Sashe 22
Kwankwason Jimina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Allah ya muku albarka baki daya... Ashfeef naga ka wanke takalman ball dinnan dan Allah dai karkayi dare kar ka dinga dare ma dai kaji ko?"
"Ummy kwana zaki acan ne?" Ashfeef ya fada Yana kallonta Jin tamkar kwana zatayi tana bashi sallahu
"Aa inshaa Allah komai dare da zan Kai a gidah zan kwana... "
"Tohm Allah yasa"
"Amnah banda wasan ruwa kinji? Kinga mura kike yi"
"Tohm ummy"
"Zo nan"Ta fada tana duban ta
Amnah ta mike daga kalbar da ake mata daman saura daya. Ta karasa wajen ummy . Ummyn ta rungumeta tsam a jikin tana shafa gadon bayan ta
"Allah ya miki albarka Amnah. Allah ya raya ku ya tsare kuruciyar ku har girma Aameen"
"Aaameen.. "suka amsa ta baki daya
"Layla bappah Auwalu Yana nan ne?"
"Eh Yana gidah"
"Okay. Idan nawrah tafito kuce ta sameni agidan Bappah Auwalu."
"Tohm ummy,"
Fita tayi da sauri ta nufi gidan Bappah Auwalu... Ta kwankwasa kofar nusaiba ta bude tana mita ta dauka Layla ce,
"Dan uban ki kinje kin zauna. Marar zuciya kawai. Kullum bini bini kina hanyarr gidan su dan uban ki. Uwar taurin Kai"
"Kai Nusaiba.... " Ummy ta fada tana girgiza kai ta Kara da cewa,
"Assalamu alaikum ga bakuwar yammaci"
"Waalykm Salam Hindu ce Ashe. Na dauka Layla ce"
"Uwar Layla ce wannan. Kai Nusaiba kiyi waa kanki fada dan Allah ki dinga shan ragowar ruwan alwala ance Yana saka hakuri ya tausasa zuciya"
"Fada mata dai Hindu."
"Ah Bappahn su ashe kana ciki,? Barka da yammaci?"
"Barkan mu dai. Ina ciki . Duk Ina jiyo ku Ina jin maganganun da take yi ai kinsan mai hali baya fasa halin sa" ya fada yana hararo nusaiba.
Ta gatsina fuska tana juya baya tace,
"Maganar gaskia ce ai. Layla kaman taci kafar kare saboda yawo,kullum tana gidan su haba ai da gajiya "
"Gajiyar me Nusaiba? Kada ki manta da nan da can din duk tsatso daya ne. Ko yau Layla ta tattara kayan ta ta koma can wallahi gidan su ne, Haka zalika idan Nawrah ta dawo nan ma gidan su ne, Nusaiba ke fa uwa ce. Maganar dama da nazo miki kenan nace miki ke uwa ce. Ta iya yiwuwa agaba ke zaki zama mahaifiyar su gaba daya ke zaki aurar da su. Ba wai sai bayan rai na ba ko a yanzu. Yanzu ace idan rai yayi halin sa Nusaiba ke ce mafi kusantakar zama uwa agare su wadda zata share musu hawayen maraicin su Nusaiba."
"Haba Hindu maganganun me ne haka kikeyi? Ai babu Wanda yasan gawar fari sai Allah. Kuma 'yayan ki ko taki ko ta so 'yayanta ne. Haka zalika nata 'yayan naki ne"
"Kwarai dagaske baooan su. Don ni anawa rashin hankalin wallahi gani nake ko ba rai na ba zasuyi kukan maraici ba saboda Ina da ku"..
"Bar ma wannan zancen ta iya yiwuwa ma duk mu mutu mu bari ki. Yaran namu ma ke zaki cigaba da renon su . "
"Sai dai idan kai ne zaka mutu ka barta Allah . Inshaa Allah sai na zama mai uban kudi na tara dukiya na zagaye kasashen duniya , na taka nera na bada dollar na lika yan dubu dubu da kyautar motoci sai na zama babbar attajira tukui" Cewar nusaiba tana murmushi da girgiza kafa
"Toh Allah ya kyauta..." Bappah Auwalu ya fada
Malama Hindu tayi murmushi ta mike tsaya jiyo muryar nawrah tana cewa ,
"Ummy na gama ki fito mu tafi"
"Bari muje bappan su. Dama gidan aiki nazan leka. Allah ya kaddara saduwar mu"
"To masha Allah, Allah ya dawo daku lafiya"
Sa kayi ta fita. Nusaiba taja dogon tsaki tana bankawa kofar da malama Hindu tabi ta futa da harara. Ta mike tamkar jirgin sama kamar zata tashi sama ta shige dakinta tana rufo kofar da karfi ji kake 'kauuuu'
Malama Hindu ta fita suka jera sika nufi titi kasancewar direban da zai dauketa ma ba zai samu damar zuwa ba. Don haka titi suka fita ta saka sika tsaya awajen aikin kai gidan nata wato bappah junaidu.
Nawrah na daga can gefe ta basu waje tana wasa da kasan hijabin ta.
"Hindu na...."
"Naam junaidu na..... Ya aikin naku ?"
"Alhamdulillah... Ai na gaya miki mai gidan dakike aikin ogan namu sun shiga meeting dazu ai yace mu taya shi da addua wasu manyan kadarori yake so ya mallaka inde ya samu dama zai mana manyan kyauta sosai . Kinga sai mu sake gyara gidan nan sosai"
"Oh shi ya saka mai dakin sa tace ya shiga meeting kar nazo da safe sai dai da yamma kenan. Allah sarki to Allah ya amince. Amma abbiyen su ai gidan mu babu abunda ya same shi kasa ka wani damu kanka Allah "
"Shagon awara nake son na bude miki daga gefen baya dinnan zaa tada shago a dingah sayar da awarar da sauran abubuwa."
" Allah sarki junaidu. Allah ya saka maka da mafificin alkhairi. Hakika bani da bakin godia agare ka. Ka a sani har kullum ba zan taba dai na godewa Allah da kasancewa mata agare ka ba. Allah yabar mun Kai har gaban abadan abbiyen su. Allah ya hada fuskokin mu da alkhairi yasa ko a aljanna mu kasance atare da juna. Nagode kwarai... "
"Wadannan kalaman fa Hindu? Sai kace wadda zatayi tafiya. Toh Allahumma Aminn ai komai na miki ban fadi ba Hindu. Domin duk inda matar kwarai ta Kai kin Kai kin zarce ma"
Murmushi tayi ta dan kallo gefen Nawraah taga ta juya baya tana danna wayar ummyn dake hannun ta yayinda ba maaikaci ko daya awajen. Ta rungume da shi da sauri ta sake shi tana goge hawayen dake neman zubo mata,
"SubhanAllah kukan meye wannan,?"
"Kuma dadi ne.. kukan farin ciki ne, kuka ne mai dauke da tarin ma'anoni. Kasancewa ta mata agare ka. Kasancewar uwa ga yarana. Kasancewar suruka ga su bappah Auwalu. Abubuwa da yawa. Nagodewa Allah da samun zuri'a ta gari wato hamidniyya Lebanon. Allah ya biyaka da aljanna Junaid .. Allah kuma ya cigaba da bude maka kofofin alkhairi ka cigaba da kula da yaran mu. Gasunan amana ne Allah yabamu. Kaga nj dai bana nan yanzu aiki zan tafi. Ka Kula da su don Allah.."
"inshaa Allah Hindu... Wannan kalamai haka? Yanzu zan koma karki ji komai Allah. Nasan dama saboda su kiketa maganganun akai kwantar da hankalin ki kinji?"
"Inshaa Allah. Abincin ka Yana can na bawa Hamma sallahu. Bari mu tafi kar lokaci ya kure"
"Sai kun dawo Allah ya bada sa'a ya miki albarka "
"Aameen abbieyn su . Komai dare ai inshaa Allah gidah zamu dawo"
"Tohm Allah ya amince Hindu"
Daga masa hannu tayi shima yana daga musu suka nufi tasi suka shiga ta Kai su can unguwar ta su Dr bintu
Gidan sika shiga bakunan su dauke da sallama suka gayshe da ita tana parlor itada mai gidan nata
Kitchen suka zarce nan da nan ummy ta fara hada abubuwan abincin da zata dafa yayinda nawrah ke tayata.
A haka har suka kammala komai. Ummy da nawrah suka nufi parlorn suka jera komai akan dinning
Dr bintu da Alhaji Sambaso mijinta sunata magana a parlorn dauke da wasu takardu agaban su...
Ya yinda tashar talabijin ke nuna wakar Maher Zain ta rahamatun lil alamin
Nawrah na son wakar don haka ta danna recording ta ajiye wayar daga can gefe don ta tariyo mata muryar Maher Zain da ke raira baitin
Waya Alhaji Sambaso ya daga ya gama amsa kiran ya saki Kara da karfi Yana jijjiga Dr bintu yace,
"Alhaji ateeks ya amince.... Plazas dinnan din sun zama mallaki na. Harda estates din mejesa da guzare dana Gpo da na bayan Maduki., shikenan nayiwa Dr abubakhr warwas matsiyaci duk tarin arzikin sa da sannu sai sun zama mallaki na..."
"Alhamdulillah.... Dama naki jinin munafukar matar sa sai uban izza da iyayi. Allah yasa su mutu acan duka kowa ya h...
Ji kake taratsats malama Hindu dake tafiya tana jinsu zata ajiye tray din jikinta sai rawa yake jin maganganun da suke kafafunta suka fara rawa tray din ya kufce daga hannuwanta ya fadi..
A matukar razane suka jiyo gaba dayan su suna kallon ta. Duk sai suka sha jinin jikin su,
"Me kike anan Hindu?" Dr bintu ta fada da karfi
"Ba abunda naji Dr.. Dan Allah kuyi hakuri santsi ne ya kwashe ni"
"Bangane ba abinda kikaji ba me kike nufi.?"
Nawrah na daga kitchen tana jiyo su ta fito da sauri ta janyo wayar ta,
"Menene wannan din me kike da waya?"
"Wayar ummy ce na ajiye" ta fada tana futa daga wajen recording din"
"Hajia sai da safe" malama Hindu ta fada tana kamo hannun nawrah
Dr bintu ta juya ta kalli mai gidan nata. Ya saka yatsa a hannu yana ciza shi.
"Hindu... Hindu?"
"Naam hajia dare yayi tafiya zamuyi"
"Ai baki gama ba, dama mana kunu" ta fada tana nuna mata kitchen
Jikin malama Hindu ya cigaba da kakkarwa tana yarfe yatsa tace
"Dan Allah hajia"
"Banason musu jeki dama mana kunu nace"
"Toh"
Komawa tayi kitchen ta janyo hannun nawrah jikinta na rawa suka futa tsakar gidan ta zaro nera dari ta mika mata,
"Maza maza tafi gidah"
"Ummy meyasa?"
"Ni dai nace miki ki tafi gidah ko? Tafi da wayar tawa ma "
"Idan aka kira ki fa"
"Baa wanda zai kira ma jeki yi sauri karki juyo ki, tafi gidah ki wuce kar ki dawo. Ki kashe wayar ma me kikayj awayar ne"
"Recording wakar Maher Zain nayi"
"Lokacin duk suna wadannan maganganun?"
"Eh bansani ba ni dai tun dazu na ajiye ta"
"SubhanAllah to tafi gidah dai ki kashe wayar idan kinje gidah ki bawa Hamman ku ya ajjye idan na dawo zan karba "
"Kai ummy?"
"Nawrah nace ki tafi ko?"
"Tohm shikenan. Ga tawa ki rike" ta mika naga wayar me torchlight ta ummyn ta da da ta bar mata ,
Ummyn ta girgiza kai tana kakaro murmushi tace,
"Ai dole sai kin saka na karba Kai nawrah dadi na dake KWANKWASON JIMINA ce MAI WUYAR SHAFAWA... Je ki Allah ya miki albarka..."
"Ummy kwana zaki acan ne?" Ashfeef ya fada Yana kallonta Jin tamkar kwana zatayi tana bashi sallahu
"Aa inshaa Allah komai dare da zan Kai a gidah zan kwana... "
"Tohm Allah yasa"
"Amnah banda wasan ruwa kinji? Kinga mura kike yi"
"Tohm ummy"
"Zo nan"Ta fada tana duban ta
Amnah ta mike daga kalbar da ake mata daman saura daya. Ta karasa wajen ummy . Ummyn ta rungumeta tsam a jikin tana shafa gadon bayan ta
"Allah ya miki albarka Amnah. Allah ya raya ku ya tsare kuruciyar ku har girma Aameen"
"Aaameen.. "suka amsa ta baki daya
"Layla bappah Auwalu Yana nan ne?"
"Eh Yana gidah"
"Okay. Idan nawrah tafito kuce ta sameni agidan Bappah Auwalu."
"Tohm ummy,"
Fita tayi da sauri ta nufi gidan Bappah Auwalu... Ta kwankwasa kofar nusaiba ta bude tana mita ta dauka Layla ce,
"Dan uban ki kinje kin zauna. Marar zuciya kawai. Kullum bini bini kina hanyarr gidan su dan uban ki. Uwar taurin Kai"
"Kai Nusaiba.... " Ummy ta fada tana girgiza kai ta Kara da cewa,
"Assalamu alaikum ga bakuwar yammaci"
"Waalykm Salam Hindu ce Ashe. Na dauka Layla ce"
"Uwar Layla ce wannan. Kai Nusaiba kiyi waa kanki fada dan Allah ki dinga shan ragowar ruwan alwala ance Yana saka hakuri ya tausasa zuciya"
"Fada mata dai Hindu."
"Ah Bappahn su ashe kana ciki,? Barka da yammaci?"
"Barkan mu dai. Ina ciki . Duk Ina jiyo ku Ina jin maganganun da take yi ai kinsan mai hali baya fasa halin sa" ya fada yana hararo nusaiba.
Ta gatsina fuska tana juya baya tace,
"Maganar gaskia ce ai. Layla kaman taci kafar kare saboda yawo,kullum tana gidan su haba ai da gajiya "
"Gajiyar me Nusaiba? Kada ki manta da nan da can din duk tsatso daya ne. Ko yau Layla ta tattara kayan ta ta koma can wallahi gidan su ne, Haka zalika idan Nawrah ta dawo nan ma gidan su ne, Nusaiba ke fa uwa ce. Maganar dama da nazo miki kenan nace miki ke uwa ce. Ta iya yiwuwa agaba ke zaki zama mahaifiyar su gaba daya ke zaki aurar da su. Ba wai sai bayan rai na ba ko a yanzu. Yanzu ace idan rai yayi halin sa Nusaiba ke ce mafi kusantakar zama uwa agare su wadda zata share musu hawayen maraicin su Nusaiba."
"Haba Hindu maganganun me ne haka kikeyi? Ai babu Wanda yasan gawar fari sai Allah. Kuma 'yayan ki ko taki ko ta so 'yayanta ne. Haka zalika nata 'yayan naki ne"
"Kwarai dagaske baooan su. Don ni anawa rashin hankalin wallahi gani nake ko ba rai na ba zasuyi kukan maraici ba saboda Ina da ku"..
"Bar ma wannan zancen ta iya yiwuwa ma duk mu mutu mu bari ki. Yaran namu ma ke zaki cigaba da renon su . "
"Sai dai idan kai ne zaka mutu ka barta Allah . Inshaa Allah sai na zama mai uban kudi na tara dukiya na zagaye kasashen duniya , na taka nera na bada dollar na lika yan dubu dubu da kyautar motoci sai na zama babbar attajira tukui" Cewar nusaiba tana murmushi da girgiza kafa
"Toh Allah ya kyauta..." Bappah Auwalu ya fada
Malama Hindu tayi murmushi ta mike tsaya jiyo muryar nawrah tana cewa ,
"Ummy na gama ki fito mu tafi"
"Bari muje bappan su. Dama gidan aiki nazan leka. Allah ya kaddara saduwar mu"
"To masha Allah, Allah ya dawo daku lafiya"
Sa kayi ta fita. Nusaiba taja dogon tsaki tana bankawa kofar da malama Hindu tabi ta futa da harara. Ta mike tamkar jirgin sama kamar zata tashi sama ta shige dakinta tana rufo kofar da karfi ji kake 'kauuuu'
Malama Hindu ta fita suka jera sika nufi titi kasancewar direban da zai dauketa ma ba zai samu damar zuwa ba. Don haka titi suka fita ta saka sika tsaya awajen aikin kai gidan nata wato bappah junaidu.
Nawrah na daga can gefe ta basu waje tana wasa da kasan hijabin ta.
"Hindu na...."
"Naam junaidu na..... Ya aikin naku ?"
"Alhamdulillah... Ai na gaya miki mai gidan dakike aikin ogan namu sun shiga meeting dazu ai yace mu taya shi da addua wasu manyan kadarori yake so ya mallaka inde ya samu dama zai mana manyan kyauta sosai . Kinga sai mu sake gyara gidan nan sosai"
"Oh shi ya saka mai dakin sa tace ya shiga meeting kar nazo da safe sai dai da yamma kenan. Allah sarki to Allah ya amince. Amma abbiyen su ai gidan mu babu abunda ya same shi kasa ka wani damu kanka Allah "
"Shagon awara nake son na bude miki daga gefen baya dinnan zaa tada shago a dingah sayar da awarar da sauran abubuwa."
" Allah sarki junaidu. Allah ya saka maka da mafificin alkhairi. Hakika bani da bakin godia agare ka. Ka a sani har kullum ba zan taba dai na godewa Allah da kasancewa mata agare ka ba. Allah yabar mun Kai har gaban abadan abbiyen su. Allah ya hada fuskokin mu da alkhairi yasa ko a aljanna mu kasance atare da juna. Nagode kwarai... "
"Wadannan kalaman fa Hindu? Sai kace wadda zatayi tafiya. Toh Allahumma Aminn ai komai na miki ban fadi ba Hindu. Domin duk inda matar kwarai ta Kai kin Kai kin zarce ma"
Murmushi tayi ta dan kallo gefen Nawraah taga ta juya baya tana danna wayar ummyn dake hannun ta yayinda ba maaikaci ko daya awajen. Ta rungume da shi da sauri ta sake shi tana goge hawayen dake neman zubo mata,
"SubhanAllah kukan meye wannan,?"
"Kuma dadi ne.. kukan farin ciki ne, kuka ne mai dauke da tarin ma'anoni. Kasancewa ta mata agare ka. Kasancewar uwa ga yarana. Kasancewar suruka ga su bappah Auwalu. Abubuwa da yawa. Nagodewa Allah da samun zuri'a ta gari wato hamidniyya Lebanon. Allah ya biyaka da aljanna Junaid .. Allah kuma ya cigaba da bude maka kofofin alkhairi ka cigaba da kula da yaran mu. Gasunan amana ne Allah yabamu. Kaga nj dai bana nan yanzu aiki zan tafi. Ka Kula da su don Allah.."
"inshaa Allah Hindu... Wannan kalamai haka? Yanzu zan koma karki ji komai Allah. Nasan dama saboda su kiketa maganganun akai kwantar da hankalin ki kinji?"
"Inshaa Allah. Abincin ka Yana can na bawa Hamma sallahu. Bari mu tafi kar lokaci ya kure"
"Sai kun dawo Allah ya bada sa'a ya miki albarka "
"Aameen abbieyn su . Komai dare ai inshaa Allah gidah zamu dawo"
"Tohm Allah ya amince Hindu"
Daga masa hannu tayi shima yana daga musu suka nufi tasi suka shiga ta Kai su can unguwar ta su Dr bintu
Gidan sika shiga bakunan su dauke da sallama suka gayshe da ita tana parlor itada mai gidan nata
Kitchen suka zarce nan da nan ummy ta fara hada abubuwan abincin da zata dafa yayinda nawrah ke tayata.
A haka har suka kammala komai. Ummy da nawrah suka nufi parlorn suka jera komai akan dinning
Dr bintu da Alhaji Sambaso mijinta sunata magana a parlorn dauke da wasu takardu agaban su...
Ya yinda tashar talabijin ke nuna wakar Maher Zain ta rahamatun lil alamin
Nawrah na son wakar don haka ta danna recording ta ajiye wayar daga can gefe don ta tariyo mata muryar Maher Zain da ke raira baitin
Waya Alhaji Sambaso ya daga ya gama amsa kiran ya saki Kara da karfi Yana jijjiga Dr bintu yace,
"Alhaji ateeks ya amince.... Plazas dinnan din sun zama mallaki na. Harda estates din mejesa da guzare dana Gpo da na bayan Maduki., shikenan nayiwa Dr abubakhr warwas matsiyaci duk tarin arzikin sa da sannu sai sun zama mallaki na..."
"Alhamdulillah.... Dama naki jinin munafukar matar sa sai uban izza da iyayi. Allah yasa su mutu acan duka kowa ya h...
Ji kake taratsats malama Hindu dake tafiya tana jinsu zata ajiye tray din jikinta sai rawa yake jin maganganun da suke kafafunta suka fara rawa tray din ya kufce daga hannuwanta ya fadi..
A matukar razane suka jiyo gaba dayan su suna kallon ta. Duk sai suka sha jinin jikin su,
"Me kike anan Hindu?" Dr bintu ta fada da karfi
"Ba abunda naji Dr.. Dan Allah kuyi hakuri santsi ne ya kwashe ni"
"Bangane ba abinda kikaji ba me kike nufi.?"
Nawrah na daga kitchen tana jiyo su ta fito da sauri ta janyo wayar ta,
"Menene wannan din me kike da waya?"
"Wayar ummy ce na ajiye" ta fada tana futa daga wajen recording din"
"Hajia sai da safe" malama Hindu ta fada tana kamo hannun nawrah
Dr bintu ta juya ta kalli mai gidan nata. Ya saka yatsa a hannu yana ciza shi.
"Hindu... Hindu?"
"Naam hajia dare yayi tafiya zamuyi"
"Ai baki gama ba, dama mana kunu" ta fada tana nuna mata kitchen
Jikin malama Hindu ya cigaba da kakkarwa tana yarfe yatsa tace
"Dan Allah hajia"
"Banason musu jeki dama mana kunu nace"
"Toh"
Komawa tayi kitchen ta janyo hannun nawrah jikinta na rawa suka futa tsakar gidan ta zaro nera dari ta mika mata,
"Maza maza tafi gidah"
"Ummy meyasa?"
"Ni dai nace miki ki tafi gidah ko? Tafi da wayar tawa ma "
"Idan aka kira ki fa"
"Baa wanda zai kira ma jeki yi sauri karki juyo ki, tafi gidah ki wuce kar ki dawo. Ki kashe wayar ma me kikayj awayar ne"
"Recording wakar Maher Zain nayi"
"Lokacin duk suna wadannan maganganun?"
"Eh bansani ba ni dai tun dazu na ajiye ta"
"SubhanAllah to tafi gidah dai ki kashe wayar idan kinje gidah ki bawa Hamman ku ya ajjye idan na dawo zan karba "
"Kai ummy?"
"Nawrah nace ki tafi ko?"
"Tohm shikenan. Ga tawa ki rike" ta mika naga wayar me torchlight ta ummyn ta da da ta bar mata ,
Ummyn ta girgiza kai tana kakaro murmushi tace,
"Ai dole sai kin saka na karba Kai nawrah dadi na dake KWANKWASON JIMINA ce MAI WUYAR SHAFAWA... Je ki Allah ya miki albarka..."