Sashe 9
Kwankwason Jimina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dariya ta saki tana tabe haba Hadi da tada hannuwa tana shewa tace,
"Lalle Auwalu wallahi ni dariya ma kake bani wai daki . Wancen akurkin ne daki? Wancen Dan ficicin wajen kamar bandakin kaji zaka ce mun daki? Koda yake banga laifin ka ba duk wata Yana sanmaka sadaka fisabilillahi ai shysa idanuwanka sika rufe baka ganin lefin su. Batin na mayar musu da mukullin na kwashe kiwon na Kuma ba zan ba. Nace bazan kwashe din ba. Raba Arne da makami ibada ne. Don sun dau wancen shirme wajen cikin tarin dukiyar su ta Ina Allah zai rage su? "
Bappah auwalu yayi kwata Yana cije kasan labban sa yace,
"Wadatar zuciyaa ce kawai da junaidu da iyalin sa alhamdulillah. Domin kowa sheda ne junaidu ya sayar da sauran kadarorin sa da sukai ragowa ya fara harkar kasuwancin Nan da ita ya sanwa Mai dakin sa take awara suka taru suke rufawa junan su asiri. Nan danacee maki ga dubu uku ki fara sanaa kema ai kikayi don haka karki sake kawo mun sukar Yan uwan kinji na gaya Miki" Yana gama magana ya saka Kai ya shige kitchen tabi bayansa tana sakee fashewa da dariya tana harara tana mita,
"Dubu uku... Allah ya kwashewa dubu ukun Nan albarka. Wallahi Auwalu nafi karfin dubu. Wacce sanaar Zan fara da dubu. Har da wani mun gori wai kar na karar kawo sukar Yan uwan ka. Yo ai ba sai kamin gori ba. Abunda naka gajiya da fada kullum nasan junaidu da Hindu Yan uwanka ne na jini dukkan su. Mtscew aikin kawai"
Ta shige daki ta tana bugo kofar garam. Bappah auwalu ya tabe kansa kawai yana juye awarar ababban tray...
::::::::
Wata hadaddiyar luntsumemwniyar mota ce ta faka a daidai kofar gidan... Sliding mirror din bayanta tayi na owners corner tana hangar dandazon layin awarar..
"Hajiya kinga layin ko! Yasin Kuma duk Wanda na roka abani basa yadda Yan taurin Kai ne Mutanen dake layin"
Agogonta ta sake kalla lokaci na gogawa. Cikin ta sai kugin yunwa yake gashi awarar kawai take son ci.
Batace masa komai ba ta bude kofar motar ta futa...Kallo daya zakai mata kasan wannan daga jinsin masu farcinan Susa tafito. Dubata kayan dake jikinta kadai ma abun kallo ne tabbas kudi yayi kuka awajenta.
Agogon dake daure awutsiyar hannunta Rolex ne latest design na shekarar. Jakar hannunta samfurin hems. Fara ce sosai tamkar baturiya, fatar ta sai sheki take duk kuwa da katon sunglasses din prada designer dake sakale a idanunta...Kai tsaye ta shige cikin gidan tamkar ta San masu gidan.......
[2/21, 6:52 AM] Hafsaat🧕: *_KWANKWASON JIMINA!!_*
_(MAI WUYAR SHAFAWA)_
🦩🦯🦾
_✍️: MX_
*_ZAFAFA BIYAR 2024_*
_vip pages na arewa👇_
*_arewabooks:mssxoxo_*
*_paid page :11_*
______
::::::::::::::::
***Bakinta dauke da sallama a gayance ta shiga cikin gidan har yar rumfar da Malama Hindu da yaran nata ke zauna suna ta tuyar awara har kasake biyu manya. Ga layi mashaa Allah anata shige da fice na sayan daddadar awarar...
Saboda awarar na da matukar dadi ga laushi mai tattare da kwai daya lullubeta. Tasha kayan hadi. Ga tumatir da albasa cucumber a yanke a gefe da Kuma yajin tafarnuwa sai kamshin kayan kamshi yake yi...
Babban al-muhim Kuma awarar akwai tsafta. Komai a tsaftace idan kaje saya. Harta abun daukar awarar aware yake a gefe da ledar hannu ta dauka itama. Don haka Yan hayu masu kudin birnin Kai har ma da talakawan ma siya sukeyi... Ga faraa da karanci da malama Hindu da yaranta ke nunawa masu sayar awarar ta su....
Wannan yasa da karfin addua da istigfari da shimfidar fuska da Kuma kyautatawa irinta Hindu da ahalin ta yasa baki daya mutane ke kaunar awararta. Don kullum sai ta kare idan anzo saya babu duk yawanta....
Ta lumshe idanun ta ta bude a lokacin data karasa inda suke suyar awarar. Malama Hindu ta daga Kai da sauri duk suka juya suna kallonta hadi da amsa sallamar da tayi Kafin daya bayan daya su shiga gayshe ta.
Ta amsa fuskar ta a sake. Malama Hindu ta mike da sauri tana cewa
"Hajiya shigo ciki"
Murmushi tayi cike da mamakin bata taba zuwa ba, Amman tamkar sun Santa har da cewa ta shiga cikin gidan?
Bakinta dauke da sallama ta shiga parlorn malama Hindu ta amsa tana daga tsaye .
"Ga wuri ki zauna, mu Kara gaisawa . Barka da yammaci? Iyalin kalau?"
"Alhamdulillah." Ta amsa ta tana duba parlorn dan karami madedeci, Amman a killace ko'ina tsaf tsaf a gyare sai kamshin turaren wuta ne ke tashi...
Lalle suna da tsafta . Ganin ba wani baki dake ciki ko masaaniyar zuwan ta balle tace shiryawa sukai .
"Ma shaa Allah" malam Hindu ta fada...
"Kinsan gidan Dr. Abubakhr dollars?"
Malama Hindu ta girgiza kai da sauri tana mai him ta da kallon Karin bayani,
"bansan shi ba gaskia"
"Hakane kam ba lalle ki San shi ba. Dubada bangaren ku daban namu damu. To shi Dr. Abubakhr din miji na ne. Ni Kuma sunana hajiya qibdiyya. Kusan kullum ai Ina aiko a saya mun awara a wajen ki"
"Allah sarki. Nagode Allah ya saka da alkhairi. Da ke mutanen da yawa bazan waye wanene ke zuwa ba"
"Hakane kam..." Hajiya qibdiyya ta fada tana murmushi hadi da duban agogon da ke daure a wutsiyar hannun ta tace,
"Yanzun ma shine mun fito tare da shi tun dazu yacemun layi yayi yawa Dakyar idan zaa samu.."
Malama qibdiyyah ta kada Kai Kafin tace,
"Eh wallahi.. masha Allah Nan da Nan da anyi take karewa. An goggode muku baki daya masu saya Allah ya saka muku da mafificin alkhairin sa. Aameen"
"Aameen"..
"Shysa na fito da Kai na .. naji zan iya samun awarar ko kuwa. Wallahi wannan ne shi ya saka " ta yi shiru bata karasa ba.
Malama Hindu na nazarce da ita daman tun shigar ta gidan dazu a farko ta hango cikin da ke jikin ta. tayi murmushi tace,.
"Allah ya raba lafiya hajiya. Ba matsala wallahi. Zaki ci anan ko a zuba Miki a pack ki tafi da ita?"
"Aah mashaa Allah, Nagode kwarai. Gashi" ta Mika mata Yan dari biyar guda biyu.
"Ta dubu biyu kenan? Har zaki cinye ta dubu biyu?
"Karki damu. Zubamin a plate kawai na ci anan. Kamar guda takwas ta Isa"
"To bari a kawo. Amman dan Allah ki rike kudin nan wallahi zan baki kyauta. Uwa uba Kuma kudin sunyi yawa "
"Ahh yar uwa banason musu "
"To shikenan nagode Allah ya saka da alkhairi Amin"
Malama Hindu ta nufi wajen babbar food flask da suke saka awara ta dakko plate ta zuba awarar fal da kayan hadi da yaji aciki..
"Gashi ranki ya dade... Bari a kawo ruwa"..
"Kakk takura kanku bari na ce driver din waje ya kawo"
"Aa dan Allah . Ki bari nima na sami lada tukun"
Hajiya qibdiyya tayi murmushi kawai hadi da kada Kai tace,..
"To shikenan tunda haka kikace. Nagode kwarai "
Malama Hindu ta sake fita tana Kiran Nawraah. Nawraah dake zubawa wani coleslaw acikin kwanon abinci ta mike da sauri,
"Naam ummy"
"Ungo rike. Ki sayo lemo daya karami da ruwa babba shima daya. Kiyi sauri banda wasa akan hanyar"
"Tohm ummy" ta fada da sauri harda hadawa da gudu. Malama qibdiyya ta koma wajen su Ashfeef dake tuyar auren Ashfeef ya hanata ta hanyar rcewa,
"Ummy kin har bakuwa ita kadai fa. Ki koma zamu karasa Allah"
"Hamma kaji abunda yace ko"
Ashir yayi murmushi Yana sosa keyar sa yace,
"Kije ummy ku cigaba da hirar ku aii sauran kasko daya daya mu karasa"
"Tohm sannun ku da kokari. "
"Yauwa ummy"
Komawa parlorn tayi wajen hajiya qibdiyya. Hajiya qibdiyya dai sai zura lomar awara take. Tamkar zaa kwace mata saboda yadda ta gigice tana wani lumshe idanun
Hajiya qibdiyya ta saci kallon malama Hindu. Jikinta a tsaftace ba akanta irin masu sayar da awara ba shadda suke tashi idan kaje kusa da su sai hamamin wari ne ke tashi. Amman malama Hindu daga ita har yaranta tsaf tsaf suke. Uwa uba ko'ina a killace musanman parlorn da take a zaune...
Ga plate din da aka zuba mata shima tas a wanke yake...tana cikin ci sai ga nawrah ta dawo rike da lemo da ruwa a hannun ta,..
"Ummy gashi"
"Yawwa an gayshe ki. Mikawa anty qibdiyya abincin"
"Tohm ummy"
Nawraah ta karasa wajen hajiya qibdiyya ta ajiye mata lemon da ruwa. Hajiya qibdiyya ta daga Kai da sauri ta kallo malama Hindu tace
"Ruwa kawai fa nace. Don Allah a mayar da shi. Kinji?"
"Ki dubi girman Allah ki amince kinji? Hindu ta fada mata.
"Ai shikenan ... Bata ta shanye naga wata karama awajen. Dake bana shan Zaki yanzu sosai Ina kan dieting ne"
"Allah ya bada sa'a. Shikenan, dauki kije ku shanye"
Amnah ta durkusa har kasa ta karba da hannu biyu. Hajiya qibdiyya na kallon ta dakyau kwarai matuka ta birgeta. Yar karamar yarinyar da bata shekara biyar ba amman take ladabi haka! Lalle iyayen ta sun bata kyakkyawar tarbiyya, ta Kuma luraa dukan su yaran nada hankali da biyayya. Ta kasa hakura bayan ta dangwali yaji ta afa a baka tana taunawa tace,
"Wannan ma yar kice ko?"
"Eh...Amnah ce"
"Mashaa Allah su nawa kenan kaman uku ko?"
"A'ahh su hudu, Biyu mata, Biyu maza.... Akwai Ashir shine wancen nawaje me tuyar awarar .sai Ashfeef sai sai nawraah wadda ta kawo lemon nan da ruwa. Sai kuma autar mu Amnah.."..
"Mashaa Allah Allah ya raya su ya musu albarka"..
"Allahumma Aameen"..
Ta matso da robar wankin ruwan da aka kawo gabanta ta wanke hannuwan ta..
"Nagode sosai.. Allah ya kara kasuwa mai albarka Amin"
"Aameen" ,
"Bayan awara sai mai kike sayarwa?"
"Awarar ce kawai ba wani abu"
"Mashaa Allah... Idan ba takura ko zaki dan dinga zuwaa kina tayani wasu aiyukan na gidah ? Mai aiki na ce tatafi. Itace mewa yara girkin abunda suke so. "
Malama Hindu tayi shiru Kafin ta daga Kai tace,
'"To zanyi shawara da abbiey dinsu. Idan ya amince zaki gani."
"Ga number wayata nan. Ki bani taki. Idan har kin amince zaki dinga zuwa to seki Kira a aiko driver ya dauke ki"
"Lalle Auwalu wallahi ni dariya ma kake bani wai daki . Wancen akurkin ne daki? Wancen Dan ficicin wajen kamar bandakin kaji zaka ce mun daki? Koda yake banga laifin ka ba duk wata Yana sanmaka sadaka fisabilillahi ai shysa idanuwanka sika rufe baka ganin lefin su. Batin na mayar musu da mukullin na kwashe kiwon na Kuma ba zan ba. Nace bazan kwashe din ba. Raba Arne da makami ibada ne. Don sun dau wancen shirme wajen cikin tarin dukiyar su ta Ina Allah zai rage su? "
Bappah auwalu yayi kwata Yana cije kasan labban sa yace,
"Wadatar zuciyaa ce kawai da junaidu da iyalin sa alhamdulillah. Domin kowa sheda ne junaidu ya sayar da sauran kadarorin sa da sukai ragowa ya fara harkar kasuwancin Nan da ita ya sanwa Mai dakin sa take awara suka taru suke rufawa junan su asiri. Nan danacee maki ga dubu uku ki fara sanaa kema ai kikayi don haka karki sake kawo mun sukar Yan uwan kinji na gaya Miki" Yana gama magana ya saka Kai ya shige kitchen tabi bayansa tana sakee fashewa da dariya tana harara tana mita,
"Dubu uku... Allah ya kwashewa dubu ukun Nan albarka. Wallahi Auwalu nafi karfin dubu. Wacce sanaar Zan fara da dubu. Har da wani mun gori wai kar na karar kawo sukar Yan uwan ka. Yo ai ba sai kamin gori ba. Abunda naka gajiya da fada kullum nasan junaidu da Hindu Yan uwanka ne na jini dukkan su. Mtscew aikin kawai"
Ta shige daki ta tana bugo kofar garam. Bappah auwalu ya tabe kansa kawai yana juye awarar ababban tray...
::::::::
Wata hadaddiyar luntsumemwniyar mota ce ta faka a daidai kofar gidan... Sliding mirror din bayanta tayi na owners corner tana hangar dandazon layin awarar..
"Hajiya kinga layin ko! Yasin Kuma duk Wanda na roka abani basa yadda Yan taurin Kai ne Mutanen dake layin"
Agogonta ta sake kalla lokaci na gogawa. Cikin ta sai kugin yunwa yake gashi awarar kawai take son ci.
Batace masa komai ba ta bude kofar motar ta futa...Kallo daya zakai mata kasan wannan daga jinsin masu farcinan Susa tafito. Dubata kayan dake jikinta kadai ma abun kallo ne tabbas kudi yayi kuka awajenta.
Agogon dake daure awutsiyar hannunta Rolex ne latest design na shekarar. Jakar hannunta samfurin hems. Fara ce sosai tamkar baturiya, fatar ta sai sheki take duk kuwa da katon sunglasses din prada designer dake sakale a idanunta...Kai tsaye ta shige cikin gidan tamkar ta San masu gidan.......
[2/21, 6:52 AM] Hafsaat🧕: *_KWANKWASON JIMINA!!_*
_(MAI WUYAR SHAFAWA)_
🦩🦯🦾
_✍️: MX_
*_ZAFAFA BIYAR 2024_*
_vip pages na arewa👇_
*_arewabooks:mssxoxo_*
*_paid page :11_*
______
::::::::::::::::
***Bakinta dauke da sallama a gayance ta shiga cikin gidan har yar rumfar da Malama Hindu da yaran nata ke zauna suna ta tuyar awara har kasake biyu manya. Ga layi mashaa Allah anata shige da fice na sayan daddadar awarar...
Saboda awarar na da matukar dadi ga laushi mai tattare da kwai daya lullubeta. Tasha kayan hadi. Ga tumatir da albasa cucumber a yanke a gefe da Kuma yajin tafarnuwa sai kamshin kayan kamshi yake yi...
Babban al-muhim Kuma awarar akwai tsafta. Komai a tsaftace idan kaje saya. Harta abun daukar awarar aware yake a gefe da ledar hannu ta dauka itama. Don haka Yan hayu masu kudin birnin Kai har ma da talakawan ma siya sukeyi... Ga faraa da karanci da malama Hindu da yaranta ke nunawa masu sayar awarar ta su....
Wannan yasa da karfin addua da istigfari da shimfidar fuska da Kuma kyautatawa irinta Hindu da ahalin ta yasa baki daya mutane ke kaunar awararta. Don kullum sai ta kare idan anzo saya babu duk yawanta....
Ta lumshe idanun ta ta bude a lokacin data karasa inda suke suyar awarar. Malama Hindu ta daga Kai da sauri duk suka juya suna kallonta hadi da amsa sallamar da tayi Kafin daya bayan daya su shiga gayshe ta.
Ta amsa fuskar ta a sake. Malama Hindu ta mike da sauri tana cewa
"Hajiya shigo ciki"
Murmushi tayi cike da mamakin bata taba zuwa ba, Amman tamkar sun Santa har da cewa ta shiga cikin gidan?
Bakinta dauke da sallama ta shiga parlorn malama Hindu ta amsa tana daga tsaye .
"Ga wuri ki zauna, mu Kara gaisawa . Barka da yammaci? Iyalin kalau?"
"Alhamdulillah." Ta amsa ta tana duba parlorn dan karami madedeci, Amman a killace ko'ina tsaf tsaf a gyare sai kamshin turaren wuta ne ke tashi...
Lalle suna da tsafta . Ganin ba wani baki dake ciki ko masaaniyar zuwan ta balle tace shiryawa sukai .
"Ma shaa Allah" malam Hindu ta fada...
"Kinsan gidan Dr. Abubakhr dollars?"
Malama Hindu ta girgiza kai da sauri tana mai him ta da kallon Karin bayani,
"bansan shi ba gaskia"
"Hakane kam ba lalle ki San shi ba. Dubada bangaren ku daban namu damu. To shi Dr. Abubakhr din miji na ne. Ni Kuma sunana hajiya qibdiyya. Kusan kullum ai Ina aiko a saya mun awara a wajen ki"
"Allah sarki. Nagode Allah ya saka da alkhairi. Da ke mutanen da yawa bazan waye wanene ke zuwa ba"
"Hakane kam..." Hajiya qibdiyya ta fada tana murmushi hadi da duban agogon da ke daure a wutsiyar hannun ta tace,
"Yanzun ma shine mun fito tare da shi tun dazu yacemun layi yayi yawa Dakyar idan zaa samu.."
Malama qibdiyyah ta kada Kai Kafin tace,
"Eh wallahi.. masha Allah Nan da Nan da anyi take karewa. An goggode muku baki daya masu saya Allah ya saka muku da mafificin alkhairin sa. Aameen"
"Aameen"..
"Shysa na fito da Kai na .. naji zan iya samun awarar ko kuwa. Wallahi wannan ne shi ya saka " ta yi shiru bata karasa ba.
Malama Hindu na nazarce da ita daman tun shigar ta gidan dazu a farko ta hango cikin da ke jikin ta. tayi murmushi tace,.
"Allah ya raba lafiya hajiya. Ba matsala wallahi. Zaki ci anan ko a zuba Miki a pack ki tafi da ita?"
"Aah mashaa Allah, Nagode kwarai. Gashi" ta Mika mata Yan dari biyar guda biyu.
"Ta dubu biyu kenan? Har zaki cinye ta dubu biyu?
"Karki damu. Zubamin a plate kawai na ci anan. Kamar guda takwas ta Isa"
"To bari a kawo. Amman dan Allah ki rike kudin nan wallahi zan baki kyauta. Uwa uba Kuma kudin sunyi yawa "
"Ahh yar uwa banason musu "
"To shikenan nagode Allah ya saka da alkhairi Amin"
Malama Hindu ta nufi wajen babbar food flask da suke saka awara ta dakko plate ta zuba awarar fal da kayan hadi da yaji aciki..
"Gashi ranki ya dade... Bari a kawo ruwa"..
"Kakk takura kanku bari na ce driver din waje ya kawo"
"Aa dan Allah . Ki bari nima na sami lada tukun"
Hajiya qibdiyya tayi murmushi kawai hadi da kada Kai tace,..
"To shikenan tunda haka kikace. Nagode kwarai "
Malama Hindu ta sake fita tana Kiran Nawraah. Nawraah dake zubawa wani coleslaw acikin kwanon abinci ta mike da sauri,
"Naam ummy"
"Ungo rike. Ki sayo lemo daya karami da ruwa babba shima daya. Kiyi sauri banda wasa akan hanyar"
"Tohm ummy" ta fada da sauri harda hadawa da gudu. Malama qibdiyya ta koma wajen su Ashfeef dake tuyar auren Ashfeef ya hanata ta hanyar rcewa,
"Ummy kin har bakuwa ita kadai fa. Ki koma zamu karasa Allah"
"Hamma kaji abunda yace ko"
Ashir yayi murmushi Yana sosa keyar sa yace,
"Kije ummy ku cigaba da hirar ku aii sauran kasko daya daya mu karasa"
"Tohm sannun ku da kokari. "
"Yauwa ummy"
Komawa parlorn tayi wajen hajiya qibdiyya. Hajiya qibdiyya dai sai zura lomar awara take. Tamkar zaa kwace mata saboda yadda ta gigice tana wani lumshe idanun
Hajiya qibdiyya ta saci kallon malama Hindu. Jikinta a tsaftace ba akanta irin masu sayar da awara ba shadda suke tashi idan kaje kusa da su sai hamamin wari ne ke tashi. Amman malama Hindu daga ita har yaranta tsaf tsaf suke. Uwa uba ko'ina a killace musanman parlorn da take a zaune...
Ga plate din da aka zuba mata shima tas a wanke yake...tana cikin ci sai ga nawrah ta dawo rike da lemo da ruwa a hannun ta,..
"Ummy gashi"
"Yawwa an gayshe ki. Mikawa anty qibdiyya abincin"
"Tohm ummy"
Nawraah ta karasa wajen hajiya qibdiyya ta ajiye mata lemon da ruwa. Hajiya qibdiyya ta daga Kai da sauri ta kallo malama Hindu tace
"Ruwa kawai fa nace. Don Allah a mayar da shi. Kinji?"
"Ki dubi girman Allah ki amince kinji? Hindu ta fada mata.
"Ai shikenan ... Bata ta shanye naga wata karama awajen. Dake bana shan Zaki yanzu sosai Ina kan dieting ne"
"Allah ya bada sa'a. Shikenan, dauki kije ku shanye"
Amnah ta durkusa har kasa ta karba da hannu biyu. Hajiya qibdiyya na kallon ta dakyau kwarai matuka ta birgeta. Yar karamar yarinyar da bata shekara biyar ba amman take ladabi haka! Lalle iyayen ta sun bata kyakkyawar tarbiyya, ta Kuma luraa dukan su yaran nada hankali da biyayya. Ta kasa hakura bayan ta dangwali yaji ta afa a baka tana taunawa tace,
"Wannan ma yar kice ko?"
"Eh...Amnah ce"
"Mashaa Allah su nawa kenan kaman uku ko?"
"A'ahh su hudu, Biyu mata, Biyu maza.... Akwai Ashir shine wancen nawaje me tuyar awarar .sai Ashfeef sai sai nawraah wadda ta kawo lemon nan da ruwa. Sai kuma autar mu Amnah.."..
"Mashaa Allah Allah ya raya su ya musu albarka"..
"Allahumma Aameen"..
Ta matso da robar wankin ruwan da aka kawo gabanta ta wanke hannuwan ta..
"Nagode sosai.. Allah ya kara kasuwa mai albarka Amin"
"Aameen" ,
"Bayan awara sai mai kike sayarwa?"
"Awarar ce kawai ba wani abu"
"Mashaa Allah... Idan ba takura ko zaki dan dinga zuwaa kina tayani wasu aiyukan na gidah ? Mai aiki na ce tatafi. Itace mewa yara girkin abunda suke so. "
Malama Hindu tayi shiru Kafin ta daga Kai tace,
'"To zanyi shawara da abbiey dinsu. Idan ya amince zaki gani."
"Ga number wayata nan. Ki bani taki. Idan har kin amince zaki dinga zuwa to seki Kira a aiko driver ya dauke ki"