← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 48 OF 100

Sashe 48

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tana  gama  fadar  haka ta  mike  a hankali  tana  share hawayen idanunta  da  suka  gagara tsayawa  tana  jin  wani  zafi a qirjinta , bazata  cigaba da d'aukar  wannna  nauyin  ba , koda  aunty bata  amince  ta  koma  ga yan'uwanta  ba ,lallai  ita   zata nemosu  a duk  inda  suke  acikin garin  nan  ."muryarta  a sanyaye  tace "umma ni   zan  wuce  sai   da  safe  " kai  kawai  ummah   ta   gyada  mata  sannan   maryama   ta  fara  tafiya  umma   tayi   shiru   tabi   bayanta da  kallo  tana  kallon  yadda  take d'aga  zara  zaran yatsun kafafunta da  kyar  tamkar  wacce  bata  da laka ."

  " A inda  ta  bar  mahaifiyarta anan  ta  sameta  tare  da  habib suna  hira  da  alamun shi  baya cikin  damuwa   kamar  ita." bata   tsaya  ba  byn  tayi  sallama tace  "aunty  sai  da  safe  tana gama  fadar  haka  ta  wuce  ta  nufi   d'akin   baccinta  bayanta suka   bita  da  kallo , yanayinta  kad'ai  ya  fahimtar  da  aunty  akwai  tarin  damuwa  atattare daita  shiru  kawai  tayi  tana  tunani "har  yaushe  maryama zata yi  farinciki  arayuwarta  ?".
A natse  aunty  ta  mike tabi  bayan maryama  tana  jin  tsinkewar zuciya  haka  shima  habib  akan kujerar  da  take  zama  idan  zatai zane  suka  isketa  ta  dafe  kanta  tana  sheshekar  kuka  atare  suka qaraso  suka  zauna  abakin  gado  suna   fuskantarta  shigowarsu  yasa  ta   tsaida  kukanta   wanda taso tayisa  sosai  har  taji natsuwar zuciyar."

    dogon  numfashi  aunty  taja tare  da  cewa "na  shiga  uku ni bilkisu   " ta furta cikin tsananin tashin hankali dan  bata  qaunar  abinda  zai d'agawa  yaranta  hankali  shi  kuwa  habib  hannun  maryama  ya  kamo  cikin  nashi  ya  damke da  karfi  cikin   tsananin  tashin hankali " heartbeat  meke damunki ?." muryarta  a  raunane tace  "babu  komai after dad "ya  babu  komai  zaki  shigo cikin damuwa  , yanzu  mun shigo mun ganiki  kina  kuka  amman  kice  babu  komai  ki fad'a min idan akwai  abinda  ke  damunki  ."

shiru  tayi  tana  cigaba  da  shesheka "ki  sani  bamu saba  boyewa  juna  komai  ba  idan kika  min  haka  baki  min  adalci  ba  ,ko  km damuwar  dazu ce  ? still  dai  shiru tayi  ,sosai  suka  d'aga  hankalinsu  ita  kuma  taki  cewa  komai  sai faman  ajiyar  zuciya  ta  saukewa ." damke  hannunta  ya sake  yi  sosai  yana  rokonta "dan allah   heartbeat  karki  daga  mana hankali  ki fad'a min kukan me  kike yi  ?kallonsa  kawai  tayi  tana lumshe idanuwanta ganin yadda  hankalinsa yay matukar  tashi da yadda ya  d'aga  hankalinsa  ya matukar bata  tausayi  daman kuma haka ne idan daya yana cikin damuwa dole ne daya shima ya tsinci kanshi cikin damuwa."

  "Yanzu princess bazaki koyi dauriya akan kowacce irin damuwa bace domin ki tsira da rayuwarki da rayuwarmu gabadaya ,Ke kenan kullum cikin zubar da hawaye akan damuwa me yasa zaki dinga asarar hawayenki  tare da qoqarin kashe kanki abanza ."?
"Gara dai ki fada mata gsky aunty domin ita rayuwar nan da take ganinta wani lokacin idan abubuwa suka wa mutun tsanani dole mutu ya rage wasu abubuwa domin tsira da rayuwarsa da lafiyarsa."
hawayen da take qoqarin maidawa ne suka samu nasarar gangarowa bisa kuncinta cikin sauri tashiga gogewa wasu na sake gangarowa duk  yadda  suka dinga kwantar da kai da murya dan  suji  damuwarta amman   taki  fad'a masu komai domin da zarar ta bude baki hawaye da sheshekan kuka Ke hanata magana dole tasa suka daga mata kafa suka  fice  d'aya  bayan  d'aya daga dakin  da zumar  zasu  lalla'bata  gobe ta fad'a  masu dalilin kukan  ."

tafi  mintuna  goma  byn fitar aunty  da  habib   zaune  sannan  ta  yunkura  ta  tashi  tana  sauke naunayen  ajiyar  zuciya ta shiga bayi  ta d'auro  alwala ta  fito ta gabatar  da  sallahr magariba da isha'i  tare  da  shafa'i  da  wutiri byn  ta  idar  ta  koma  kan  katifa ta  zauna  tare  da  jingina bayanta da  pillow  ta  rungume hannuwanta  duka  a qirjinta ."

ahankali  ta  runtse  idanunta  tana tariyo  komai  daya  faru  dasu tun suna  yara  "Kenan  adalili  rasa  mahaifi  da  kaka  yasa  rikonsu  ya dawo  hannun  abban  sadam  ."tun  tana   qarama yar shekara hud'u a  duniya ta  taso cikin so daga  bangaren  abban sadam da umma  da  mahaifiyarta   amman  daga   bangaren  aunty  hassana  da  sauran  'yan'uwan  mahaifinta   kuwa  saboda  haushin  da kiyayyar  mahaifiyata  yasa  suka dinga   nuna  masu  tsana  da tsamgwama ,  sun ci wuyarsu  sosai  most  especially  Ita   ganin kiyayyar  dangin  mahaifinsu  da irin  tsanar  da  baba  gali  yayi masu  ya  bawa  aunty  salma  damar  cin kashi  akansu  da mahaifiyarta ."

tun  daga  lokacin  kuruciya har zuwa  girmanta  abinda  yake  rage mata  zafin  gidan  shine soyayyar umma  bancin  ita  kowa a gidan baya   sonsu amman kuma  wani lokaci   shi   kanshi  baba gali  ya kan  tausaya masu  in dai ba fad'a sukai  da  sakina  ba ko  yarshi qarama  ba , idan  tayi  mata  laifi ta  d'an  daketa  shine   zai  fito da 'bacin  ransa  har  ya  fito  da  zallar  kiyayyarsa  ,kuma  tun da ta lura  son ya'ya ne  dashi domin ba ita ba  ko uwar  data  tsugunna ta haifesu  baya  raga  mata  akan ya'yansa  ."

"yayan  baba  gali  uku  ne aliyu sakina  wacce sa'artace  sai mai bi mata  salamatu  wacce  taci  sunan hajiya  kakarsu  ana  kiranta da shukura  bata  fi  shekara sha bakwai  ba a yanzu ,itama babu yabo  babu  fallasa  suna  d'an  shiri  daita  sai  dai  idan  taga uwarta  na  fushi  da  zagina bata hanata  sai  ma  dai  ta zugata domin  itama  tana  nuna kishinta akainta  idan  taga  umma tana tarairayata ko wani ."
Baba  gali  dinki  yake  ada  rasuwar abban  sadam  yasa   gidan  buredi da  rikonsu  ya  koma  hannunsa  alhamdulillah  babu  laifi  ita  din mai  qokari  ce  ta  kowani fanni boko da arabic ga baiwar zane da Allah  ya  bata ."

Alokacin  baya  kullum  ta  allah  sai  aunty  tayi  masu  special  lesson  ita  da  habib  kusan kokarinta ta samu ne a wajen mahaifiyarta  ,duk  unguwar da makarantarsu  ana  maganarsu akan  ilimi  bokon  da suke dashi haka  duk  gidan  ba masu  jin   turanci  kamar  ita  da  habib ko wani  abu  za'a  tambaya  ita ko habib  ake  tambaya mahaifiyarsu ta  tsaya  masu  akan  karatunsu shiyasa  ma  education  dinsu  yayi  very  fast  kuma à sanadiyar qoqarinta ita da kawarta subai'a yasa gwanati ta dauki nauyin karatunsu zuwa lagos state university ".

   bangaren sakina da  sauran  yaran  gidan  matsalar  iyayensu ne dan  basa  maida hankali  akan karatun  yaransu  gashi  sam  basu da  isashen  ilimin  boko ko Arabic barin  ma  aunty  salma  karta ji labari  ba  arabi ba boko sai  uban girman  kai  ,sau  tari  idan shukura tazo   koyon  wani  abu a wajenta bata  só  sai  ta  nuna  ai  itama tasani  dan  me  zatazo  wajenta akarshe  idan  tayi  mata  zero take samu  a makaranta shiyasa da  yarinyar  ta gane ta daina  bata  idan tace ta kawo kai  tsaye  take ce  mata  bataso   zero  zataci ."

hatta  alwala  ba  daidai aunty salma  take yi ba  kuma sallah ma bata  dameta  ba  ,tun  suna yara baba  gali Ke  mata   fad'a  akan tarukun  sallah din  da take yi amman  taki  ta  daina  shi  kansa daya  gaji  sai ya  rabu  daita ya dinga  Kwa'bar  yaransa da yin sallah  sanin  in  har  dan uwarsu ne sai  dai kar su yi  babu abinda ya  dameta dan  idan ma  koyi zasu yi  daita  sai  dai su  koyi taruku sallah."

Su  kuwa  aunty  bata yarda tana gama  dauro  alwala  zata  tura habib  zuwa  masalaci  ita km ta umarceta taje  tayi  alwala sannan  a  kullum  dare auty  ta kan fito  tsakar  gidan  tare dasu  har  sakina  kasancewar  tana  qaunarta  ta  koya  masu  darasin lissafi , tana  daukar  lokaci akansu  har sai  taga sun gane sannan ta bukaci  wanda yake da damuwa a bangaren  karatunshi ko baka da matsala  zatai  'yan  tambayoyi  ana  bata amsa  idan bata gamsu da  amsar  ba ta qara yi masu  bayani , bangaren  karatun alqurni kafin  suyi  bacci  sai  aunty tasa sun  karanta izawaka  da tabaraka kafin  su  kwanta  da  safe kuma sai  sunyi murajaa  alqurni sannan su shirya su wuce  school  ko islamiyya ."

A ranar batayi  isashen  bacci ba  ga tsananin  tunani  ga  kwadayin son  ganin  yan'uwan  mahaifiyarta  gargadin  kanta  ta shigayi   akan fad'awa  soyayya  da ma ko waye idan  kuma  soyayyar ta zama dole sai  dai  tayi a gidan aurenta  ga duk wanda ta aura har  asuba  tayi maryama batai   wani  yi  baccin  kirki  ba shiyasa  kiran  sallahr  farko  acikin kunnenta  akayi   ta  gyara kwanciyar  ta koma  ta  kwanta bacci   kad'an  tayi ta  lalubo wayarta  ta  duba  taga biyar da  rabi   saura  lokacin  sallah yayi dan har an  tada sallah a matsalacin unguwarsu ."

a hankali ta  mike  zuciyarta cike da damuwa bakinta dauke da  adduar   tashi  daga  bacci ta kai tafukan hannunta tana shafa fuskarta sannan a natse ta zuro kafafunta ta sauko ta  shiga  bayi ta dauro alwala ta fito cike da sanyin jiki ta  gabatar da sallah asuba  byn ta idar  ta d'auko  alqurni ta soma karatu  cikin suratul  baqara anatse ta  kai idanunta  ga  window d'akin taga gari ya  fara sha tayi azkar  din safe tana nan zaune tana lazimi har shida  saura sannan ta koma ta kwanta akan sallaya nan da nan  bacci mai nauyi ya dauketa ba ita ta tashi ba sai goma saura ."

Ta  mike da  kyar  bakinta  dauke da  salati  sakamakon qirjinta dake wani irin bugawa ta 
gyara gadonta ta fita ta dauko tsintsiyar  shara
ta  share d'akin  ta fito har falo ta shiga d'akin  mahaifiyarta  bata  ganta ba   tasan may be ko tana byn gida wajen yin wanki ,dan wannan kaida ne  kullum safiya sai  tayi  wanki  kayanta wani   lokacin  da nasu  ta  share d'akin  tasss ta fito da  sharan zuwa falo ta  shiga  kitchen ta hada kayan wanke wanke ta wanke atake  ta goge koina ta sharo sannan ta hada da share falo tayi mopping ta koma daki ta cire kayan jikinta ta shiga wanka bata wani jima ba tayi alwala ta fito kai tsaye ta shimfida daddumar sallah ta sallacci salatul duhu byn ta idar ta shirya kanta ta kwanta lamo cikin zullumi ta kamkame jikinta waje daya wani iri take ji a duk gbdy ilahirin jikinta soyayya irin wacce iyayenta sukayi bazata ta'ba yarda ta jefa kanta cikinta ba".
Chapter 48 · 0% Book details