← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 63 OF 100

Sashe 63

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

acikin  duhu ta sheida murmushinsa  ganin hasken hakoransa ta dan saki ranta da kawar da damuwar fuskarta  barkanki  da fitowa  gimbiya  maryama "numfashi  ta fesar "kai  ya kamata a yiwa barka da zuwa da  kuma sannu da  qoqarin  zuwan  da kayita yi  baka  samun ganina da km qoqarin da kayi   da iyayena last week  na  gode sosai  " ya dan kyaleta "iyayenmu dai na gyara miki ."  maganarsa ta dan mata dadi wannan yasa ta dan sakin fuskarta kad'an "ya kamata mu samu waje mu zauna ko can ne ya dan nuna mata wani dakali dake makoftansu ."

tare  suka  qarasa  amman  shi  yaki  zama ya tsura mata ido ya kamata ace kece kika fara zama sannan ni tayi shiru dan tuni ta gane manufarsa ta dan kallesa da idanunta cikin sauri ta kawar da kai ganin kwayar idanunshi na kanta to shikenan na zauna kema ki zauna ta zauna tana gyara zaman hijab dinta sukai shiru na dan tsawon lokaci daga  bisani ya dago ya dubeta "Maryama zuciyata duk ta gama tattara komai agareki a yanzu bani da wani shakka ko kwankwanto akanki muradina ne na samu damar da zan kawo kaina ga iyayenki domin a samu tsayayyen magana a tsakaninmu ."

     Soyayyarki ta jima ajikina maryama nayi dawainiya da soyayyarki tun kafin ki kai wannan lokacin na koyar da zuciyata dabarun da kuma yadda na dauki hakuri dan kawai na samu soyayyarki ban ta'ba gazawa ba , ina sonki maryama da zuciya daya ban qara jin ina sonki ba sai danaji halin da ke da mahaifiyarki da kaninki kuke ciki a gidanku bazan boye miki ba ina jin tausayinku most especially mahaifiyarki domin ta fuskanci abubuwa dayawa akan rayuwa kuma tayi hakuri na tausayawa rayuwar da kuke  ciki ki daure ki samar dani acikin zuciyarki mu daga darajan uwa da kuma danuwa mu tallafi rayuwarta data kanin mu  dukkan wani muradinki zan bi na tabbatar kina da burin kiyi aiki byn kin qare  bautar qasa kamar yadda naji kawayenki suna fad'a,burinki kiyi karatu mai zurfi Kiyi aiki ni nan zan barki Kiyi komai kike só zan barki ya dan saurara yana kallonta hawaye taji akan kuncinta  tasan  su da mahaifiyarsu abun tausayi né suna cikin tsananin kunci da bazai yuwu a boyesa ba ."

ahankali  ta dubesa "naji dadin  yadda kace zaka tayani  kula da mahaifiyata da kuma danuwana mlm yahuza ina matukar son Mahaifiyata ina son na gatatan rayuwarta domin ita kadace dani na yarda da soyayyarka kuma na amince duk lokacin da kake da lokaci kofar neman aurena a bude take domin burin mahaifiyata kenan  na tsayar da mijin aure fatana ka rikeni amana tayi shiru saboda kunyarta ta motsa ya sauke ajiyar zuciya a zahiri take fahimtar farincikinsa dan bai boye ba ."

Yayi  murmushi  yana  shafa  fuskarshi "maryama amanarki  agareni  bake  zaki bani amanarki daga allah  daya  halicceni ce  domin  shi na dinga roko ya bani ke  amatsayin  mata aurena  allah ya amsa tunda  har kin amince min dan  haka shi ya bani  wannan amanar dan haka nayi alkawarin bazaki taba  ganin  sabanin  haka daga gareni ba ,ba kuma zakiyi  danasani ba , aurena zai zame miki abun alfahari  bazan  ta'ba gudunki  ba bazan ta'ba juya miki baya  ba ."Soyayyar sati uku  da  sukai da  mlm yahuza ta fuskanci  tsantsar  son da yake mata kulawa kuwa  har  da mahaifiyarta abun mamaki kowa a unguwarsu  yasan  da soyayyarsu wasu  nasa albarka wasu  nacewa  ba girin girin  ba  allah  yasa a d'aure  kar ya  gudu ya barta kamar sauran."

******

Cikin   wannan  lokacin  maryama da   kawarta  subai'a  suka  je adamawa  domin   suyi   cam for three  weeks  bayan  sunyi  sati uku  a adamawa  alokacin  mlm yahuza   yayiwa    wani  mutun magana  akayi   masu  change  of  location  ita  da kawarta   daga  adamawa   aka  dawo  dasu lagos inda  zasu  fara  bautar  qasa a   Z &A    comapany   dake  kan  titin  guness  bayan  ciku cikun  da  mlm  yahuza  yayi  masu domin  shine  ya  shiga  ya  fita  ya  kar'bo  masu   letter   suka  kai wa  nysc  aka kar'besu  a kamfanin  bayan sun dawo  lagos  suka  fara savieces  dinsu  wannan taimako da mlm yahuza yayiwa maryama  ya  wanke   zuciyar  habib  yaji ya shiga ransa har ma ya fara kiransa da  otherhaif kuma yake  girmamasa yana mai jin ba qaramin dace yaruwarsa tayi ba domin kuwa samun maza irinsa suna  da matukar wahalar samu ."

"gashi shi dai ba wani zurfi yayi  a boko ba dan karatunsa  iya  diploma  ne  amman  yana  da  hanya kuma yasan  mutane  sosai dan shugaban RRS  mai ci alokacin abokinsa ne tare sukayi karatun tun daga primary har zuwa secondary inda anan suka rabu amman har gobe suna mutunci  da abota , fara  bautar qasa yayiwa maryama dadi dan daman  zaman gidan ya isheta dan tun da suka qare karatu babu inda take zuwa bayan  islamiyya  gashi ita daman fita bai dameta ba saboda ita ba maabociya son yawo bace amman wahalar da take sha da yawon sata aiki da mutanen gidansu keyi yasa tayi maraba da da wannan fitar tata kullum fatan allah ya taimaketa tana qare bautar qasa ta samu aiki ."

Ranar  wata  asabar  tana  zaune  shiru a side dinsu  tana tunane  tunane  akan  sakina  tana matukar  qaunar sakina  aranta ta kasa jurewa   abubuwan da take mata batare da tasan laifinta  ba ,zuciyarta ta bata  shawarar taje ta tmbyeta  ko  wani laifi tayi  mata wanda yasa ta canza mata ,nan  take  ta amince da  shawarar  zuciyarta , dan hk ta mike tsam ta fito ta nufi side dinsu ta yi sallama a tsakar gida babu wanda ya amsa  mata  dan  haka  ta wuce daki  inda tafi  tunanin sakina take  mintuna sha uku da zamanta  amman  sakina  bata ko kalleta ba ."

Ahankali  maryama ta  tunkarareta  da abinda ya shiga  a tsakaninsu "haba "yar uwata  mai na yi miki ki ke fushi  dani  tsawon Lokaci  ko  magana ba kya min  mai  nayi miki  da hukuncina ya cancanci haka.?""Cewa na yi kin min wani abu?sakina  ta tambayeta tana  mai  kallo  cikin   idanuwanta  maryama ta sauke nata  idanun  ganin irin  kallon da Sakina ke mata. Ta ce"tô  Sakina tsawon  lokaci   naga  bakya min  magana, in da nayi miki laifi  ne sai ki sanar dani na nemi yafiyarki bana jin dadin yadda kike nuna ko in kula gareni  tsaki kawai sakina  taja ta fice tana magana cikin ranta wanda sam maryama  bata ji  dadin abinda tai  mata ba  "na shiga uku maryama   ta fada a ranta me  zai sa sakina ta yi min  haka  kawata kanwata kuma yaruwarta masoyiyarta?ya Allah  ka  sanyaya  zuciyar  sakina  akaina  idanunta   cike da hawaye ta baro  side dinsu ."

Ranar  wata  laraba  aunty  salma da yaranta biyu suna zaune a tsakar  gida  aunty  salma ta dubi sakina "wai  Ke  kwana  biyu  nan mai yake damunki ne  sai  ki dinga kadaita  kanki  kina wani shiru idan wani  abu   aka miki  bazaki fad'a ba  sakina tace" ko na gaya miki ba iya magance  min zakiyi ba duk da ku  ka jawo halin da muke ciki nida  yaruwata shukura ,maryama dake kokarin shigowa cikin side din nasu  ta  dan. tsaya  ta kasa kunne aranta tace "allah  sarki ashe  yaruwata  laifi akayi mata tayiwa gidan kudin  goro  kowa bata shiri  dashi."

aunty  salma tace " koma  me akayi  muku   zurfin cikinku ne ya janyo muku Ke kanki kinsani duk damuwarku  kema  kinsan zanyi qoqarin magance  muku   ita matukar  ina numfashi  acikin duniyar nan  sanar  dani  menene  aka muku  da har  yake saka ki  cikin kunci "kusan rabin yan makarantar islamiyyarmu  sun  san  yadda shukura ke son mlm yahuza  amman  kiri kiri  kuna kallo wannan banzar ta  juya abun ya koma  kanta gashi har ana batun saka  rana  aure ."

Da alamun  aunty  salma  taji dadin furucin sakina akan maryama  domin  duk irin kunci  da halin koin kula da suke ciki da sakina bata gani ba bare ta shiga cikin maganar  tayi musu sulhu "aunty salma tace" to meye  keda yaruwarki  ? maryama ta fahimci kalmar  cikin  zolaya tayi  maganar ,ai kuwa nan da nan sakina  da shukura suka bata rai cikin nuna tsantsar  tsana "wannan banzar ce yaruwarmu daace kun  koresu a gidan Kmr  yadda kika ce ai da bata yiwa  shukura  kwacen  saurayi  ba  yanzu  gashi nan muna  ji mun gani  wanda shukura take so  dole zata hakura "a'a waya  gaya maku ai  babu wani  maganar wani  hakuri  ,kuyi  hakuri tunda kun fad'a min ku bani  kwana uku zaku ga abinda zai faru."

hankalin maryama  ya tashi  kwarai da gaske har yasa  daga  nan bata  sake  sanin abinda suka cigaba da tautaunawa ba  saboda wani daci da  zuciyarta ta dauka ."jiki a matukar ta sanyaye ta dawo side dinsu "ita bata san shukura tana son mlm yahuza ba da sam  bazata  amince da soyayyarsa ba sai ma ta hadasu  amman yanzu ya zatayi ?ko da  yake ta fahimci wani sabon salon cin zarafi ne ake son bullo mata  mata  dashi  dan arabasu dan  haka zata bari adduarta tayi karfin  da bazasu samu nasara akanta ba  tun daga ranar bata sake runtsa idanuwanta ba wajen kiyamul laili  domin  kiyamullaili  tana  qarawa nauyin mizanin  bawa, tana qarawa mutun hasken  fuska  da  samun kwarjini da d'ga darajan mutun acikin mutane kariya ga dukkan sharri  tare da biyawa bawa bukata."

Duk  bayan  kwana  biyu  mlm  yahuza  yana  zuwa wajenta  Kmr yadda ta tsara  masu dan bata  son  yawon  zance ,tun bayan kwana biyu  sunyi da mlm yahuza zai  zo sai dai har  karfe  takwas na dare daya saba  zuwa   bai zo  ba amman ta rasa dalili hakan ta kasa  hakuri  ta  shirya  tsaf ta fito zuwa bangaren Ummah  ta iske  shukura  tana  zance  sai  dan kasancewar  dare  bata lura da wa take zance ba sai dai  kawai  kamshin  turarensa  yayi  mata kama dana  mlm yahuza amman  ko  kadan  bata kawo shi bane ta shiga bangaren umma tana zaune suka gaisa
Daga  nan  suka shiga hirar duniya har sanda shadaya ta buga ta mike tayi mata sallam ta  koma side dinsu  cikin  tsinkewar zuciya dan bgabanta banda luguden bugawa babu abinda yake ."
Chapter 63 · 0% Book details