← Book details Kwankwason Jimina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 41

Sashe 12

Kwankwason Jimina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

_AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_

_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._

_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_

_NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_

_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_

:::::::;

   "Ka san shi ne abbieyn su?" Ta tambaye shi, Fuskar ta dauke da son sanin karin bayani...

Malam junaid ya kada mata kansa cikin tabbatarwa yace,

"Na san shi..... Amman ba wai sanayya sosai ba. Aminin mai gidan mu ne nan inda muke aiki a maqera. Alhaji Sambaso. Abokai ne kwarai da gaske. Don wadanda suka dade suna aiki a wajen ma suka ce kullu yaumin tare suke. Daya yana wajen daya... Suka ce mutanen kwarai ne sosai. Kuma yanada kyauta ainun shi Dr. Abubakhr din domin nima kwanaki da na aiko Ashir da dubu biyu ya kawo miki wanda nace miki awajen aiki aka bamu kyauta ai shine wanda ya mana kyautar. Dubu biyar biyar... Ko da na tambayi abokanan aiki na awajen sukace mun sunan sa Dr. Abubakhr dollars... Aminin Alhaji Sambaso ne. Don da sukace daloli yake rabawa ma da su yake kyauta. Anan ya gado sunan nasa. Ana ce masa Alhajin dollar." Ya kai karashen zancen yana kada kansa cikin tabbatar da maganganun da yayi.

"Mashaa'Allahu..... Lalle mutanen kwarai ne..."

"Ba lefi kam... A dai yadda mutane suke fada. Kuma nima da zai babbamu kudin hannu biyu ya karbe ni har yake tambayar shi uban gidan namu yana ce masa ya sunana? Amma ni sabon dauka ne ko dan bai sanni ba. Alhaji Sambaso yace masa eh daga baya na dawo Naduka da iyalina..."

"Mashaa Allahu, Allah sarki... To Allah yasaka musu da alkhairi duka damu baki daya"

"Allahumma Aameen ... Ina sauraron ki. Meya faru?"

"Yauwa to ashe mai dakin sa ce. Tace sunan ta hajiya qibdiyya kuma ita mata ce agare shi. Wai ko da direban yace mata akwai laayi ba lalli su samu ba shine ta kasa hakuri kasancewar batada lafiya tana Kuma son taci awarar sosai. Shine tashi go ciki kanta tsaye tana sallama baiwar Allah..."

"Allah sarki. Allah ya bata lafiya yasa kaffarane"

"Allah ya sauketa lafiya"

"Aameen"

"Don daman tana shigowa Ina duban yanayinta kasancewar saitin wajen Kwan lantarkin nan ta tsaya hasken ya haske ta nan na hango mashaa Allah. ..."

"Allah sarki.... Ina sauraron ki sai meya faru?"

Malama Hindu ta sauke numfashi tana murza yatsunta tace,

"Catai idan ba damuwa dan Allah ta yaba da hankali na da tsafta ta idan zan iya girkawa yaranta abinci mai yi musu tatafi... Ta bani wani kati da number wayarta ta karbi tawa.."

Bappah junaidu ya kada kansa kana ya numfasa ainun tukun yace,

"Sai kika bata amsar me?"

"Ina ni Ina yanke hukunci abbieyn su? Ai sai abunda kace. Kaga yaran nan suma haka suka fada sukace duk hukuncin da abbiey ya yanke Allah sa shine mafi alkhairi Amin"

Bappah junaidu ya sake numfasawa ya daga kansa tamkar mai tunani sai Kuma ya sauke yace,

"Wane irin aiki kenan?"

"Abinci.... Na yaran ta, meyi musu tatafi ita kuma tayi nauyi"

"Tohm banyi niyyar amincewa ba gaskia dubada ba sanin hallayar ta mukai ba sai dai dan kin ga wasu daga ciki datazo din .. Kuma mai gidan nata ma ance bashida matsala. Babban abunda yasa zan iya amincewa Kuma shine dalilin wannan nauyi da kikace tayi Allah ya sauketa lafiya Amin"

"Aamin ..abbiey ka amince kenan?"

Bappah junaidu ya kada Kai Kafin yace,

"Eh to.... Bazan hanaki ba. Ban Kuma gama amincewa da barin ki kije ba saboda banyi magana da Hamma ba naji hukuncin dashi zai fi dacewa duk kuwa da nasan babu matsala ... Amman zan same shi yanzu inshaa Allah. Duk yadda muka tattauna muka yanke zan gaya miki.",

"Toh shikenan abbieyn su. Allah ya zaba abunda yafi alkhairi a rayuwar mu gaba daya Amin"

"Allahumma Aameen..."

"Azubo abincin yanzu?"

"Eh azuba.. Amman akai wajen su Bappahn su zanje muchi da shi daga nan sai mu tattauna abunda zamuyi idan na dawo zakiji komai"

"Toh Allah yasa muji alkhairi Amin, bari a zuba."

"Aameen... Allah ya miki albarka"

"Aameen abbieyn su... Duk hukuncin daka yanke na aminta da shi wallahi. A har kullum amincewar ka nake so a dukkanin lamurana. Kasani har a raina ban yanke hukuncin komai ba sai wanda ka zabar mun. Hasalima bansa zanyin ba. Dubada aikin awara da mukeyi muma anan din."

"Nasani Hindu.... Kada ki damu kinji? Mu Mika lamuran mu wajen Allah baki daya. Badan rayuwa ma data sauya mana ba Hindu ai munfu karfin duk aiyukan nan abaya... Sai dai ma mu mu kyautar ba dai abamu ba. To ruwa ne ya daki babban zakara. Allah yasamu dace"

"Allahumma Aameen..."

Kasan suma sauka a tare. Bappah junaidu ya fice zuwa gidan bappah Auwalu.

Ya yinda malama Hindu ta nufi kitchen cikin babban tray ta jera komai na abincin dede cin su ta hada da plates biyu da cokula,

"Ashfeef..."

"Naam ummy"

"Ungo bi abbieyn ku dashi ka Kai musu gidan bappan ku acan zasu ci"

"Tohm" Ashfeef ya karbi tray din ya fita ya nufi gidan bappah Auwalu.

A barandar kofar gidan ya hango su a zazzaune su biyun akan tabarma. Ya kai musu ya ajjye agaban su bayan yayi sallama ya gayshe da su.

"Sannun ka Ashfeef . Allah yayi albarka" Cewar bappah Auwalu

"Aameen Bappah..."

"Tashi kaje ko? Magana zamuyi"

"Tohm abbiey. Bappah a huta lafiya"

Mikewa yayi har zai nufi hantar gidah yaci karo da Ahmad tsaransa wato yayan Layla. Abokin sa ne kuma dan uwan sa ne. Wata biyu ne a tsakanin su. Don haka suna aminta sosai.

"Waje na kaje ne?" Ahmad ya tambaye shi Yana nuna kofar gidan su

Ashfeef ya girgiza kai yana sosa kasan keyar sa yace,

"Wajen su Bappah naje na kai abinci"

"Okay... Ya za'ai ball fa da Argentina zo muje mu kalla. Ana haskawa a gidan kallon ball dinnan. "

"Tohm bari na tambayi ummy tukun. "

"Ga bappah nan ka tambaye shi mana"

"Abinci zasuci Kuma magana zasuyi shi yasa. "

"Okay muje ka tambaye ta"

Suka mike suka tafi gidan su Ashfeef din suna tafe suna hira. Suka shiga cikin gidan bakin su dauke da sallama.

Ahmad ya gayda su ummy ya zauna a bakin kujera. Ashfeef ya tambayi ummy tace,

"Kuje amman karku dade ana tashi ku dawo gidah"

"Inshaa Allah ummy"

Ashir na zaune yana sauraron labarin da Amnah ke bashi na yara ya saka hannu a aljihun sa ya zaro nera hamsin ya mikawa Ahmad

"Ungo ku sayi wani abun"

"Mungode Hamma"

"Godia muke Hamma"

Suka fice sunata murna. ..ummy ta dubeshi tayi murmushi kawai... Kyawawan halayen Ashir sunada wuyar misaltuwa....

____
Bappah junaidu da bappah Auwalu sun jima sosai suna tattauna sun Kuma yanke shawara maganar aikin ummy na gidan Dr. Abubakhr dollars..

Don haka Kai tsaye ya nufi gidah bayan sun gama maganar. Ya shigaa parlor bakinsa dauke da sallama ba kowa yaran duk sunyi bacci sai malama Hindu data saka radio a kunne tana sauraron wa'azin da akeyi...

_INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_

_KU MARMATSO KUSA...🔊_

_ZAFAFA BIYAR 2024_

_ZAFAFA BIYAR!!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_

_SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_

_YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_

_GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_

_________

_1_
*_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_

_2_
*_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_

_3_
*_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_

_4_
*_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_

_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
[2/22, 6:28 PM] Hafsaat🧕: _K'K'J_
_(M/W/S)_

_✍️:MX_

_15_

_ADVERT👇👇_

_YERWA INCENSE AND MORE_
_(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_

_INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_
_TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_

_MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_

_*YERWA INCENSE AND MORE*_
_DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._

_AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_

_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._

_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_

_NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_

_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_

::::::::

Ya sake sakin sallama a karo na biyu yana Mai zare takalman dake kafafun sa...

Sai a sannan ummy ta jiyo sautin sa. Ta zare rediyon daga kunnenta tana mikewa tsaye,

"Sannu da zuwa abbieyn su"

"Sannu kade... Yi hakuri na shagala munata hira ashe dare ya kule haka .. duk sunyi bacci ko?"

"Wallahi kuwa... Kowa yayi bacci"

"Ayyah... Yi hakuri na shiga hakkin ki. Wallahi sai da Nusaiba ta leko tana cewa ya shigar mata da tabarmar idan mun gama na duba agogo nace kai haka dare ya wuce bamu sani ba? Astagfirullah."

Malama Hindu tayi murmushi tana jijjiga kai tace,

"Kai Nusaiba.... Halinta sai ita"

Bappah junaidu yayi murmushin shima yace,

"Allah yasa mu dace"

"Aameen..."

"Muje ko?... Mayi maganar a sama"

"Tohm abbiey."
Chapter 12 · 0% Book details