← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 100

Sashe 26

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

ATA  bai motsa daga Inda yake ba har MB ya shigo ya zauna cike da tausayin abokinsa dan kallo d'aya zaka masa kasan baya tare da walwala da farinciki  har wata siririyar rama yayi "ATA..!" ya kira sunansa  anatse ATA  bai amsa ba illa zuba masa kwayar idanunshi   da yayi yana sauraronsa "yana  ga duk ka rame ? shiru yayi bai ce uhm ba bare uhm uhm sai dai ga dukkanin alamun hankalinsa na kanshi "dan Allah ka kwantar da hankalinka komai na duniya mai wucewa ne idan kabi komai a sannu da sannu komai zai zama normal ."

wani huci numfashi ya saki yana sake tsaida idanunshi da gbdy  suke cikin damuwa akan mb
sai da yayiwa MB kallon wasu mintuna sannan ya furzar da abinda ya tsaya masa a makoshi mai mugun daci cikin son danne duk wata damuwarsa yace "na rasa yadda zan cire wannan damuwar MB "kallonsa MB yayi yayinda ATA ya Maida idanunshi ya lumshe "Ina zanganta ?ya furta a saman labbansa cikin tsananin damuwa  "wa kenan ..?Idanunsa dake lumshe ya d'an bud'esu  da   kamar  bazai yi magana ba sai Kuma ya furta ", princess.."

  murmushi MB yayi "ka iya fad'ar sunan nan tamkar kai ka fara tsarashi a duniya "zaka ganta inshallahu Ina maka adduar ta zamo mutun ce ba aljana ba , sai abu na gaba  ka fara da abinda mami   take so "bana jin zan iya MB zan dai ta bin sweetheart  a hankali  har  sanda zan samo yarinyar ko  kuma na samo wata dabam  amman wannan guntuwar yarinyar  bazata zamo mata a gareni ba  sun dade suna tautaunawa kafin daga baya sukayi sallama duk Kuma maganar da suke akunne mami   sukayita ,
dan  haka ta shaka sosai  tun a lokacin ta fara  shirya abinda zata masa ."

Tunda  masu aikin gidan suka  san  ATA  ya sauka kowan nensu ya shiga hankalinsa hatta shigowarsu part din hjy zulaiheart ya taikaita sannan komai cikin sauri suke yi kasancewar sun san  shi dan Oya  oya ne duk da ba  abincinsu yake ci ba sai na mahaifiyarsa  kuma  bata zauna ba har washegari  tana kan  yi masa hidimar abincin da zai ci tare da abokansa Amar, shawul, shamsu MB  sun baje  a falonsa sai kwasar abinci suke Amar yace "friend duk fa matar da ka aura muddin bata iya girki irin na mami  ba zaku samu matsala daita  ",Sosai kuwa dan ni dai Ina ganin zan kawo fedy gurin mami  a sake  bata class na mussaman dan wanan girki yayi inji cewar  MB " suka sa dariya banda ATA  dake rike da waya yana duba mahimmam bayanai masu shigowa  .

Sai  daya  rage  mahimmam abubuwansa  sannan 
ahankali ya motsa  lip's dinsa "gaskiya ne Ina son macen da ta iya girki kuma qala dabam dabam  shiyasa kuka ga Ina dojewa auren yarinyar  nan dan nasan  babu abinda ta iya sai salo da  rike waya da shiga social  media ,ni Kuma ta Inda za'a samu matsala dani  kenan  dan  bazan yarda da rashin kamun Kai ba.

   gbdy suka  gyda  Kai  batare  da  sunce komai  ba  sai can  shawul yace  "ai idan princess dinka  ka aura ko bata iya  girki ba zaka  zauna daita haka  har karshen rayuwarka ATA ya sauke numfashi kawai   batare da yace uffan ba "kayi  shiru ko ba haka bane ? Inji cewar MB "ka'ajiye wannan magana bama zata  zo a haka ba  am very sure ta iya komai  ." Shawul yayi sigili yace " mai kmr mrym me zaiyi da wannan princess din taka ya watsa masa wani mugun kallo  "ra'ayina kenan princess  bana son mace  irin wannan yarinyar da ake kokarin lika min  yayi mgnr yana furzar da iska mai  zafi  daga bakinsa.

"Wai  Kai wayace  maka ana auren mace mara kiba a yanzu Kai gaka ba jiki ba , Kai    Kashi  ita kashi kuzo Kuna haihuwar kasusuwa Kai da zaka samu mai nama irin Marym chubi daita komai zamzam inji cewar Amar  gbdynsu babu Wanda bai dara ba MB kam har da fadowa yayi kasa  daga kan kujera dan dariya "ko jini  zamu dinga   haifa   ba kasusuwa ba. nafi  sonta  akan wannan  mai  siffar aljanu guntuwa  gata nan  dai  fari ne kawai ya taimaki rayuwarta.

  nana  hauwa'u  da  mryam  dake tsaye a bakin kofar falon hannu nana hauwa'u rike da tiren silver mai d'auke da gasashen kifi anyi raping dinsa  ita kuma mryam na rike da tire na harish   suka  Kalli  juna dan sunji abinda suke tautaunawa daga ciki , naunayen ajiyar zuciya nana  ta sauke tace "mu shiga sister ta fad'a tana  rike tiren hannun maryam  dake  k'okarin  subucewa qirjinta na dokawa tace  "a'a sister  ke dai ki shiga ke kad'ai  bari na tsaya anan  har  ki fito banason na shiga Ina jin tsoron kar ya disgani agaban abokansa ta k'arasa maganar tare da  d'aura  tire  dake hannunata akan tiren hannun nana hauwa .

suna  tsaka da hira suka jiyo sallama a bakin kofar falon MB ya bada izinin shigowa tare da komawa mazauninsa    ta shiga a natse ta  gaishesu  cike da ladabi  sai dai kallo d'aya zaka mata kasan ranta a 'bace  yake ta tsani taji yayanta yace bai son mrym ko aibantata  bare yau a gaban abokansa ."

Amar ya washe baki yana dubanta kana ya  soma  mata wasa kasance warsu abokan wasa   "a'a gasu cubi   hauwa  fa  ,farar mace alkyalbar  mata Ina ganin nida  madam  zamu  lalla'bo muzo  ki sammana man da kike shafawa kullum ke da maryam kmr bakwa fita rana,  gaku na nan  dau  kmr yanzu kuka sauko daga sama."

  tayi masa banza   tana jan tsaki a ranta "Ina kika baro mrym dan nasan ke daita 5&6 ne?  ta sake sharesa   tana kokarin   ajiye  tiren hannunta wayarta dake rike a hannunta tayi kasa zata fadi madadin ta bar wayar sai tayi k'okarin rikota  Aiko tiren  gbdy suka  sullube a hannunta sukayi kasa tiren  kifi ya kife nan take mai  ya fara malala  gabanta ya buga da karfi  nan take jikinta ya kama rawa   ta d'ago da sauri ta Kalli Inda ATA yake zaune gabanta na cigaba da fad'uwa ."

wani dogon tsaki ATA  yaja kana ya soma magana cikin fushi da zafin rai   "  kunga irin haukan nasu ba koina zaaje da waya kamar wasu  yan kauye "haba ATA  me yasa zaka dangantata da  Kalmar hauka tsautsayi ne ko babu waya a hannunta hakan zata  kasance "shawul karka goyi  bayan wad'an yaran sam babu abinda suka iya sai hauka komai na mata basu iya ba basu iya girki ba basu iya gyaran daki ba sam basu iya komai na mata ba yan iskan banza kawai  sai aikin rike waya  da surutun banza da wofi da  maza  kije ki dauko abinda zaki  gyara min guri kafin na soma kwallo dake, sai naci ubanku daya byn daya kafin na koma idan Kuma baki dawo kin gyara ba kika turo min masu aiki  sai na canza miki kamanni stupid kawai ."

fuuuuu ta fita tana zunburo baki   a bakin kofar  nana hauwa'u ta samu  mrym  tsaye duk ilahirin jikinta rawa yake gbdy  duk ta Kara firgicewa
Ta kalleta tana hawaye bata tsaya yi mata bayani ba ta wuce dan tasan taji komai  daya faru."
Kai tsaye   kitchen Inda hjy zulaiheart take  ta shiga  ita Kuma maryam ta gudu tayi dakinsu , nana hauwa'u  na gama shiga kitchen ta   soma zuba balai "wai mami  dole ne sai ya Adam   ya  auri mrym ne ."

"Dan girman allah me zai hana abar maganar kowa yaje ya auri wanda yayi masa  ? mami ta dubeta a natse  "me yasa kika fadi hk  hauwa wani abu ne ya faru  ?"to  gashi can sai faman fad'awa su ya amar yake wai bai sonta guntuwa ce  fari ne kawai ya  ceceta  mene mene  ko ance masa itama tana son shi ne ? gsky kiyi masa mgn ya daina  nima yanzu kafin na fito sai daya tozartani a gaban abokansa shiyasa wallahi ban so zuwa ba ,wallahi duk matar data auresa ta shiga uku da matsalolinsa  wallahi ni dai a fasa had'in nan da marsi  tana gama fad'ar haka ta juya fuuuu  ta fita  mami  tayi murmushin  takaici  kawai tana girgiza Kai ,nana  bata so komawa bangarensa ba amman babu yadda ta iya haka ta d'auki abun gyara ta koma kafin yaci ubanta  ".

******
Washegari  da misalin Karfe biyu   daidai  Kiran aunty shahida  ya shigo wayar mrym  tana    d'auka tace ki samemu a parlour'n mami  na biyu bata tsaya ji abinda  zatace ba ta katse Kiran ,shiru tayi tana sauke wayar daga kunnenta jiki a sanyaye ta mike ta d'auki mayafin abayar dake sanye ajikinta tayi rolling din kanta ta fito ta nufi parlour'n gabanta na dukan uku uku.

     zaune ta iskesu gbdy ya'yan  hjy zulaiheart 
banda  nana hauwa'u ATA zaune yana rike da waya yana daddanawa  sau dari zaka gansa to  da waya ne ko system yana operate "samu guri ki zauna aunty zabiba ta fad'a tana nuna mata kan kujera  kasa zama tayi a Inda ta nuna mata .
a hankali ta samu guri ta zauna nesa kadan dasu a qasa dan gudun balain ATA  ta kasan idanunta take qare masa kallo  sanye yake da dogon wando da riga mai gajeren hannu blue   da ratsin fari kayan sun yi masa kyau sosai ga gashin Kan nan nasa sai sheki yake wanda da alama yana shafa man gashi ne yasa yake fitar da sheki  ko yaushe ."

"Adam ga mryam  nan "inji cewar aunty shahida "naga  tantiriya mara kunya mara mutunci , uhm
Ina jinki ki  maimaita abinda kika fad'awa aunty  a gabana ".  sai da gabanta yayi wani irin  mugun fad'uwa taji wani abu ya tsarga mata tun daga qirjinta har zuwa kasan mararta  take taji  marata ta soma murd'awa  taji wani abu mai d'umi ya zubo mata wanda bata raba d'ayan biyu na tsananin tsoronsa ne."
Chapter 26 · 0% Book details