diyar  kaninta  ita zai aura  "da gaske ka tabbatar mrym zai aura ? ya gyda mata kai kawai  yana maida hankalin Kan wayarsa dake qara "

"ina sam sam wannan aure bazai taba yuwa ba ta runtse idanunta da karfi  ATA jarumin nmj né uwa uba kyau da natsuwa da Kamala ga tarin dukiya dasanin yakamata ai babu macen data dace dashi sai sultana gani yana mata wani irin kallo tayi saurin dawowa haiyacinta  sunanta ya sake kira tare da jawo hannunta ya zaunar daita akan kujerar daya tashi cike da rauni tare da yin kasa da murya yace "abida meke damunki ?babu abinda ke damuna nidai dan Allah kar aje neman auren nan wai ma waye ya hada wannan auren ?shi ATA din da kasan  ne ya zabi auren mrym din ?"ta karasa maganar cikin tsananin tashin hankali da bacin rai akan fuskarta ."
Chapter 36 · 0% Book details