← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 25 OF 100

Sashe 25

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"ai Kuma shine babban matsalar abokina domin yarinyar  itama ta kafe akan bata sonka amman nasan da zaka mata magana  da kanka zata iya amincewa kayi k'okarin  ka shawo kanta da kanka dan Allah ,ka kwantar da kai  ka shawo kanta  yarinya nan yar'uwarka ce jininka ce  sannan ita din mace  ce ,mace Kuma 'yar rarra..."
"ban son iskanci MB  ya katseshi a matukar  tsawace yana furzar da huci mai zafi daga bakinsa " sbd me zaka  fad'a min hk ?" how dare you talk to me like that   ? “

shiru mb yayi  yana mamakin yadda abokin  nashi  ke saurin  daukar   zafi  akan abinda bai kai ya kawo ba "to me ma ya fad'a da zai dauki zafi haka ?mr ATA ya mike zumbur  daga Kan kujerar da yake  zaune tare da tura  kujerar baya tamkar ita tayi masa laifi ya soke hannunsa daya cikin aljihun wondonsa "Ita din  makiyata ce ita din ba jini bace karka sake fad'a min cewar yaruwata ce ko jinina ce Ka dinga sanin irin maganar da zaka fad'a min taya da girmana da mutuncina zakace na tunkareta common mace daita yarinyar da umarni kawai zan  bata  kuma dan dolenta tabi ,ta Inda yake shiga bata nan yake fita ba  "

Shikenan kayi  hakuri abun ne yazo  hk amman  dai  ka  k'okarta ka....."dan Allah malam ka maida   hankalinka  jikinka sai  wani  qoqarin son saka min magana abaki kake wannan ai  mgnr banza  ce   "ka tsaya ka saueareni mana nifa hankalina  yana  jikina kai dai.... "dan Allah malam  kayi min shiru  babu wani saurararka da zanyi a yanzu  ".yana gama  fad'ar hk  yay disconnecting din   Kiran yana huci  ..."

    "Nonsense girl kawai ai bata Isa ba ,bata ma kai wannan matsayin ba shi da mata ke bi suna kuka suna rokonsa  ko gaisawa su dingayi bai kaskantar da kanshi ya amince  ba bare har ya ajiye girmansa matsayinsa komai nashi yace yana son mace macen ma irinta  ko cikakken minti biyar bai yi da katse kiran    ba kiran hjy zulaiheart ya  shigo  sai   da gabansa yayi wani irin mummu nar fad'uwa kusan yanzu duk sanda zai ga kiranta sai hankalinsa ya tashi saboda yasan Kiran baya wuce akan  wannan banzar yarinyar  bane ."

ilai  kuwa yana d'auka  da  maganar ta fara "Adamcy  kana  son ganin 'bacin raina  yayi saurin girgiza mata Kai kmr yana gabanta  "wallahi zan cire hannuna acikin lamarinka idan haka kake so "kiyi hakuri sweetheart inshallahu zanyi yadda kike so "kullum abinda kake fad'a kenan ka kasa aiwatarwa dan hk ka  shirya shigowa nigeria dan  cikin satin nan  maryam  zata dawo Kuma tana dawowa zaayi mgnr aurenku  da baba babba  har ta gama maganarta  bai sake  cewa qala ba ganin tayi shiru shima yayi shiru yaki cewa komai duk da yaso komai yaya ya bata hakuri  amman zafin da zuciyarsa keyi ta hanashi aiwatar da hakan har kusan minti goma tana jin yadda numfashinsa Ke sauka  da karfi kamar wanda yayi gudun tsare da kyar ya iya fezgo magana "sweetheart akwai abubuwan da nake son na kammala bazan samu damar dawowa nan kusa ba zaku iya yin  .."

  "No babu  wani uzuri  da zanyi maka kayi duk abinda zakayi ka gama ka shigo cikin satin nan shiru ya sake yi yana sauraronta  tana gama fad'ar haka ta katse  Kiran bayan wayar ta katse ya bita da kallo zuciyarsa na rawa ."ajiye wayar yayi  akan makeken table din dake office din ya buga wani uban tagumi wanda dagani na takaici ne."

   ya sake had'e fuskar nan  tashi  sosai wani irin bakinciki yake  ji acikin zuciyarsa, ji yayi kamar zuciyarsa  zata kama da wuta yana matukar  jin  bakinciki  abinda mahaifiyarsa  take  bukatar yayi ,shi da yake adduar komai ya watse a manta komai  amman ita kullum burinta  bai wuce taga faruwar wannan auren ba .

banda 'bacin rai mai Kona zuciya babu abinda yake ji mikewa yayi ya shiga zariya a office din  yana zagaya koina  yana zurfafa tunaninsa kafin ya soma magana shi kadai  "ya zanyi ?me zanyi ?taya zan soma  rayuwa da yarinyar  da kake qoqarin amincewa aurenta ? sosai kwakwaluwarsa ta shiga tunani neman mafuta  dan dole yasan abun yi kafin mahaifiyarsa tayi masa  wannan auren  mr ATA ranar  kwana yayi  yana tunani  ."

******
Bayan  kwana  biyu  maryam  ta dawo  daga  Abuja murna gurin  nana hauwa'u hjy zulaiheart  da sauran 'yammatan   gidan babu  magana  dan  sunyi  matukar  kewarta sosai  hira  ce  ta yaushe gamo ta barke a tsakaninsu sai yamma suka bar gidan haka ma washegari  suka cika gidan har da rukkaya makociyarsu anan grã gidansu yake asalinsu nufawa né suna cikin hira rukkaya ta Kalli  maryam sannan ta Kalli  diyana  da nuzla tace   "nafi  kowa  Jin dadin dawowar  marsi  bari na  baku labari    nayi wa marsi    saurayi  kyakkyawa   ajin   farko ."

     maryam   ta  kalleta   tana  kwa'be  fuska cike
da takaicin Jin  maganarta   yayinda  itama rukkaya
ta kalleta tana  sakar mata murmushin  jin dadi  .
Sai dai a matukar  wulakance  maryam ta
cigaba da  kallonta  kamar ta rufeta da dukan
mutuwa   sannan ta  fara  magana cikin fushi da 'bacin rai  "bangane  kinyi min  saurayi ba ance Miki  bani  da  saurayi ne  ko ya    ? ke da duk fuskarki ta dame da   bille  kota  Ina an watsa  miki shi ba'a ce anyi miki saurayi  ba  sai ni  da fuskata take  lafiya lau  babu zane ko daya    ,Kalli  bakinki duk a warwatse  kamar  lefen sakarya shine zakice  kinyi  min saurayi , karki qara min  irin  haka wallahi  banaso ai kinfini bukatar saurayi ."

Gabad'aya  suka kwashe da dariya rukayya kuwa tsayawa tayi tana kallon maryam da mamaki nana hauwa'u kam har da zubewa kasa  tare da rike ciki dan dry  ."Ina ganin dai  baki san    aljanu sun  shigi     marsi  ba ko ?  ai  babu damar  ayi mata  maganar maza sai hankalinta   ya tashi ." nifa  ba  haka bane  Ina da zabi  acikin  zuciyata  Ina da ra'ayin irin mijin da nake son aure ba kowani shasha ba  amman dai  na  barwa zuciya  irin mijin da nake so Ke mai bille sai ki rike saurayin dan kinfini bukata ."

rukayya  ta Kalli nuzla nuzla ta kalleta  sannan a matukar fusace rukayya tace  "karki qara cewa fuskata anyi  min bille "to karya ne ba'a yi miki ba ? "idan bakya so nace miki hk  nima ki barni da batun wani saurayi can   tun da bance miki  nayi ina son ba wadan da nake dasu ma sun Isheni bana neman qari sun  dade  a d'akin  suna hira  akarshe duk suka watse  suka kama gabansu."

******
Karfe   shabiyu   daidai jirgin   Mr ATA ya sauka  a lagos  a haraban  gidansu tun   kafin   jirgin ya k'arasa sauka  security's  dinsa  ke zagaye da gurin har sanda ya sauka , a hankali   ya  mike yana  gyara zaman rigarsa Sannan   ya fara  takowa  daga matattakalar bene yana taku da  kyar cikin  tafiyarsa nan nashi na Koda yaushe wato tafiya cike da alfarma da izza  yana d'aga  kafafunsa yana shakar iska  da kyar  tare  da hura hanci  escort  dinsa already sun fito suna  nan tsaye  suna  jiransa duk Inda ka duba acikin haraban  gida masu aiki ne ke Kai kawo suna aiwatar da aikinsu."

yana qarasa saukowa escort dinsa da security's  sukayi masa caaaa har zuwa Inda yake tsaye Inda ya fara taku suna biye dashi har zuwa bakin kofar  shiga cikin   parlour'n mahaifiyarsa  na d'aya ,  yana isowa gurin yaja ya tsaya  d'aya daga cikinsu mai suna muzammil  ya  bud'e masa kofar  ya shiga yabi bayansa shi kad'ai rike da bakar jaka  ATA   bai tsaya akoina ba  sai  a babban falon  mahaifiyarsa   ya  shiga ya zauna ya kame akan  d'aya  daga cikin kujerun falon  ya d'aura hannunsa d'aya  akan gwiwarsa  yana d'an  jijigawa yaronsa  muzammil  ya rankwafo  ya ajiye  masa  jakarsa  ya  bashi  izinin tafiya ya  juya da sauri  ..." 

A hankali  mami  tayi sallama cikin  had'ad'd'en falon a zaune ta samesa akan kujera ya lumshe lumtsatsun idanuwanshi ,da kyar  ya bude baki ya amsa sallamarta  batare daya bud'e idanunshi ko matsowa ba har sanda ta zauna akan kujerar dake kallonsa tana jin sanyi da farinciki mara misaltuwa  da ganin kamilallen  danta mai nagarta da haiba illarsa dai rashin ajiye  iyali da miskilanci da zafin rai duk wannan farinciki daga ciki take jinsa dan bata bayyana shi ba .

a hankali ya bud'e lumtsatsun idanunshi ya mike ya k'araso gabanta ya rusuna  har  kasa  "mun sameku lafiya  sweetheart? Wani sanyin dadi Ya ratsata  ta kai hannunta kanshi "alhamdulillah ka sauka  lafiya   ya aiki Ya  fama da jama'a ? ta fad'a fuskarta  babu yabo babu fallasa "alhamdulillah sweetheart  yayi magana yana matukar tausayin Kansa dan yasan tunda ya zo ya  dinga cin karo da matsaloli kenan dole sai yayi hakuri dan magana daya ce za'a yita ana mai maitawa ,."

A natse  ya mike ya koma mazauninsa ya zauna 
yana neman layin M.B  da sauran friend's dinsa   kafin kace me hjy zulaiheart tasa an  cika masa gabansa da kayan itatuwa dabam dabam sai dai babu wanda ya d'auka yaci illa amsa waya da yake ta bangare damba dabam , nana hauwa'u ta shigo ta gaishesa cike da ladabi  "yayanmu Ina yini ka dawo lafiya .?"
"Lafiya auta  ykk ya fad'a  atakaice"  lfiya ta bashi amsa da haka sannan  ta  mike ta koma ciki dan yadda fuskarsa take a  murtuke  nan   komai  zai iya faruwa , haka  rashida   da muna   yaran baba qarami   sun shigo  gaishesa a mutunce ,  babu yabo  babu  fallasa ya amsa  haka akayita shigowa yi masa sannu da zuwa sai dai ya amsa atakaice ba tare daya bi ta kansu ba maryam ce kawai bata shigo kawo gaisuwa ba har  sanda MB ya k'araso sai daya yi sallama a bakin kofar falon aka bashi izini  shigowa sannan  ya shiga .
Chapter 25 · 0% Book details