← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 57 OF 100

Sashe 57

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

lokacin da zaa kawo  bilkisu gidan mahaifinku babu wanda ya rakota saboda ta auri talaka daga ita sai mahaifinku suka  baro gidansu zuwa rubabben dakinsa  inji cewar hjy rahma dan wulakancin da sukai mana yasa babu wanda je dauko amarya .
babu abinda iyayenta sukai mata na kayan dakin kuma har yau yan'uwanta na jini babu wanda yasan inda  take sun dai san tana zaune acikin lagos din nan amman a ina take basu sani ba babu wanda ya ta'ba zuwa ."

Kusan bakin hjy rahma yayi tasiri akan bilkisu dan sai datayi shekara uku tare da ussein batare da tasamu ciki ba har aka auro salma bata samu ciki ba ussein bai bawa mara d'a kunya ba dan sosai ya dawo da shaye shayensa lokacin data masa mgn akan alkwarin da yayi mata na dainawa yace" yaushe sukayi haka ?sai byn da salma ta haifi ali sannan kwatsam sai ga ciki bilkisu ta samu har lokacin da tayi haihuwar fari tace  abarta  a gidan mijinta 
ni  nasan da wani mai arziki ta  aura ko bata je ba dole zaazo a dauketa  ,babu wanda yazo dan lokacin mahaifinku da kanshi yaje ya sheida masu ta haihu intakaice miki korar kare aka masa wai yazo rokon kudi shiyasa duk lokacin da mahaifinku ya bata mata  rai sai dai ni naji   mata haushi ita kuma  tayi kuka ta hakura dan bata san inda zata dosa ba mutane gidan nan gbdy sun daukenta  sha sha wai  ta tare a gindin miji to idan tace ma ta gaji ina zata ?

yau da'ace tayi saar uwa da tun tuni ta koma gareta domin tana  neman taimakonta amman no way domin zamanta a gidan ussein  shine gatanta kinga ta rasa gatanta shiyasa a kullum take ganin bata  da gatan daya wuce ussein daku yayanta komai yayi mata  take hakuri wanda kusan hakan yake cikin dalilin da yasa salma da hassana suke cin kashi akanta ta sha wahala sosai acikin yanuwan ussein bayan an haifi habib rashin Lfy ya kama  hjy haka ta dauko hannun bilkisu tasa a tafin hannuna tace na rike mata amanar bilkisu kar na bari tayi kuka idan ussein yasata kuka na tabbatar na wanke mata zuciya sannan ta qara da cewa byn ta mutu bilkisu ta dawo bangarenta ta cigaba da rayuwa acikisa  nace ta tara yayanta ta fad'a agabansu hakan kuwa akayi abun bai masu dadi ba amman haka suka yi hakuri kwana uku tsakani  tace ga garinku ."

Bilkisu tayi kuka kamar zata bita domin a gasky ita akayiwa mutuwa dan kusan nauyinta akan hjy yake itace komai nata bare Ke da kika ci sunan mahaifiyarta komai tasamu kece da bilkisu ne shekarar hajiya daya da rasuwa rashin lafiya ya kama mahaifinki  koda aka dubashi ciwon sigari ne ya kamashi har yayi masa illa bilkisu bata gujesa ba itace komai nashi  ,ita Ke kaisa asibiti gwanati ga ciwonsa na bukatar kudi amman babu ke babu irin wahalar da batayi ba har wankau tayi dan  ta rufawa kanta asiri cikin wannan halin rashin lafiya aka samu cikin habib har aka haifesa mahaifinku bashi da lafiya ranar da habib ya cika shekara daya a duniya  Allah ya dauki ran mahaifinku  ,yanzu shekaru ashirin da uku kenan rabonta da yan'uwanta da iyayenta kuma har zuwa wannan lokacin babu mutun daya daya nemi  inda take  to me  zai sa ku ku damu da   inda suke ?

Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan  09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

        Page 19

A  matukar  zuciye  ya  sauke duka hannuwansa   yana  huci  sai dai har  lokacin  kwayar  idanunshi na kan  fuskar   baban   gali   yana masa  wani  irin  mugun  kallo  mai tattare  da  bakinciki  lokaci  d'aya kuma  yana  ta  qoqarin  danne  fushinsa  dan  baya  son  'bacin  ran  mahaifiyarsa  ."

baba   gali  ya  sakar   masa  murmushin  mugunta  sannan  ya kalli   aunty  hassana  da  aunty  salma  "kuga  wannan  tantirin  mara   mutuncin  yaron    wai  ni   zai  kai  hannunsa   jikinata  saboda   nace  zasu   bar  gidan  nan  kamar  da   kudin  ubansa  ko  da  kudin  uwarsa   aka  gina  gidan  nan  da zai  wani   d'aga  hankalinsa dan  Allah   ku kalli   Irin  kallon  da  yake  min  nasan  yana   jin  kamar  ya  kasheni  ne ."ya  qarasa  maganar  yana  dariya ,"

Murmushin  jin  dadi  aunty  hassana  tayi  itama  "ai  kuwa  bai  isa  ya  kasheka  ba  sai   dai  ya   kashe  uwarsa  ko  yaje  ya  kashe   wad'an  can  marasa  mutuncin  dangin  uwarsa  ba  amman  mu  nan  munfi  karfin  d'an  kutumar  uba,  shegen  gora  mai  falla  fallan  kunnawa , an  nace  mana  an  zo  an  haifa   mana   irin  jaraba  kuma  wallahi  sai  Kun  bar  gidan  nan  matsawar  bazaku   daina   mana   rashin  mutunci  ba  ."

cike  da   raunin   zuciya  habib  yace  "mahaukatan   banza   kawai  da  basu  san   ciwon  kansu  ba "
"mu   kake   cewa  mahaukata ?eh !lallai   yaron   nan  wuyanka  ya  isa yanka  ,amman  ka  sani  bamu ne mahaukata  ba  ga  mahaukaciya  nan a  gabanka  kana   kallo wannan  wannan  itace  mental  itace  mahaukaciya da ka  kiramu  dashi  aunty   hassana  ta  fad'a  tana  nuna  gefen  kanta ."

"Hassana !" ya  kira sunanta  a matukar  hassale
Aunty   hassana   tayi  saurin  zaro  idanuwanta  waje  tana  duban d'anuwanta   cike  da  mamakin  habib "yes  abinda  kunnuwanki  suka  ji  na  fad'a  kenan   dan haka ki  ma  daina  mamaki  zan ma iya fad'ar  abinda  yafi  haka " mutun takin  me  zan  tsaya  yi tunda  kin  kasa  mutunta  kanki ?"

ta  maida  hankalinta  da  idanunta  kanshi   sosai  tana  nazarin mgrsa sa  sai  daya   samawar  jikinsa   natsuwa sannan  ya  cigaba  da  zaro  magana  "Ki  kalli   aunty  tsab  ki  gani   Kinsan  dasu wa maganata  ta  dace ,ku  din  dai  kune  mahaukata  kuma  bazan  ta'ba   sauya  maganata ba."

  Hawaye  ne  yake  zubowa  daga  idanun   aunty   gashi  magana take  son  yi  dan  ta  basu  hakuri  sannan  ta  tsawatarwa  habib amman  ta  qasa  bud'e  bakinta  bare  ta  sarrafa  harshenta a wannan  lokacin  ita  kanta  taga ya dace  ta  koma  cikin  'yanuwa  cikin  asalin ta  amman kuma idan ta tuna  irin  rayuwar  datayi  har ta kawo  wannan  matsayin  sai  taga komawar   nata  bashi  da  wata  amfani  me  zata  cewa  alhj rafi'u  giwa  da mahaifiyarta  wacce  tafi  kowa  d'aukar  zafi  akan  kowa  wacce  ta  gindaya  mata sharadin  cewar  ta  manta daita ta manta da  kowa  nata  tunda ta zabi auren  ussein  ?".

  "gidan  nan  kowa  yasan  gidan  kakanmu  ne  wanda  ya  haifi mahaifinmu   yadda  kuke  taqamar  kuna  da  iko  akan   gidan  nan  haka  muma  ya'yan  ussein  muke da  iko  da   gidan  nan  matsawar  zamu  zauna  acikin   gidan   nan  dan  dole   mahaifiyarmu  ta zauna acikinsa   ."

" Ke  ! hassana   da  kike  cewa a dole  mu  bar  gidan  nan  kisani  bamu ya  kamata  mu  bar  gidan nan  ba  ke  da  ya'yanki  yafi  dace wa  ku  bar  gidan nan  dan   da   gidan  miji  mace  take  taqama  ba da  gidan  uba ba  , aunty  a gidan  mijinta  take   zaune  Ke  fa  ? da  har  yanzu  Ke da  ya'yanki  baku  san  garin   ubansu  ba  bare  su  san  dangin  ubansu  ,ki  fara zuwa ki  kai  ya'yanki  su  san dangin  ubansu  tukun  kizo  ki  kori  wad'an  da  su  muhalinsu  suke  ."

Cike  da  sanyin   jiki  maryama  ta  dinga  jan gwiwowinta  har  ta qarasa  gabansu  aunty  hassana jikinta  na  wani  irin  rawa   Kafin  tai  kai  ga yin mgn  taji  aunty  hassana  ta hau surfa  mata maseefa  "dan  ubanki  yau  dai  karki  kuskura ki bamu hakuri , shegiya  yarinyar  munafukar Allah taala kin wani  marairaice  fuska  kamar  ta  kirki  zaki bawa mutane  hakurin  gulma  wallahi   yau   shine  zamanku  na  karshe  acikin  gidan nan   sai  kun bar  mana  gidanmu  ,gara  ma  tunda  wuri   Ki  san yadda  zaki  d'auke wnn  uwar  taki  da wannan shegen  kannin naki mai falla  fallan kunnuwa Kmr na fir'una ku  bar  mana  gidanmu  mu  huta da jaraba  sanda  ussein  yana  raye  bai  barmu  mun huta ba sannan  bai  tsinana mana  komai  ba  sai  ruwan shaye shaye da d'auko  mana  magana  wanda sanadiyyar  haka  ya  kwaso  mana  wannan munafukar  uwar  taku  gashi  ya  mutu  ya  barmu da  mugun  iri ."

   "Kuka  maryama  ta  fashe  dashi  hade da  sake durkusawa a wajen  batare da tasan abinda zata fada ba,  tana  mai   bakincikin  irin   kalar   rayuwar  da  mahaifinta  yayi a  sanda yake  raye, gashi ya  bar duniyar  amma  basu  huta  ba , wannan wace  irin rayuwa  ce ? me yasa wasu yanuwa suke yin haka ? "tasani da ubansu mai  arziki  ne da  duk abinda yayi babu mai tuna masu  bare  har a zagesu   dashi  ."

tsaki   baba   gali  yaja  yana cewa  " Munafukar  banxa  sai  anyi  magana  kisa  mutane a gaba kina kuka,  da  ubannaku  bai shaye shaye  ba  zaa fada? daya  zauna da mutane lpy  zaa ki  fada ?kullum yana cikin d'auko  mana  magana  gashi ya mutu ya bar iri  an  iya  tujara iya tujara  sauran  shaye shaye .."

"Allah  bazai sa  ba  ,baba  ka daina masa mugun fata "me ya saura yaro ya zama dan daba ai sauran shaye shaye, habib zai yi  magana   maryama  tayi saurin dakatar  dashi  tana cewa "walalhi karka sake cewa komai ai ga  irin abinda ka haifar ko ?"ni dai na fada maku  maza ku san ynd zaku  yi  ku bar mana  gidanmu tunda  gdn bana ubanku bane,"

  maryama da  tarin  qunar  zuciya  da qunar  rai take zubar da hawaye  tafi  karfin minti  goma a durkushe  sai daga baya ta koma  inda  tabar aunty ta durkusa  kusa daita  hawaye na  zuba a idanunta Itama aunty  hawayene take zubarwa a  nata  idanun  tana  jin ciwon abinda  habib  yake  duk da tasan  gsky  yake  fad'a  masu  amman  bata só  yana  fadar duk  abinda yazo   bakinsu  dan  kome  zai faru bazasu  ta'ba  sonta ba  har   yau   tarasa  me  tayi   masu  mai  zafi  a duniya  da  suka  kasa  yafe  mata  sannan suka  kasa   danne  tsanarsu akanta  da  yaranta ."
Chapter 57 · 0% Book details