← Book details Ƙarfe Daya Ba Ya Amo Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 42 OF 42

Sashe 42

Ƙarfe Daya Ba Ya Amo Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

A hankali ya ɗan motsa wani azaba da raɗaɗi da bai taɓa jin irinsa ba na ziyartarsa amma yanayin da ya ke ciki ya sa dole ya buɗe idanunsa, hasken rana ne irin na safiyar nan dake fita tarrr ya shige mishi idanu da ya sa yayi saurin rufe wa saboda zafi da ya ziyarcesa kan ya sake tattare ɗan ƙarfin da ya rage masa ya buɗe idanunsan da suka sauya kwarai.

A kan gefen cikinsa da yake jin azabar ta fi yawa ya sauƙe idanunsa yana tunano abin da ya faru a jiyan, tabbas wani abu aka bashi a cikin shayin da ya sha amma ba zai ce ko abin bugarwa ba ce ko guba amma ya san ya fice a hayyacinshi, kan Wuƙa ne kuma a jikinshi jini ya lalata duka ɓangaren farar jallabiyarsa ta sauya zuwa ja.

Ya runtse idanun a hankali ya sake bude wa kan ya juya kanshi zuwa gefen kafadarsa da yake jin nauyi idanunsa suka sauka kan gashinta da ya wargaje ya rufe mata fuska gabadaya, hannunta na cikin nasa ɗaya kuma kanta na kwance a kan kafaɗarsa dayan hannunta na riƙe da cikinta.

Sai a lokacin ya tuna a jiyan ya ganta kamar almara, ya tuna yadda take rikesa take kuma jansa don tseratar da rayuwarsa, ya tuna yadda take kara masa karfin gwiwar yayi gudu idan suka riskesu ita kaÉ—ai ba za ta iya ba!

Hannu ya sa a kanshi ya cire Ghutra dinshi da har lokacin yana kanshi ya saka mata yana rufe mata gashin, motsin da yayi ya farkar da ita sai idanunsa suka sauka kan jinin da duk ya bata jikinta, idanunsa ya tsayar a kai kan ya kawar ya mayar kan wuƙar jikinshi ya na kokarin taɓawa tayi carab ta kama hannunsa.

"Kana motsa wannan wuƙar ko ka cireta babu abin da zai hanaka mutuwa! A jiyan ma da sun zare da yanzu wani maganar ake ba wannan ba!"

Ta faɗa chan ƙasa yanayinta babu ƙarfi sammm Idanunta suna ta lumshewa, hayaniya suka soma ji kaman mutane sai kuma suka ji ana ta kwalla kiran sunanshi don wuri ne uncompleted buildings na dayawa cikin ɗaya daga ciki suke, ta miƙe da kyar ya sake kallon jikinta amma bakinshi ya kasa furta komai ta riƙe shi ya miƙe suka fito daga nesa suke hangen motoci da hukumomi ana ta cigiyarsa! Sai da suka fito sarari har wasu sun gansu kan ta sake shi ko kan yayi magana ta juya ta bar wurin yayi ƙasa a daidai nan aka janyo hankalin su Ammar

"Ga shi chan! Ga Sheikh chann!!"

Kan ka ce kwabo an rufu mishi aka É—auke shi Ammar na ta kiran sunanshi amma bai buÉ—e idanu ba aka sanyashi a ambulance sai asibiti.

Tashin hankali karamin suna ne da za'a ƙira halin da ahalin Familyn suka shiga don a daren da abin ya faru yayi munin da ko ina maganan ya baza Malam Bala yana coma, Imam na kwance asibiti sai kuma ga labarin an kama Abbiey an kuma rufe companynsa don ana zarginsa da safarar miyagun kwayoyi da sunan Company!

Ammar ya rasa inda zai sa kanshi shi da Abba dole Abba ya tsaya wurin hukuma shi kuma Ammar ya bi ayarin masu neman Shehi don Imam ya tabbatar musu mutanen basu kashe shi ba ya gudu sun neme shi sun rasa a kan idanunsa komai ya faru kuma Shehi ba zai iya nisa ba saboda raunin da suka ji masa!

Surgery kai tsaye aka shiga da shi don wukar a ƙasan cikinsa ne, Ammiey kam ta fice hayyacinta Maamah da su Daddah sun yi kuka har sun rasa hawaye a iya jiya rayuwarsu na neman juyewa daga sama zuwa ƙasa!

Neman faɗuwa Ammar ke yi a sadda yake jin wasu kalamai da suka girmi tunaninsa cikin TikTok da mutumin gefensa ke kallo zaune cikin reception na asibitin da Shehi yake, da sauri ya kalli su Maamah tabbas su ma sun ji don Tuni sun miƙe tsaye!

Girgiza kai tayi ta isa ga mutumin ta fusge wayan tana kallo tana girgiza kai Idanunta na tsiyayar da kwalla!

"Tabbas 'yata ta dawo gida amma cikin wani mummunan yanayi, daga taimakon wannan babban Malamin Sheikh Irshad Al-Noor Kasancewar ba ya hayyacinsa ya yi Mata FYADE! Hotunan dake zagayawa ba ƙarya ba ne!"

Bugawa ne ya saura zuciyoyinsu basu yi ba, scrolling hannun Maamah yayi sai ga hoton Irshad ɗin riƙe a jikin Diva jikinta akwai jini kaman yadda nashi yake da jini, basu san daga ina ya fita ko wa ya ɗauka ba amma tabbas a safiyar ne kuma media ta ɗauki dumi dama kiris ake jira nan Scandal ya fara Shehi ya yi wa wata 'yar Daba fyade daga taimako!

Abu ne da hankali ba zai taɓa ɗauka ba amma sanin Imam ya ce musu kaman tun farko Shehi ba ya cikin hankalinsa don tabbas akwai abin da ya shiga kansa a lokacin don har hana shi sauƙa yayi amma yadda yake abu kaman cikin maye ya tsinka musu gaba! Tabbas idan wani abun maye ne aka shayar da shi zai iya aikata hakan ba tare da ko ya sani ba Innalillahi wainna ilaihi raji'un...!!!!!

*Toh jama'a anan muka kawo ƙarshen free pages za mu tafi hutun kwanaki, da yardar Allah bayan kwana goma za mu dawo muku da cigaban wannan labari!

Idan har Shehi ya aikata fyade wa Diva me kuke tunanin zai faru? Zai ma rayu kuwa? Me ya haɗa Abba da Safarar kwayoyi? Zubaidah kuna ganin mahaifiyarta za ta cigaba da cin galabar tarwatsa rayuwarta? Ma'u na hannun NAPTIP Jiddah na hannun J shin waye ne ma J ɗin? Iyayensu za su samesu kuwa ko sun tafi kenan? Kuna tunanin Dagaci da ya kama gomnati ya kama dahir kuwa a taimakon al'umma? Menene Jagaban ke ɓoyewa? Waye ke sace kudin company kuma yake ɗora wa Ammar? Diva za ta shiryu kuwa? Waye yake neman ran Shehi??
Ko anan muka tsaya na san kun fahimci wannan kalma ta ƙarfe ɗaya ba ya amo dole sai ya haɗu da wani ƙarfen ɗan uwansa!

Hmmm akwai fah sauran tafiya a gaba ku dai ku gyara zama kawai ku mu cigaba da tafiya*

Trio of tales za su zo muku cikin farashi mai sauƙi....

DAÆŠIN ZAMA BY SEEMAHWRITES
JODA BY SADI-SAKHNA
ƘARFE ƊAYA BA YA AMO BY GUREENJOH

*A whatsapp
One 1k
Two 1800
Three 2400*

*Telegram
One 700
Two 1200
Three 1500*

Account details
0545475847
Gt bank
Fatima Muhammad Gurin

Sai a tura shaidar biya ta
09039206763

🖤Gureenjoh🖤
Chapter 42 · 0% Book details