← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 66 OF 100

Sashe 66

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

    ta shirya cikin wata doguwar rigar   atamfa   yellow  touch  of   black atamfar   ba  wata  sabuwa bace  dan  ta  dan  kode  sai  dai  fés  take  agoge  sai takalmi flat  kasancewar maryama mayar saka flat ce cikin kankanin lokacin habib ya fito yana kiranta yana d'aura agogo a tsintsiyar hannunsa na gama ke nake jira fa "ganin nan   fitowa   nima na gama hijab  kawai  zan  saka  da  nikaf ,byn   second   biyar   ta  fito  suka yiwa aunty sallama "sai mun dawo aunty ."

" to sai kun dawo Allah ya tsare min ku habib ka kular min da yarinya na baka amanarta yayi murmushi yana cewa "to ni kuma wa zai kular miki dani ? ."kai   wannan yaro   wannan yaro akwai manyamce  ku dai je Allah ya tsare karku dade suka fice suna fitowa suka hango yaya sadam a haraban gidan hannusa  daya  rungume a qirjinsa yana waya da murmushi akan fuskarshi suka gaishesa hannu kawai ya d'aga masu suka wucesa ."

Basu suka dawo gidan ba sai daf da magariba habib ya wuce massalaci maryama ta cire nikaf dinta tare da hijab ta fad'a bayi domin yin alwala bayan ta idar da sallah suna zaune sai ga dan sako daga umma cewar tazo babu ' bata lokaci ta mike ta nufi side dinta bakinta d'auke sallama ta shiga a natse kamar koda yaushe umma tana zaune a parlour'n   gefenta yaya  sadam ne zaune ya d'aura kafafuwansa duka a saman table yayi crossing leg's dinsa suka amsa mata sallamar ,cike da girmamawa ta gaishesu sannan
ta samu waje ta zauna tana fuskantar ummah " .

"yauwa maryama gobe  idan Allah ya kaimu zamuyi baki daga cikin gari zasu zo Ina son dan allah gobe da safe kizo ki tayani aikin kaji dazu na aika kizo aka ce kin fita  tare  da habib har na aka Islam ta siyo  min kayan miya ina ganin gobe ma tare daita  da  sakina zaku tayani aiki ."
"To shikenan ummah Allah   ya  kaimu zuwa karfe goma yayi ko karfe nawa kike bukatar nazo"? tayi mgnr cikin jin kunya ,"eh to zuwa tara ma yayi ,maryama ta d'an jima suna hira da umma yayinda sadam Ke waya."ahankali ta mike tai   mata  sallama ta dawo side dinsu tana sheidawa mahaifiyarta bukatar ummah dan haka bata tsaya yin wata doguwar hira ba dan lokaci ma ya fara tafiya kai tsaye taje tayi sallah isha'i ta kwanta bacci dan ta  samu ta  tashi da  wuri ."

washegari tun bakwai na safe ta tashi ta fara da gyara d'akunan su karfe takwas da rabi ta kammala da aikinta na yau da kullum sannan ta nufi   side din ummah ta fara kama   mata  aiki sakina da  Islam  na zaune basu da ma alamun saka hannu har sai da yaya  sadam ya buga masu tsawa sannan  Islam  da sakina suka  kama mata aikin kajin, saboda ganin aikin da maryama take yayi mata yawa , wanda ita ko ajikinta dan ko ita kad'ai aka bari da aikin zata kammala komai ta tashi ."

d'aya bayan d'aya mutanen gidan ke shigowa hatta baba gali sai daya shigo cikin tsananin murna da zuwa bakin da zasuyi wanda ita maryama aranta take raya irin bakin da umma zatayi hakika ko su waye lallai masu matsayine a gun kowa dake cikin gidan tunda take a gidan bata ta'ba ganin hakan daga garesu ba, baya farincikin da suke ciki har da  hidmar wanda ke nuna wani mai matsayi ne zai zo ."

Sosai ta kasa kunnuwanta tana son ko kad'an taji irin bakin da zasu zo amman bataji komai ba sai dai ummah da aunty hasana da aunty salma suna ta hira   akan bakon da alamun sun san wanda zai zo alhji  alqasim maude   kenan yaushe rabon shi da kasar nan?".

"Ke ai kudi sunyi wallahi dan baki ta'ba zuwa gidansa ba wannan yar wayewar da kike ganin kina dashi sai kin nemeta kin rasa inji cewar ummah ,aunty hassana tayi murmushi cike  da  jin  dadi "haka naji abakin babansu sakina ya ta'ba zuwa tare da abban sadam allah ya jikinsa da rahma yace aljannar duniya ne gidansa kamar ba qasan nan yake ba su kansu mutanen unguwar da yayi ginin kallon gidan suke ."aunty salma ta  fad'a  tana  tafa  hannuwanta ."

Sai yanzu maryama  ta gane waye zai zo abokin abban sadam ne wanda sukayi karatu tare tun daga  primary har zuwa diploma har suka girma sukayi aure dake shi alhji alqasim maude yayan mahaifiyarsa yana siyasa shi ya samammarsa shcolaship zuwa qasar india ya wuce tare da matarsa wannan ya dan yanke zumuncin abban sadam dashi sannan mutuwa ta qarasa gabadaya sai dai jin rasuwarsa ya mugun d'aga masa hankali sosai ."

mutuwarsa ya dawo da zumuncinsu ya d'aure sosai shine ma ya d'auki nauyin karatun yaya sadam har ya qare karatu kuma shine mutumin daya samammar masa aikin da yake yi ahalin yanzu a awaf  ,alhj  alqasim maude mutun ne mai kirkin gaske da sanin darajan mutune da taimakawa talakawa a yadda ta samu labari duk ya kwashe ya'yan yan'uwa zuwa kasashen duniya wasu na karatu wasu na kasuwanci shine ma ya bud'ewa abban sadam gidan buredi kuma yana taimaka masa a duk   sanda yazo qasar "

Umma ta mike tsaye rike da wayarta sakamakon qarar data d'auka ta nufi hanyar shiga side dinta dake a tsakar gida suke aiki aunty salma na gani ta tashi tace "sakina Islam   ku  cire hannunku haka nan ku huta ku barwa   yar wahala ta cigaba da aiki tunda dama ita ta saba aikin neman suna da  neman  gindin  zama  ,wallahi  ba  ai kin kyauta salma  daman tun   dazu  nake  son  dakatar  dasu
su bar   shegiya  yar  wahala  ta cigaba  a  haka rayuwarta  zata  ware  bauta ,maryama ta kallesu batare data ji zafin maganarsu ba, dan aiki kam matukar na umma ne zatayi shi sai inda karfinta ya qare ,tayi nasu ma da basu da aiki sai nacin zarafinta bare na umma ,ta cigaba da aikinta ta dauki wata roba ta qarasa inda  korfot yake ta wanke shikafar dake ciki ta bud'e tukunyar dake kai ta zuba shimkafar cikin ruwan zafi tana cikin aiki shukura ta fito daga side dinsu ta zauna adaidai lokacin umma ta fito ."

Aunty hassana da aunty salma  har  ma  da  ya'yansu suna hira ummah ta kalli sakina da shukura da islam  zaune suna tayasu hira ta kalli maryama dake  faman dikar aiki "a'a ya zaku bar maryama da aiki ita kadai Ke shukura sakina islam kusa hannu kuyi tare mana na gayyatoku ne dan kutayani aiki ba dan ku zauna kuyi hira ba ,maryama ta fahimci maganar ba dasu shukura kadai ummah tayi ba har dasu aunt hassana tayi cikin rashin son aiki suka qaraso inda take gyara kaji shukura na kunkuni wanda bazai kai ga kunne ummah ba , maryama tace "kinga shukura idan baza kiyi ba ki koma ki cigaba da zamanki idan ma gbdy bazakuyi ba ku barshi duk zanyi dan kawai an sakaki aiki zaki dinga wa ummah kunkuni
ta watso mata harara tare da kallon banza "ke ki kama kanki dan na lura tunda mlm yahuza ya dawo da neman aurensa kaina kike min kallon gani gani nake miki kallon gani gani ko kike min ?"
maryama ta fad'a  a dan hassale  tana  hura  hanci .

"Ban sani ba banza kawai mai bakin jini sai wani 'bare 'bare kike dan kinga mai kudi zai
zo , abinda kome zaayi na banza né tunda babu abinda zai haifar sai cigaba da  zaman gida da yawon  ta  zubar  wai  ana  zuwa  bautar  kasa "Ke ni kike gawa magana "? an gaya  miki me zakiyi ?"ai maryama cikin fushi ta zabga mata mari wani qara ta saki tana dafe  kuncinta wanda yasa aunty salma da duk wanda suke wajen suka juyo zuwa inda suke ita kanta irin qarar da shukura ta saki sai da gabanta ya fadi ta tabbatar yau ta dibowa kanta ruwan dafa kanta "kutumar uban can   me tayi miki kika zabga mata mari haka ?"aunty salma ce akan maryama take neman ba'asi cike da maseefa."

Maryama tayi shiru tana datasanin Marin datai mata hakan shi ya fusata aunty salma bata tsaya wata wata ba ta zabgawa maryama nata mari har biyu a kowani kunci "idan dadi né kema kiji ina dalili daga tazo ta tayaki aikin wahala sai mari jakar gidan ubanki ce ? taja hannunta zuwa kofar dakinsu tana share mata ruwan figar kajin data goga mata ."

Ummah tace "maryama me ya hadaku har daya kaiki ga marinta ? tayi shiru tana shayen zafin marin dan bazata iya fad'a mata bakaken maganganun data fad'a mata ba kawai ta rufe fuskarta saboda tuttukin bakinciki da zuciyarta Ke mata nan da nan kuka ya kwace mata umma ta qaraso kusa daita "kinsan kema uwarta bazata barki ba me yasa kikasa hannunki ajikin shukura ?sakina kanta ta tausaya mata tana son tayi mgn dan kare maryama da sheidawa ummah cewar ba laifin maryama bane laifin shukura né amman ta kasa ."

"kinsan halinta ya kamata ki dinga kiyayye duk abinda zai hadaku daita da yaranta ni wallahi nayi danasani ma sakasu cikin aikina kinga sakina tashi ki bisu kuje kema Islam jeki na gode kema hassana wuce  idan  bakin  sun  qaraso  kwazo  ku  gaisa " kukanta ya fiyye mata maganar ummah , bata cewa ummah komai ba tana tsaye akanta ita kuma tana cigaba da kukanta ta share mata hawaye "kiyi hakuri kinji Allah zai saka  miki  maryama bata ce mata komai ba ta cigaba da aiki datasata domin tana ganin hakan shine zai fiyye mata akan kukan da take ."

Karfe tara da minti arba'in  da daya daidai bakin suka shigo cikin unguwarsu cikin wata qatotuwa Jeep mutun uku ne a cikin matarshi da kuma shi kanshi alhj alqasim maude sai mai tuka su inda baba gali da yaya sadam suka fito tuni tsayuwar jiransu da sauri baba gali ya qarasa ya bude kofar da alhj alqasim maude yake da murmushi cike da kulawa suka gaisa sosai."
Chapter 66 · 0% Book details