← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 43 OF 100

Sashe 43

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*****
Bayan  kwana  biyu  da  faruwar wannan  alamarin  maryama  tana tafiya  cikin  kayan  islamiyya ta Ardus-salam   yayinda  hannunta ke rungume  alqurani , yammaci ne duk  mazan  unguwarsu  sun  dawo  daga   aiki  duk  inda  ta  wulga  sai an  kalleta da  shaawar  tafiyarta   tmkr  bata  son  taka qasa tana   cikin  tafiya  taji  tafiya  abayanta  bata  juya ba dan  hakan  baya  daga  cikin d'abiarta ,  sai  ma   qara  saurin da tayi  ta cigaba da  tafiyarta saboda tasan  kowaye  ita yake  bi  zarginta  ma  cikin  samarin  unguwarsu  ne   dan  akwai  masu  nuna  suna  sonta  acikinsu ."

"maryama  wannan  uban sauri haka  da  kike  zabgawa ko dan gudun  kar  na  biyoki ne ?ta  tsaya cak  lokacin  data  fahimci  muryar malamin  islamiyyarsu ne  na Ardus-salam  mlm  yahuza  ta juyo a natse  ta  dubeshi  cikin nikaf dinta  tare  da  girmamawa ta gaishesa  ."ya  gyara  tsayuwarsa  yana kallonta , kunyarta  ita  tafi  komai tsoratashi  ,duk  iya  takun  saurayi  in  har  ya  had'u  da  mace  mai kunya  yana  samun  karaya matuka  a zuciyarsa ."

yayi  dan  murmushi  irin nasu  na ustaz "maryama  har  kullum zuciyata  bata  da  sukuni  jiddan wala  khairan  ,na  kasa mantawa dake  ,bani  da wani  sukuni  face na  samu  amsarki  game  da bukatata  dana  kawo  miki  ."yayi  shiru  tare  da tsayawa  yana sauraron  yaji  me  zatace  nan take  tayi  kicin  kicin  tamkar wacce  aka  tsare  da wuka  zaa yankata sai da ta  dauki  second  goma  sannan  tace "uhm  !sai   kuma  tayi  shiru  ta  qasa  qarasa  abinda zata fad'a  maganar ta makale acikin zuciyarta  shi  kanshi ganin motsa  lip's  dinta  bai  sawa ranshi cewar zatace  uffan ba  bayan  abinda ta furta  ba ."
ba  yau  bane farko haka  zalika  yasan  ba  yau  bane zai  zama   karshe ya  saba tareta a hanya  ta kasa ko  ambaton  sunan shi  bama shi  kadai  ba  kusan  mutane  suna  yawon  fad'ar  haka akanta   bata  da  yawon  surutu  da  saurin  sabo  da  mutun  duk wanda  ka  ganta dashi  tana d'ar d'ar  alamun  tsoro  shima dan matsayin  da  yake  dashi  na malaminta ne  yasa  har  ta tsaya akan  hanya  babu wanda ya kai ta tsaya  dashi  akan  hanya ".

"Maryama  idan  na lura  da yanayin  fuskarki  ba soyayyata bace  baki  amsa ba  amman kuma bazan  tabbatar akan cewar kin amsa  ba  ,tunda a kwayar idanunki kawai  nake  iya  karantawa shine kunya  ce ta  hanaki  ki  fad'ar   abinda  Ke  cikin  zuciyarki maryama  ki  daure  ki sanar dani menenê  acikin  zuciyarki  akaina  ko  zuciyata  zata  samu  sukuni da natsuwa  ?".

shirun  dai  da  baya  só  shi  tayi dan  bata  da  abinda  zatace  masa  ,bazata  iya  wata  soyayya ba  da'ace  ta d'aurawa  kanta  soyayyar  samari  da  lokacin da suke  guduwa  suna  barinta da ba qaramin  tashin  hankali  zata  shiga ba  gara  ta qarasa rayuwarta  haka  tunda  soyayya  ba  dole bane  arayuwar   mutun  haka  ma  aure   sunah ne matukar  mutun  zai  iya  rike   kanshi   domin  acikin
Sahbbai  ma  akwai  wad'an da  suka mutu basuyi aure  ba  dan  haka  mutun  zai  iya zamansa  haka   kuma   aure   da  haihuwa  bashi  bane   karshen   duniya  a ganinta  ko  babu  shi  mutun zai iya  rayuwarsa ."

"hakika   maryama   duk   cikin  unguwar  nan  kai  garin  nan  ma  gbdy  har  cikin  islamiyyarmu banga  diya  macen  da  take  burgeni   kuma   zuciyata  take dawainiya   da tarin  soyayyata  kamar ki ba ki samar  da  amsar  soyayyata a cikin  zuciyarki   ko zan samu farinciki da  sukuni  koda  ta  wata  sigace  da  zan fahimta ."sosai  hankalinta  ya  kai  kololuwar tashi  tama  qasa  tsayuwa  bisa kafafunta , kafafunta suka   shiga karkarwa  ,yana  son  ya  bata dama  ta  wuce  gida  saboda  halin  daya  karanta  atattare  daita amman  kuma  bai  gaji  da  kallonta  ba  kuma shi yasani ko zai kwana  tsaye  atare  daita  bazai gaji  ba , sakina  da kanwata ne suka  zo  zasu  giftasu malam yahuza  yayi  sauri yace "sakina ku tsaya  ga  maryama  tsaye  ku wuce  gida  tare ."

Shukura  ta  kallesa  tana  jin  wani  irin  tuttukin  bakinciki   acikin   zuciyarta   abun  yayi matukar  bata  mamaki  maryama  tare da mlm yahuza malamin da  take  matukar  só  amman  tsoro da  shakkansa   ya   hanata   fito  da  soyayyarsa
"malam ! kawai  tace  tayi  gaba  tana  jan  tsaki  acikin  ranta  dan tasan muddin  tayi a fili ta kad'e  har  ganyenta  dan  mlm  yahuza  babu wasa  wajen  disfila  d'alibai  da  iya  karatu  da  d'aukar  wanka  ga  tsantsar  kyau  shiyasa  kowani  d'alibi  ke  matukar  jin   tsoronsa  a kaf  ardus-salam  babu  malamin  da'ake   shakka  da só kamarsa  da yawa yammata  na   qaunarsa ."sakina  kam   jikinta  a matukar sanyaye  ta  wuce  batare  datayi  mgn  ba  maryama  ta  bita da  idanuwanta  wani  abu ya soki zuciyarta  domin tun safiyar yau ta lura  sakina  ta  canza  mata abun ya  matukar d'aure  mata  kai amman  tayi  mata  uzuri  da cewa yanayin  rayuwa  ne ."

Mlm  yahuza  bai  sake  magana ba sai  tunanin  kunyar  shi da sakina taji  dan  ganinsa  da maryama  yasa  ta  kasa  tsayawa dan haka  yace "maryama  sai  gobe  idan  mun  had'u  a makaranta amman  fa  kisani  bazan  ta'ba  daina  tsaidake  anan  ba har sai ranar  dana  samu  na  cire  kunyar nan  kika  amince min  "Kanta  kawai  ta  gyada  masa muryata  a  matukar sanyaye tace "sai  da  safe  ta  juya  ta  cigaba da  tafiya  a natse  bai  bar wajen ba  sai  da  tayi  nisa  sosai  ta 'bacewa  ganinsa  ."

yana  juyawa  sukai   ido   biyu   da  mlm  umar mai hausa  atare   sukai  murmushi "wato  kai  har  kullum bazaka daina  wahalar da kanka akan maryama ba  ko ?"Mlm yahuza ya qarasa  inda mlm umar yake ya tsaya  yana cewa "ya  zanyi  umar  allah  ya  jarabeni  da  soyayyar  maryama  bazan  iya hakura  daita  ba "kai   kuma  allah  ya  jarabi mata dayawa  da  sonka  ba ?"wannan kuma  damuwarsu  ce ,ai  dama  haka  zaka  fad'a  duk  kuna  son  maso  wani  ,kai  ma ka tausayawa masu  sonka  sai  allah  ya duba lamarinka  ".

"Allah  ma  ya sani  babu  wacce nasan  tana  sona  bare na tausayawa  ya fad'a yana wani  sham kamshi  "Uhm uhm  mutumina  banda  fad'ar son  rai   duk  wanda  ka  fadawa  haka  zai  d'auka  bakasan  abinda kakeyi  ba ,"kaga  umar rabani da wannan  zance  mu  barta  matsawar  bata  sarauniyar  mata zaka  min  ba "karka  duba yanayin  gidansu  maryama  amman  dai  kai  kanka  kasan  tafi  karfin  aurenka , maryama  macece  daya  kamata wani  hamshakin mai kudi  yayi wuf daita ."

dan  murmushi  mlm  yahuza  yayi yace "haka  ne  amman  ai  duk  mace   bata  fi  karfin  auren  nmj ba kuma  kowani   mutun  yana da nashi  matsayin  da  zai  iya  burge mace , kuma  ina  dashi  ina da quality da  mace  zata  soni  koda kuwa   bani   da  kosisi  bugu  da  qari  ita  mace  ba  kudi  take  bukata a soyayya  da  kulawa  take so ni  nan  kuma  zan  kula da maryama   ."

"da  me  zaka  kula  daita ?karka  manta  ita  din  cikakkiyar 'yar boko ce , yarinyar  da  idan  ta  fara aiki  yanzu  sai  ta  d'auki  nauyin ciyar da  mutanen  gidanku  gbdy  dan haka  banga abinda zai sa ka dinga wahalar  da  kanka  kana 'batawa kanka  lokaci  akanta  ba , kayi hakuri ka rabu daita  domin dai babban goro sai  magogin karfe ."

Mlm yahuza  ya  dan ji  zafin maganar  malam  umar dan haka ya  rage  farar  fuskashi "wai me kake  nufi ? kana nufin dan  ita din yar boko ce  tana da  kyau na bugawa a jarida  kana tunanin zata samu aiki  nan  gaba  zai sa ta  iya fin karfin  halittar  ubangiji "? yahuza  abinda  nake  son ka fahimta duk  wad'an nan  abubuwa da  kake  gani  fifiko ne a tsakaninka  da maryama  kawai  abinda  nake so  kaji  aranka  tafi  karfinka tafi  karfin  aurenka  ."

"kaga  dan  allah  mlm ka  barni ka zuba  min  ido ba wahalar banza nake  yi  ba ina cikin zuciyarta kunyar da take yawon nunawa akaina ta wadatar dani cewar nayi mata , nan  gaba kad'an zata fahimtar  dani  ."Ka  dai  bi a sannu kar  wata  rana  kana zaune wani hamshakin  mai  kudi ya shigo har cikin  unguwar  nan  ya  aureta .".

"bari  kaji  babu  wani  mai  kudin da  zai  aureta  domin  suma  masu kudin  sunfi  son ya'yan masu kudi yanuwansu , ita  maryamar da ba  galihu ne  daita  ba ,ai  ba uban da  zai  shigo  cikin  wannan  rubabbiyar  unguwar   ya   kwashta ai  duk wannan  kyawun  nata akan  irinmu  zai  qare "yana  gama fadar haka ya  juya  dan  baya  son  ya  sake 'bata  masa  rai ."

Tafiya  kawai  maryama  take zuciyarta  cike  da  kunci  da  tunani  barkatai  ba  kuma  akan mlm  yahuza  ba   sai  sabon  sauyin  data  gani  akan  fuskar  sakina  dan  na  shukura   mai  sauki ne idan  da  sabo  ta  saba  ita  da yaran  aunty  hassana  haka  suke mata  amman  sakina  fa  basu saba  haka  ba  suna  matukar  qaunar  junansu  tun  suna  yara su din  masoya  ne  na  hakika ."

da  wannan   tunani  ta  qarasa  cikin   gidansu   kai   tsaye   ta  nufi  bangaren su  sakina   domin  tambayarta  dalilin  sauyawarta  ashe  wahala ce  ta  shigo  daita  tana sallama  aunty  salma  tace " Yauwa maryama  d'auki   tsintsiyar  ki   share  min  d'akuna  tas   shine  amsar  sallamar  da aunty salma tayi  mata  kamar  tace  bazatai ba amman  ta  kasa  ta  ajiye alquranin  dake  hannunta  ta  d'auko  tsintsiya  ta  fara  shara  batare  da wata  damuwa  ba ."

tana  shara  aunty  salma  na  zaginta  ita  da  shukura   amman  sakina  na  zaune  batace  komai  ba  sa'banin da da bata  yarda a  zageta  ko  sakata aiki  akan  idanunta  ,tana  shara wani  gurin  da  simiti  wani gurin babu  ga  kuma  sakina  na   zaune ta  d'ago  idanunta  a  natse ta  kalleta  taga  kurar sharar  na zuwa inda  take  muryata a sanyaye tace "sakinata   ina  ganin  sai  kin  d'an  tashi  kinga  kurar  tana  zuwa  inda  kike  ta  wani  watso  mata harara  "ai  gudun  ruwanki  nake  kallo  naga zaki shareni  ko  kuwa   ."?

maryama  tayi  shiru  tsaye  tana karantarta  akwai  wulakanci  acikin   maganarta  "ke  kika  kyaleta  aunty  sakina  amman  banda  jakanta  irin  nata tana   kallon  mutane  suna  zaune zatace  su  matsa , banza  shasha  kawai   mai  siffar  mayu ." inji  cewar  shukara  dake  zaune  kusa  da  aunty  salma  abun  bai  yiwa  aunty salma  dadi  sosai  ba  domin  kuwa  sakina taso ta furta ma  maryama  haka  ba shukura ba  ,sakina  kam  tun maganar  farko  datai  bata  qara ba  ta  tashi  cikin  bacin  rai  ta  shige  daki tana jin  wani  zazzafan  kiyayyar  maryama  ."
Chapter 43 · 0% Book details