Sashe 40
Kwankwason Jimina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Duk daya suke awaje na, 'yaya na ne. Wai tsaya na tanbaye ki. Baki tunanin mutuwa ne? Bakya tunanin idan kika mutu kika bar naki yaran wa zai rike mike su? Ko gani kike ba mutuwa Zaki ba jiran duniyar zaa bar Miki eh? Idan baki sani ba duk abunda kayiwa Dan wani ko kaiwa wani na badai dai ba Allah sai anyi akan naka. Musanman maraya wallahi maraya yayi kuka akan zalun tar da kake masa na rantse da Allah Allah dai ba zai barka a haka ba. Na Miki karatun nan nayi nayi amman saboda kwakwalwar kifi ce dake Sam kinki dauka to bari kiji wallahi kin Kai ni karshe. Kinsan Allah sai anyi window a dakin nan sai dai ki hadiye zuciya ki mutum ai dan uwana ne yabaki wajen Kuma mahaifi ne agare su. "
"Sai Kuma kayi. Duk wadannan zubar maganar da kake kamar rubabbiyar bishiyar kanya ba damuna take ba kaji na gaya maka. Abunda na sani wallahi summa tallahi idan akayi window a dakin nan sai kasha mamakin abunda Zan aikata narantse da Allah sai kayi dana sanin sani na"
"Ko? Yo zan nuna Miki ni ne mijin ni ke auren ki ba kece ke aure na ba. A karkashina kike. Kina wani tunkaho kina chatting da matan manya kina hada kanki da su. To bari na tuna Miki Naduka mu zuwa mukai, Baki ne ba anan aka haife mu ba. Kuma mu ba kowan kowa bane bamuda ko sisi. A baya munyi dukiya a bunza a zuriyar mu ta hamidniyya lebanon Wanda ke bakya ciki ma. "
"Yanzu ka fito da abunda yake ranka Auwalu. Gorine Allah na tuba ba yau ka saba ba. Naji bani acikin zuriyar ku ta hamidniyya Lebanon Amman Nima nawa jinin ba matsiyata bane. Allah na tuba kuda kuka Tara dukiyar yanzu Ina fake eh? Mutum ya dinga sanin maganar da zai fada ba'
"Ke dalla can sakarya. Wadda ke bude baki waaaa tana zuba agaban yaran data haifa. Allah ya jikn Hindu a ranar da zata rasu ma sai data Miki nasiha ki kula da yaranta Amma baki daya kinyi fatali da zacen ta"
"Haba nagaji ya ishe ka haka. Hindu Hindu Hindu Hindu kullum dai ba gajiyawa"
"Hmm. Faccalanci dai ba hauka bane. Wannan rashin hankalin naki tun kina amarya na daukar faccala kamar kishiya ba Zaki sauke shi ba. Ace mace ta mutu ma Amman baki dai na kishin faccala da ita ba. Bayan ita bata zauna dake a faccala bama sai yar uwa.. Allah ya wadaran halayar kishin ki ta faccaloli datafi ta kishiya wannan hauka ne. Duk wannan tsanar da kike wa halainta daga nan ta farko. Saboda ta fiki da komai ko. Ta futo a tsatson manya tsatson mu daya sannan anmata kaya na yar manya lokacin bikin su. Sannan tanada kashin samu da yalwar arziki a komai ta kere ki shine dai kike wannan abubuwan to Allah ya kyauta. Ace ta rasu ma Amman kin cigaba da bakin kishin faccalar ki akan yaranta. Suma abin Yana bi su. Allah ya kyauta."
Nawraah da fadan su ya isheta ta jima daki ta dauki hijabi ta zura ta rike hannun Amnah zasu fita nusaiba tace,
"Kagani ko? Yanzu wannan ita zataje haka? Ni fa ban yadda da wannan yawon naki ba kina wani rike hannun Amnah."
Layla ta mike zatabi bayan Nawraah. Nusaiba ta janyo ta ta bayan rigarta ,
"Ina zakije? Ba bu inda Zaki bita. Koma ki zauna ba Zaki koyo wannan halayyar tata ba ta fita gaba gadi kullum a titi ",
Bappah junaidu daya kasa magana saboda tsananin bakin ciki kawai ya durkusa ya gyara zaman takalman sa ya shige cikin gidah
Nusaiba tabi bayan Nawraah da harara tana yatsina fuska tana gatsine gatsine .
Ko da Nawraah suka futa tsayawa tayi ajikin bango tana kife kanta hawaye ne masu dimi suka shiga zirara daga idanun ta na bakin cikin kalaman nusaiba.
"Kenan zargina take? Zargina take Ina aikata wani abun awaje kenan na haramci! Yaushe nake fita nida kullum Ina gidah? Yaa Allah kana gani Allah ka mun sakayya. Allah ka dubemu ka saka mana. "
Ta share hawayen ta ta cigaba da tafiya tana rike da hannun Amnah. Baki daya ta gama tsorota da halayen nusaiba. Ta Kuma gama yanke kundurinta kawai
"Ko guduwa zamuyi mu bar garin? To muje Ina? Ko mu rama abunda take mana mu fasa window ta karfi? Kai Yaa Allah Yaa Allah" ta karasa fada tana dafe kanta dake mata tsananin ciwo
Suna ta tafiya har zuwa Naduka crescent. Suka tsaya awani shago ta dakko nera hamsin din wajenta ta sayawa Amnah biscuit da alawa kamar Koda yaushe. Ta kan Dan fitar da ita haka su sha iska saboda dakin da suke babu window. Gidan su nusaiba Kuma da sunje shan fanka take fara hararae su. Shysa Nawraah take dan zagawa da Amnah su sha iskar Allah ta waje. Ko Amnah taji dadin jikin ta. suka cigaba da tafiya..
Tana daga Kai ta sauke akan dankareriyar jami'ar nan da akace sun samu gurbin karatu ta Al-Haramein Naduka.
Tsayawa tayi sosai tana yaba kyawu da tsaruwar ginin na makarantae. Sai kache a turai.
Manya manyan gidaje ne na masu kudi a layin harda gate dinsa layin . Ya hadu kwarai matuka layin dan Bata taba zuwa nan haka ba ta shagala tanata kallon ko'ina lungu da sako.
Kallon ta ya sauka akan tankamemen wani katon gidah an rubuta masa NADUKA GRAND ORPHANAGE PALACE a kasan Kuma an rubuta (Gidan Marayu) gidan marayun na kallon wani sugnoard da taketa tunanin a inda tasan sunan wato DR. ABUBAKHR DOLLARS DWELLING....
Zuciyarta da gangar jikinta nata ingizata ta shiga cikin katafaren gidan marayun janye da hannun Amnah. Ga mata nan Yara da manya harda Wanda ake rikewa a hannu Kuma duk marayun ne.
Ga Kuma wani bangare daga hagu can an saka wasu manyan wayoyi na karfe anyi Katanga an rufe wajen maza ne can kuma bangaren su
Da sauri ta shiga cikin reception/waiting area. Sukaga matar in charge of wajen Nawraah ta karasa ta gayshe da ita hakama Amnah
"Meke tafe daku Yan kanne na?" Matar ta tanbaye su.
Nawraah ta dan sunkuar da kai tana lankwasa Yan yatsunta tace
"Marayu ne iyayen mu sun rasu da babban wan mu. Daga ni da kanwata sai dayan yayan mu muka rage. Bamuda wani sauran gata da yarage mana. Shine Allah yasa na biyo nan yankin haka naga nan gidan marayun. Bansani ba ko kuna daukar marayu ko Yaya a abun yake?"
"Allah sarki Allah ya jikan su da ra rahama. Daga wace ungeua kukazo kenan?"
"Aameen Yaa rabbi. Daga Naduka zone muke"
"Okay to .. bakuda wasu Yan uwa ne haka da sauran su?"
Nawraah tayi shiru tana tunani. Wane yan uwan Zata ce bayan yan uwan nasu sun juya musu baya. Da su da babu su duk daya ne. Bappa Auwalu ne Kuma yayi iya yinsa, matar sa tafi karfin sa. Shi ma Kuma bashida halin da zai iya rike su, da sauri tace,
"Ba muda kowa. Duk sun rasu dama daga birnin bunza mu kazo da iyayen mu Kuma daya bayan daya cikin kankanin lokaci duk suka rasu kowanne ba rata da daya sosai "
"Allah ya rahama musu"
"Aameen yaa rabbi"
"Abunda za ai shine. Kuje kuzo da yayan naku da kayan ku kawai. Din yanzu ma ba paper da form da sauran su.."
"Toh inshaa Allah"
"Nagode sosai. , bari muje"
Nawraah ta mata sallama suka fita. Sunzo zasu wuce ta kofar signboard din gidan dazu taga wata zungureriyar mota da alama kaya ne aciki, sai wasu biyu masu matukar tsada da fara da blue hadaddun motoci, sun bi bayan babbar motar suka nufi gidan dataga signboard din DR. ABUBAKHR DOLLARS DWELLING. Motocin suka tunkari gate din da alama mutanen gidan ne sukayi tafiya suka dawo alokacin.
Tayar dayar motar bayan ta sache alokacin direban ya kasa jarasa shiga da motar gidan. Gashi sauran motocin ba dama su shiga. Motar ta tokare...
Wata kyakkyawa mata tafito daga cikin bayan motar owners corner tana gyara mayafin ta..
Bayan tafito ne wani matashin saurayi shima ya futa daga bayan moyar Yana latsa wayar hannun sa.
"Anees...." Matar takira shi da alama mahaifiyar sa ce saboda tsananin kamar da suke.
"Naam Mami"
"Yi sauri mu shiga mana. Ka tsaya. "
"To mami"
Yana biye da ita a baya suma yan sauran dayar motar suka fito daga ciki. Harda babban mutumi. Kana gani kasan mahaifin su ne. Yana tafe da waya a kunnen sa yana amsawa.
Can kuma sai ga mace da namiji suma da Nawraah take kyauta zaton Yan gidah daya ne. Saboda suna kama.
"Anees, junior meye haka kuzo mu shiga gidah mana. Ke Hayfa duba bayan mota na manta USB cord na ki dakkomin "
'Anees, Junior, Hayfa...." Nawraah ta shiga nanata sunayen su tana waywayawa baya har suka shige cikin gidan su.
Itada Nawraah suka dauki hanyar gidah a filin ball taga Ashfef Yana buga karasa ta sanar da shi duk abubuwan da akayi tundaga gidahn Bappah Auwalu da nusaiba ya zuwa gidan marayun data gani. Kan zasu koma da zama nan
Ashfeef bayi musu ba. Yayi addu'ar Allah ya zaba musu abunda yafi alkhairi idan zaman dakin tumakin ne alkhairi Allah ya zaunar da su idan kuma tashin su ne Mafi alkhairi Allah ya hada su da Mutanen kwarai
Suka koma gidah Nawraah ta fara hada musu kayan su ta gama tsaf. Asubar fari suka bar gidan suka nufi gidan marayun...
*ALHAJI SAMBASO AVENUE*
Shirye shiryen dawowar yaran Dr bintu takeyi. Kowanne da irin abincin da yake so..
Karfe hudu na yamma jirgin su ya sauka..direba yaje ya dakko su
Matashin saurayi ne mai jini a jika. Wanda mahaifiyar su Dr bintu ta nufe sy tana musu lale marhaban..
Marwan ya rungume mahaifiyar tasu Yana murmushi. Harda kunan Dadi. Lily kuwa ko ajikinta ta yi murmushi kawai tana yrigzia Kai.
:;;
..... Bappah Auwalu ya nemo su Nawraah Yana rokon su dawo kusa da shi Nawraah tace gaskia zaman su ya kare agidan nan. Yana rokon sa suna rokon sa ya kyale su
Domin dakuna ne da gado hudu a dakin gidan marayun... Kowanne daki
"Sai Kuma kayi. Duk wadannan zubar maganar da kake kamar rubabbiyar bishiyar kanya ba damuna take ba kaji na gaya maka. Abunda na sani wallahi summa tallahi idan akayi window a dakin nan sai kasha mamakin abunda Zan aikata narantse da Allah sai kayi dana sanin sani na"
"Ko? Yo zan nuna Miki ni ne mijin ni ke auren ki ba kece ke aure na ba. A karkashina kike. Kina wani tunkaho kina chatting da matan manya kina hada kanki da su. To bari na tuna Miki Naduka mu zuwa mukai, Baki ne ba anan aka haife mu ba. Kuma mu ba kowan kowa bane bamuda ko sisi. A baya munyi dukiya a bunza a zuriyar mu ta hamidniyya lebanon Wanda ke bakya ciki ma. "
"Yanzu ka fito da abunda yake ranka Auwalu. Gorine Allah na tuba ba yau ka saba ba. Naji bani acikin zuriyar ku ta hamidniyya Lebanon Amman Nima nawa jinin ba matsiyata bane. Allah na tuba kuda kuka Tara dukiyar yanzu Ina fake eh? Mutum ya dinga sanin maganar da zai fada ba'
"Ke dalla can sakarya. Wadda ke bude baki waaaa tana zuba agaban yaran data haifa. Allah ya jikn Hindu a ranar da zata rasu ma sai data Miki nasiha ki kula da yaranta Amma baki daya kinyi fatali da zacen ta"
"Haba nagaji ya ishe ka haka. Hindu Hindu Hindu Hindu kullum dai ba gajiyawa"
"Hmm. Faccalanci dai ba hauka bane. Wannan rashin hankalin naki tun kina amarya na daukar faccala kamar kishiya ba Zaki sauke shi ba. Ace mace ta mutu ma Amman baki dai na kishin faccala da ita ba. Bayan ita bata zauna dake a faccala bama sai yar uwa.. Allah ya wadaran halayar kishin ki ta faccaloli datafi ta kishiya wannan hauka ne. Duk wannan tsanar da kike wa halainta daga nan ta farko. Saboda ta fiki da komai ko. Ta futo a tsatson manya tsatson mu daya sannan anmata kaya na yar manya lokacin bikin su. Sannan tanada kashin samu da yalwar arziki a komai ta kere ki shine dai kike wannan abubuwan to Allah ya kyauta. Ace ta rasu ma Amman kin cigaba da bakin kishin faccalar ki akan yaranta. Suma abin Yana bi su. Allah ya kyauta."
Nawraah da fadan su ya isheta ta jima daki ta dauki hijabi ta zura ta rike hannun Amnah zasu fita nusaiba tace,
"Kagani ko? Yanzu wannan ita zataje haka? Ni fa ban yadda da wannan yawon naki ba kina wani rike hannun Amnah."
Layla ta mike zatabi bayan Nawraah. Nusaiba ta janyo ta ta bayan rigarta ,
"Ina zakije? Ba bu inda Zaki bita. Koma ki zauna ba Zaki koyo wannan halayyar tata ba ta fita gaba gadi kullum a titi ",
Bappah junaidu daya kasa magana saboda tsananin bakin ciki kawai ya durkusa ya gyara zaman takalman sa ya shige cikin gidah
Nusaiba tabi bayan Nawraah da harara tana yatsina fuska tana gatsine gatsine .
Ko da Nawraah suka futa tsayawa tayi ajikin bango tana kife kanta hawaye ne masu dimi suka shiga zirara daga idanun ta na bakin cikin kalaman nusaiba.
"Kenan zargina take? Zargina take Ina aikata wani abun awaje kenan na haramci! Yaushe nake fita nida kullum Ina gidah? Yaa Allah kana gani Allah ka mun sakayya. Allah ka dubemu ka saka mana. "
Ta share hawayen ta ta cigaba da tafiya tana rike da hannun Amnah. Baki daya ta gama tsorota da halayen nusaiba. Ta Kuma gama yanke kundurinta kawai
"Ko guduwa zamuyi mu bar garin? To muje Ina? Ko mu rama abunda take mana mu fasa window ta karfi? Kai Yaa Allah Yaa Allah" ta karasa fada tana dafe kanta dake mata tsananin ciwo
Suna ta tafiya har zuwa Naduka crescent. Suka tsaya awani shago ta dakko nera hamsin din wajenta ta sayawa Amnah biscuit da alawa kamar Koda yaushe. Ta kan Dan fitar da ita haka su sha iska saboda dakin da suke babu window. Gidan su nusaiba Kuma da sunje shan fanka take fara hararae su. Shysa Nawraah take dan zagawa da Amnah su sha iskar Allah ta waje. Ko Amnah taji dadin jikin ta. suka cigaba da tafiya..
Tana daga Kai ta sauke akan dankareriyar jami'ar nan da akace sun samu gurbin karatu ta Al-Haramein Naduka.
Tsayawa tayi sosai tana yaba kyawu da tsaruwar ginin na makarantae. Sai kache a turai.
Manya manyan gidaje ne na masu kudi a layin harda gate dinsa layin . Ya hadu kwarai matuka layin dan Bata taba zuwa nan haka ba ta shagala tanata kallon ko'ina lungu da sako.
Kallon ta ya sauka akan tankamemen wani katon gidah an rubuta masa NADUKA GRAND ORPHANAGE PALACE a kasan Kuma an rubuta (Gidan Marayu) gidan marayun na kallon wani sugnoard da taketa tunanin a inda tasan sunan wato DR. ABUBAKHR DOLLARS DWELLING....
Zuciyarta da gangar jikinta nata ingizata ta shiga cikin katafaren gidan marayun janye da hannun Amnah. Ga mata nan Yara da manya harda Wanda ake rikewa a hannu Kuma duk marayun ne.
Ga Kuma wani bangare daga hagu can an saka wasu manyan wayoyi na karfe anyi Katanga an rufe wajen maza ne can kuma bangaren su
Da sauri ta shiga cikin reception/waiting area. Sukaga matar in charge of wajen Nawraah ta karasa ta gayshe da ita hakama Amnah
"Meke tafe daku Yan kanne na?" Matar ta tanbaye su.
Nawraah ta dan sunkuar da kai tana lankwasa Yan yatsunta tace
"Marayu ne iyayen mu sun rasu da babban wan mu. Daga ni da kanwata sai dayan yayan mu muka rage. Bamuda wani sauran gata da yarage mana. Shine Allah yasa na biyo nan yankin haka naga nan gidan marayun. Bansani ba ko kuna daukar marayu ko Yaya a abun yake?"
"Allah sarki Allah ya jikan su da ra rahama. Daga wace ungeua kukazo kenan?"
"Aameen Yaa rabbi. Daga Naduka zone muke"
"Okay to .. bakuda wasu Yan uwa ne haka da sauran su?"
Nawraah tayi shiru tana tunani. Wane yan uwan Zata ce bayan yan uwan nasu sun juya musu baya. Da su da babu su duk daya ne. Bappa Auwalu ne Kuma yayi iya yinsa, matar sa tafi karfin sa. Shi ma Kuma bashida halin da zai iya rike su, da sauri tace,
"Ba muda kowa. Duk sun rasu dama daga birnin bunza mu kazo da iyayen mu Kuma daya bayan daya cikin kankanin lokaci duk suka rasu kowanne ba rata da daya sosai "
"Allah ya rahama musu"
"Aameen yaa rabbi"
"Abunda za ai shine. Kuje kuzo da yayan naku da kayan ku kawai. Din yanzu ma ba paper da form da sauran su.."
"Toh inshaa Allah"
"Nagode sosai. , bari muje"
Nawraah ta mata sallama suka fita. Sunzo zasu wuce ta kofar signboard din gidan dazu taga wata zungureriyar mota da alama kaya ne aciki, sai wasu biyu masu matukar tsada da fara da blue hadaddun motoci, sun bi bayan babbar motar suka nufi gidan dataga signboard din DR. ABUBAKHR DOLLARS DWELLING. Motocin suka tunkari gate din da alama mutanen gidan ne sukayi tafiya suka dawo alokacin.
Tayar dayar motar bayan ta sache alokacin direban ya kasa jarasa shiga da motar gidan. Gashi sauran motocin ba dama su shiga. Motar ta tokare...
Wata kyakkyawa mata tafito daga cikin bayan motar owners corner tana gyara mayafin ta..
Bayan tafito ne wani matashin saurayi shima ya futa daga bayan moyar Yana latsa wayar hannun sa.
"Anees...." Matar takira shi da alama mahaifiyar sa ce saboda tsananin kamar da suke.
"Naam Mami"
"Yi sauri mu shiga mana. Ka tsaya. "
"To mami"
Yana biye da ita a baya suma yan sauran dayar motar suka fito daga ciki. Harda babban mutumi. Kana gani kasan mahaifin su ne. Yana tafe da waya a kunnen sa yana amsawa.
Can kuma sai ga mace da namiji suma da Nawraah take kyauta zaton Yan gidah daya ne. Saboda suna kama.
"Anees, junior meye haka kuzo mu shiga gidah mana. Ke Hayfa duba bayan mota na manta USB cord na ki dakkomin "
'Anees, Junior, Hayfa...." Nawraah ta shiga nanata sunayen su tana waywayawa baya har suka shige cikin gidan su.
Itada Nawraah suka dauki hanyar gidah a filin ball taga Ashfef Yana buga karasa ta sanar da shi duk abubuwan da akayi tundaga gidahn Bappah Auwalu da nusaiba ya zuwa gidan marayun data gani. Kan zasu koma da zama nan
Ashfeef bayi musu ba. Yayi addu'ar Allah ya zaba musu abunda yafi alkhairi idan zaman dakin tumakin ne alkhairi Allah ya zaunar da su idan kuma tashin su ne Mafi alkhairi Allah ya hada su da Mutanen kwarai
Suka koma gidah Nawraah ta fara hada musu kayan su ta gama tsaf. Asubar fari suka bar gidan suka nufi gidan marayun...
*ALHAJI SAMBASO AVENUE*
Shirye shiryen dawowar yaran Dr bintu takeyi. Kowanne da irin abincin da yake so..
Karfe hudu na yamma jirgin su ya sauka..direba yaje ya dakko su
Matashin saurayi ne mai jini a jika. Wanda mahaifiyar su Dr bintu ta nufe sy tana musu lale marhaban..
Marwan ya rungume mahaifiyar tasu Yana murmushi. Harda kunan Dadi. Lily kuwa ko ajikinta ta yi murmushi kawai tana yrigzia Kai.
:;;
..... Bappah Auwalu ya nemo su Nawraah Yana rokon su dawo kusa da shi Nawraah tace gaskia zaman su ya kare agidan nan. Yana rokon sa suna rokon sa ya kyale su
Domin dakuna ne da gado hudu a dakin gidan marayun... Kowanne daki