← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 100

Sashe 30

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

" mrym tashi ki shiga  ki d'auko min wayata a daki na kira naji yadda ake ciki  ta  mike  tsam ta shiga cikin  bedroom din hajiya zulaiheart ta iske wayar akan katifarta ta d'auka tana duba fuskar wayar nan take gabanta yayi wani mummunar fad'uwa  sakamakon idanunta daya sauka akan hoton ATA  tayi shiru tana kallonsa cikin suit bakake  idanunshi manne da farin  glass yayinda  fuskarsa ke  d'auke da murmushin gefen baki wanda bai gama bayyana ba hakan km qara masa kyau  yake , ta lumshe idanunta tana Jin wani iri a gbdy ilahirin jikinta ,ada sam bata jinsa aranta amman  tun sanda  yasa  akayi kiranta akan batun soyayyarsa ta soma Jin wani Abu akansa komai nashi mai kyau tamkar shi ya hallici kansa ."

jiki a sanyaye ta Kai mata wayar  ta amsa tana kokarin neman layin uncle jay byn sun gaisa take tmbyrsa halin da'ake ciki "mgn dai daya ce nace  abarwa Allah abar ruhin diyata ya samu salama  ".
"uncle jay taya zaka fadi haka  byn kasan zuciyar  sha'awanatu  bazataji dadi ba   ? "nasani   amman  yarinyar nan da ake tuhunma  ba itace tayi kisan ba , tabbas makashin mutun d'aya ne da wanda ya kashe mubina da wanda ya kashe sadear mutun d'aya ne  amman ba wannan yarinyar bace, ita dai ta taka tsawun barawo ne gbdy bincike ya nuna makashin da hannun hagu yayi kisan  ita  Kuma hadiza  hannun dama take amfani dashi  sam gbdy babu alamun sheidar hannunta  ,yanzu  haka an gama duk wani bincike  ranar monday kotu zata wanke  yarinyar Allah dai ya jikan  mubina yasa ta huta  "Ameen Hjy zulaiheart ta furta a fili tana mai tausaya masa "ko me suka yiwa wannan makashi da yake musu kisan gilla?   "Allah masani  "sun dan jima suna waya sannan sukayi sallama .

"Maryam ...!" mami  ta kira sunanta gbdy ta tattara duk wani attention dinta zuwa gareta tana kallonta "Ina saka rai zuwa  karshen satin  nan za'a yi mgnr bikinku  da  Adamcy  " gabanta ne ya sake fad'uwa kmr zai fasa qirjinta yayo  waje "ya kamata ki sake kwarewa agurin girki da sauran abubuwan da yake da bukata  dan haka daga yau kice zaki cigaba da kulawa da komai na bangaren abincinsa  kinji ko ".
ta gyada mata Kai  kawai tare da amsawa da "to !" hawaye na ciccikowa acikin kwarnin  idanunta tayi saurin dennewa  ta rasa dalilin da take tsananin Jin  tsoronsa da tsoro  aurensa."

"  ki  samu natsuwar zuciya ki tashi kije yanzu ki tmbayesa abinda yake bukatar ci a hankali ta mike jikinta na rawa kamar mazari  ta nufi part dinsa
akan hanyarta ta tsaya tana  daidaita natsuwarta sannan ta k'arasa kofar shiga falonsa tayi sallama ba'a amsa ba har ta juya taji sautin muryarsa yana cewa ",waye ne ? ta juyo da sauri "ni ...nice ta fad'a da sauri jikinta da bakinta na rawa "ke wa kenan ? ya sake tmby tayi shiru jikinta na cigaba da rawa hawaye na sake cikowa a idanunta  ta rasa dalilin  hawayen  nata  Jin shiru yasa ya taso da kyar yana mika  daga shi sai gajeren wando  army  green  iya cinyarsa da farar singlet wanda suka bayyana  surar  jikinsa a fili ake iya ganin  kwantaccen sumar dake kwance  a cinyarsa  da  qirjinsa haka kan nipples dinsa  sai farin silifas dake sanye da kafafunsa da farin agogo da alamun aiki yake ."

A tsaye ya ganta a bakin kofar gbdy bata cikin  haiyacinta a hankali ta d'ago ta  kare masa kallo saboda kusancin da suka samu muryarsa a kasalance yace  "ke lafiyarki  tsayuwar me kike yi anan  ya fad'a fuskarsa a murtuke"kayi hakuri please mami  ce tace nazo na tambayeka abinda zaka ci a girka maka "  ya tsuru mata Ido  a zahiri yake iya hango yadda qirjinta ke  bugawa wani dogon tsaki yaja a fili ya juya ya koma ciki ya barta tsaye . juyawa tayi tana daga kafafuwanta da kyar ta dawo parlour'n ta tsaya hjy zulaiheart ta dubeta "yaakayi me yace zai ci ?hannuwanta ta tsarke cikin juna sannan ta bud'e baki da kyar "wai a dafa masa komai."

mami  ta fad'ad'a fuskarta da murmushin jin dadi , ita Kuwa nana hauwa'u sarai ta fahimci wani abu a tattare da marsi tasan sarai ba abinda yace mata  kenan ba   "to shikenan maza ki shiga ki dafa  masa  abinda  yazo cikin tunaninki amman ki natsu sosai kinji. "ta gyada mata tana cewa "sister muje ki tayani "me .....?dan girman Allah ki rufa min asiri na tsira da mutuncina ke dai kije Allah ya bada sa'a kiyi kokari yayi dadi  sosai ta k'arasa maganar tana kakkabe hannunta. "haba sister ki taimaka mana kin san fa  komai tare mukeyi ,nasani amman ban da wannan wallahi bazan Saka hannu ba abinci yazo bai yi dadi ba ya had'amu yaci ubanmu"  hjy zulaiheart tayi murmushi "Kai Adamcy hukuma kowa tsoronsa yake ji amman Kuma fa yana da sauki Kai Kinga mryam  yi tafiyarki kinji  duk abinda baki gane ba kizo ki tambayeni Simi Simi ta juya ta shiga kitchen kmr ta daura hannunta  tayita kuka dan tasan muddin tayi kuskure sai yaci ubanta duk iya k'okarinta na dafa  masa rice and stew bai ci ba ya wuce juma'a ."

*****
Da  misalin  karfe  biyu  na  rana  bayan  an  sauko  daga massalaci  hajiya   zulaiheart  da  kanta  ta fito  zuwa  haraban  gidan ta fara  rabawa yaran dake shigowa haraban estate din sadaka  wake da shimfa  acikin takeaway fari tare  naira dari  biyar biyar sababbin yayinda  ATA  ke tsaye daga can nesa kadan da inda take kunnensa manne da waya yana tafiya a hankali irin na jinin saurarata dan sauranta  yaki   barin jininsa komai nashi  irin nasu ne sanye yake cikin farin yadi voil  kafafunsa sanye da takalmi fari haka ma Kansa sanye da hula fari mai ratsin  baki  yayinda tsintsiyar hannunsa ke d'aure da  agogon silver rolex   yayi  kyau sosai kamar ka sacesa ka gudu  sai dai kallo d'aya zaka masa kasan   zuciyarsa dakushe take  da tsananin damuwa ."

tsayawa yayi cak yana cigaba  da kallon mahaifiyarsa  cikin haka ta  juyo  nan take  suka had'a  Ido daita ya sakar mata  taadaddaden murmushinsa dake sake bayyanar da ainihin bawar kyawun da Allah yayi masa wanda wannan murmushin babu mai ganinsa sai ita , murmushi
ta sakar masa cike da farinciki ganin murmushinsa  da ba kowa yake gani ba tana tsananin son kyakkyawan tilon  d'anta shi  din dabam ne acikin zuciyarta  ,uwa Uba nagarta   tana   masa so mai  tafiyar da ruhi shine karfin  gwiwarta ."

a hankali  ya soma takowa zuwa Inda take har ya k'araso gareta ya tsaya kusa daita yana tayata rabawa yaran kudi duk wanda ta bawa takeway sai ya mika masa kudi  ,tana raba abinci  tana dubansa tana murmushin jin dadi "thank you my beloving prince  " you're welcome my  queen ya fad'a yana kallonta  bayan sun gama  tare suka koma ciki  suna tautaunawa a falonta  sukayi  masauki ya zauna yana runtse idanuwanshi."Adamcy nah...." !
ya amsa  can kasan makoshi" inshallahu wannan satin zanyiwa su  baba babba maganar aurenku ayi a wuce gurin muryarsa a raunane yace "to sweetheart kuyi duk abinda ya dace na sallama miki komai ."

"bangane ka  sallama min komai ba kana nufin bazaka tabuka komai ba ?"me kike son nayi sweetheart idan akwai abinda kike bukatar nayi ki sanar min zanyi ganin  idan  ya  cigaba da biye mata  maganar auren zasuyitayi yasa yay  saurin  runtse idanuwanshi yana cewa "wayyohhhly sweetheart cikin kwantar da murya tace "ya'akayi Adamcy ? "sweetheart  yunwa nake ji cikina har ya fara zafi murmushi tayi   "ko kunya baka ji ba kmr wani jinjiri ka dai rage wannan shagwabar ka bar wa yaranka  "a'a sweetheart ki barni nayiwa uwata  suma idan sunzo ga guri nan kowa yayiwa mamansa "to ai shikenan bari nasa maryam ta samarmaka abinda zakaci "wace mrym kuma dan Allah kiyi min da kanki karki rage min Jin dadi wannan yarinyar babu abinda ta iya Kuma ma nafi son Ina cin abinci daga hannunki  ni dai gsky banason abincinta "ya Isa sarkin naci amman dole kaci daga hannun matar da zaka aura wata rana ."

"naji amman  ayi sauri ayi min please dariya ya bata sosai  wai ayi sauri ayi mishi  ATA  kenan ko  yaushe idan yana tare da mahaifiyarsa daukar kanshi yake kamar karamin yaro hjy zulaiheart ta d'auki wayarta ta soma Neman layin maryam  sai dai bai shiga ba ta ajiye wayar tana Kiran daya daga cikin masu aiki ."

Tana zaune a d'akinsu  hjy zulaiheart ta  Aiko mai  aiki akirata da hanzarinta ta Isa parlour'n tace "kije ki kawowa Adamcy wani Abu yaci yunwa yake ji ta Dan saci kallon Inda yake tana Jin mummunar fad'uwa gaba  sannan ta gaishesa  sai dai bai Kalli Inda take ba bare ya amsa gaisuwarta  ,Kai tsaye kitchen ta nufa sai dai ta rasa me zata dafa masa shap shap yaci ,kawai tayi tunanin daura masa indomi da kwai ta kawo masa a lokacin data  fito  bata  tarar da  hjy zulaiheart ba sai aunty khadeja  zaune agurin suna magana da ATA ta ajiye akan table din dake gabansa tare da gaishe da aunty khadeja kamshin  indomin da yaji ya ziyarci hancinsa ya balain ta'ba zuciyarsa na take ransa ya baci .

a hankali ta juya zata wuce dan Sam bata jurar tsayuwa a duk Inda yake muryarsa a kasalance yace"ke meye wannan kika kawo ? ta dawo a hankali ta tsaya  tare da cewa  "indomi da ......"a fusace ya dan gyara zamansa ya tsaidaita  "shine abinda kika iya dafawa?  jikinta na rawa ta dubi aunty khadeja dake zaune  tana juya masa Kai "nace shine abinda kika iya dafawa ?ta girgiza  masa kai jikinta na rawa gbdy a tsorace take a tsaye,shi kuwa  kallonta kawai yake da seyx eye's dinsa wanda hakan yasa hantar cikinta cigaba da kadawa  lumshe idanunshi yayi tare da yin shiru  ya  koma ya jingina  jikinsa  da kujerar da yake zaune ya soma motsa labbansa   "wai  irin wannan matar ake min  sha'awar  ajiyewa a gidana  ?yayi mgnr a fili  yana sake jan tsaki a fili "wacce irin  sakariya mata ce wannan khadeja saboda rashin tarbiya indomi fa me zanyi da ita ?
Chapter 30 · 0% Book details