← Book details Kwankwason Jimina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 41

Sashe 14

Kwankwason Jimina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Wasu irin Royal chairs ne ainihin royal na sarauta. Kirar oman kalar golden da white. Ya yinda curtains din parlorn ma royal ne design din kujerun suma.

Kai harta marikin labulayen da tv stand da dinning area da sets dinsa da ke gefe duk royal ne. Komai da komai na parlorn royal design ne. Lamarin sai dai ache tubarkallah kawai.

Dattijuwar matar tafito daga cikin dakin da take tana gyara zaman dankwalin data daura akanta.

"Baliwar hajiya ce ke"

"Eh...Ina kwana ?"

"Lafiya kalau Alhamdulillah. Bari a gaya mata"

"Tohm shikenan"

"Ki zauna ga waje nan bari na kirata"

"Tohm godia nake"

Malama Hindu ta nemi waje ra zauna a kasan carpet jikin wata kujera, ta hango dattijuwar ta nufi wajen wata waya dake manne a bango 'intercom' ta danna wasu number ta kira waya.

"Assalamu alaikum... Eh tazo to shikenan" ta mayar da wayar ta shiga wata kofa dake kallon daya bangaren inda dinning area yake. Wanda zaka tabbatar kitchen ne

Tray ta fito dashi ta ajiye agaban malama Hindu. Dauke tray din yake da lemo da ruwa da snacks da kofi na tangaran,

"Bismillah tana zuwa"

"Nagode... "Malama Hindu ta fada tana gyara zaman tray din

Matar ta koma cikin kitchen ta rufo kofar. Malama Hindu na zaune shiru shiru sai dube dube take

Cikin haka sai ga sakkowar hajiya qibdiyya daga bene sanye cikin doguwar riga bubu ta material marar nauyi ta daura dankwalin kayan a kanta.

Ta dashare hakora a lokacin da suka hada idanu da malama Hindu

"A kasa? SubhanAllah... Tashi tashi ki koma kan kujerar dan Allah"

"Ah wallahi nanma ya Isa hajia. Ina kwana"

"Dan Allah banason musu ki hau ki zauna please. Mama Talatu, mama Talatu"

Malama hindu ta haye kan kujerar ta tsakure kanta a kasa.

Dattijuwar ta fito daga kitchen da alama itace malama talatun.

"Hajiya ga ni.."

"Mena ce miki idan bakuwar nan tazo?"

"Kikace nache kina zuwa. Na Kuma kawo mata ruwa da lemo da su cake."

"Bance ki ce ta zauna ta jira ba"

"Na gaya mata hajia"

" A kasan carpet saboda Allah? me ze hana kice ta hau kujera haba mama Talatu"

"Kiyi hakuri hajiya nayi kuskure"

Malama Hindu da sam bata dauka abunda hajia qibdiyya zata ce bane da sauri ta g girgiza kanta tana daga hannu,don sam batason daga zuwanta sanadiyyar ta mutanen da suke zaune da ita su bata Kuma ace ta dalilin ta. Cike da sauri tace

"Wallahi ta jatbte ni hannu biyu, Muka gaysa ta kawo mun su lemo. Allah ni ko tace na zauna akan kujerar ma bana zama hajiya. Nafi kaunar zaman kasan . Mama Talatu ba ruwanta wallahi"

Mama Talatu kanta a kasa ta ce,

"Ayi hakuri hajiya."

"Je ki...." Cewar hajia qibdiyya.

Jikin malama Hindu yayi sanyi. Gaskia sam batajin yadda hajia qibdiyya ta yiwa mama Talatu ba. Tamkar kuwa ta ga zuciyar ta. Tache da ita,

"Karfa ki dauka Ina da faada .... Wannan dinma kamawa tayi. Kinsan lokacin abu ka gyara shi kawai ba daga baya idan bata nan ba nazo inayi da ita ban kyauta ba. Haka nake ni a duk sanda kowane yayi Abu alokacin zan wankeshi awuce wajen . So wallahi wannan abun ma ya wuce. Kakki damu ai muna tare. Mama Talatu yar uwa ce ta zarce yar tayin aiki ba ita kadai bama harda sauran maaikatan.. kinaji na?"

"Ina sauran ki hajia"

"Ita wanan da tabar nan sunanta Mama Talatu. Babbar Mai aiki ce dake abincin gidan gaba daya idan zaa ma Mai gidan ma ita ke tayani, yanada diabetes so ba komai yake ciki ba"

"Allah sarki Allah yabashi lafiya Amin"

"Aamin Yaa Rabbi... Ni sunan ki nema ke kwatanin wlh"

"Sunana Hindu..."

"Mashaa Allah.. sunana hajiya qibdiyya kamar yadda na gaya Miki a baya. Alhaji abubakhr dollars shine mijina, Kuma babban maikacin lafiya ne da kasa keji dashi baki daya. Don har number yabo ta duniya aka bashi watanni uku da suka wuce. Na zangon farko kan mukamin gwarzon dayafi kowane likitan iya tiyatar haihuwa ",

"Mashaa Allahu hajiya. Allah yakara hazaka. "

"Aamin... Ni yar kasuwa ce. Ina saye da sayarwa na manyan dilolii ke kaiwa manyan yan kasuwa Kaya suna Kuma zuwa su Sara awaje na cargo cargo. inaga foundation na tallafawa marayu da marasa karfi Mai taken,

"MARIYATUL QIBDIYYA DOLLARS (Compassion care foundation) "

"Mashaa Allah! Allah ya kara tsarewa ya buda Amin"

"Aamin tare da ke. Yauwa sannan inada Yara uku, Wanda yaci sunan mahaifin su Dr. Muna kiraan sa da junior shine na fari, sai ta biyu Hayfa. Sai auta na na karshe.... ANEES ABUBAKHR DOLLARS.........

_INA MASOYAN ZAFAFA BIYAR?_

_KU MARMATSO KUSA...🔊_

_ZAFAFA BIYAR 2024_

_ZAFAFA BIYAR!!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_
_ZAFAFA BIYAR!!_

_SHIN YAN UWA KUNA DA LABARIN ZAFAFA BIYAR DINKU SUN SAKE ZUWAR MUKU DA WATA TAFIYAR LITTAFAN SU MASU MATUKAR MA'ANA DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA?_

_YA KE YAR UWA KADA KI BARI A BAKI LABARI... DOMIN DA A BAKI GWARA KI BAYAR...WAI AKACE ZUWA DA KAI YAFU AIKE_

_GA SUNAYEN LITTATTAFAN WANNAN TAFIYAR... CIKE SUKE DA ILIMIN DARUSSAN RAYUWA KI KOYA KUMA KI GYARA DA KAN KI..CIKI HARDA ZALLAR KAUNA TACACCIYA MARAR GAURAYE_

_________

_1_
*_AMEENATUH_*🧕💖: _MAMUH GEE_

_2_
*_TSUTSAR NAMA (ITAMA NAMA CE)🐛👣_*_:BILYN ABDULL_

_3_
*_GUDUN KADDARA🏃🐾_*:_SAFIYYAH HUGUMA_

_4_
*_KWANKWASON JIMINA(MAI WUYAR SHAFAWA)🦩🦯_*_:NANA HAFSATU (MX)_

_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
[2/24, 1:29 AM] Hafsaat🧕: _K'K'J_
_(M/W/S)_

_✍️:MX_

_17_

_ADVERT👇👇_

_YERWA INCENSE AND MORE_
_(DUNIYAR KAYAYYAKIN KAMSHI MASU MATUKAR DADI DA KAMA JIKI, GIDAH, KAYA DA SAURAN SU)_

_INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_
_TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_

_MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_

_*YERWA INCENSE AND MORE*_
_DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._

_AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_

_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._

_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_

_NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_

_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED_

::::
17

     Malama Hindu ta jinjina Kai tana sauraron hajia qibdiyya har ta karasa maganar da take yi.

"Mashaa Allah. Allah ya raya su baki daya ya inganta su ya Kuma tsare musu kuruciyar su har girman Amin "

"Aamin Aaameen godia nake .... Hindu, Allah Kuma ya saka da alkhairi da kika amince da rokon da nayi Miki...."

"Bakomai hajiya. Ni ceda godiya"

"Ni dai x.... Kinga me musu girkin tatafi kauye ne ganin gidah wai. To Kuma sai ta Kirani ma take cemun bazawarin da zai aure ta ya matsa yanaso ayi auren kawai. Nace mata babu komai wallahi ai auren shine gaba da komai. Allah yasa albarka. To yaran Kuma basa cin abincin da ake wa baban su Wanda mama Talatu keyi saboda akwai Abubuwa da yawa da baa saka masa a abinci kasancewar ciwon sukarin da yake da shi.... Wannan wadda tazo nan itace malama Talatu. Itace babbar mai aikin mu. Sai basariya tana Ina ne.? Basariya" hajiya qibdiyya ta kwadawa sunan basariya kiraa da karfi

Basariya ta sakko daga sama da sauri,

"Naam! Ga ni"

"Zo.."

Tazo har wajen su. Ta tsugunna ta dubi malama. hindu tace,

"Ina kwana?"

"Lafiya kalau basariya ."

"Itace basariya... Je ki"

"Mashaa Allah Allah ya rayata Amin"

"Aamin Aameen " direban daya dakko ki sunan shi malam Liti. Direba na ne shi.. Sai emeka direben Alhaji ne. Ana Kiran sa da oga emaka..... Da Ribado direban Yara ne. Ya kai su makaranta da.sauran su. Sai su Mudi, Barau... Masu gadi ne. Sai Samuel gateman, wato security in charge of the inspection da sauran su.. sai Ghali da dahiru masu wanki da guga. Bilal Mai share share. Nuhu gardener ne. Sai latifa ita ba kwana take ba jeka ka dawo take. Tana zuwa ta share ko'ina na cikin gidan nan ta gyara ta wanke da dakuna da sauran su. "

"Mashaa Allahu...Allah yakara arziki ya biya ku baki daya"

"Allahumma Aameen.... Hindu .. dama already kin gaya mun yaran ki hudu ko da sunayen su"

"Eh duk da dai ban buda sosai ba. Sunana Hindu. Mijina sunan sa junaidu. Mu mutanen yankin garin bunza ne zama ne ya dawo da mu Nan Naduka. "

"Bunza dai ta gabas?"

"Eh ita.."

"Allah sarki. Nasan bunza farin Sani. Akwai matar kawu na yar garin ce muna kanana an Sha zuwa da mu sosai ita bafulatanar ce kinsan garin naku ya Tara yarika kala kala"

"Allah sarki..eh haka nekam .donmu kan mu zuriyar tamu ta rabu gidah biyu"

"Mashaa Allahu. Tabbas kala kala qabilu kam naga harda larabawa lokacin muna kanana"

"Eh tsatson zuriyar mu ne. Larabawan. Kuma mun hada fullanci"

"Kai mashaa Allahu. Ai ina ganin ki da yaran ki nace Kai tubarkallah mashaa Allahu. Tamkar larabawa ashe ashe akwai jinin su atare daku"

Malama Hindu tayi murmushi. Hajia qibdiyya itama murmushin tayi tace,

"Ku kadai ne anan garin kenan?"

"Aa akwai yayan miji na da iyalin sa anan. Da duk ma anan din zamu zauna to Kuma sai kowanne aiki ya mayar shi wani wajen shi da iyalin sa. Allah vai amince ba sai mu biyu kawai. Mu da iyalan yayan baban yarana"

"Mashaa Allahu... "

"Tare muke da su... Gidan su na gaba da mu bamu da nisa sosai"

"Allah sarki Allah yabar zumuncin ku, Hindu ... Me yaran ki ke Kiran ki saboda yaran nan din su dinga Kiran ki da haka?"

"Ummy suke cemin"
Chapter 14 · 0% Book details