← Book details Joy Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 45 OF 46

Sashe 45

Joy Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da misalin karfe biyar na yamma yaro ya yi sallama, tsakar gidan Ummi ya sanar da ita wai wani mutum na sallama da ita a waje, a lokacin ita kadai ce a gidan Fatima na islamiyya Al'ameen kuma na gurin sana'arsa, cike da madaukakin mamaki, ta ce "Balkisu aka ce ka kira ko dai Fatima." Yaron ya tabbatar mata da Balkisu ake kira, har ta ce ya je ya ce wanene, sai kuma ta ce ya barshi, ya ce wa mutumin ya shigo daure ya kirata tana zuwa, ta dade zaune tana sake-sake , kamar ta fasa fitar don hankalinta bai kwanta ba sai dai ta dake ta mike ta sanya hijab dinta ta fitan........

Oum ummeetarh
09116099486
[12/29, 2:50 PM] AyshaNalado: 🌀🌀 *JOY* 🌀🌀

~FARHAT~

*PAGE 43*

Mikiya Writers Association

*Masu facebook ku yi following wannan account ɗin domin samun damar cin giveaway ɗin da muke yi, da kuma tattaunawa akan yanayin rayuwa*

https://www.facebook.com/naeemerh.suleiman?mibextid=ZbWKwL

“A'uzu billahi minashshaidanir rajim” Ummi ta furta lokacin da ta yi arba da ba‘kar fuskar Tanimu a matsayin wanda ke sallama da ita. Dakatawa ta yi daga bakin k'ofa ta kasa k'arasowa cikin zauren, sai bin shi take yi da wani irin mugun kallo, mai cike da tsana tsaba. Zuciyarta cike take fal da tsoro, amma a zahiri sam babu alamar hakan a kan fuskarta. Shu'umar murmushinsa ya saki yana jan dogon gemunsa yana binta da wani kallo, irin ta gogaggun y'an duniya tare da ce mata "K'araso mana Balkisu mai gadon zinare, Alheri ne ke tafe sa ni, na canza shawara domin daren jiya na kasa barci kyakkyawar surarki ce ta dinga yi mini gizo zuciyata ta sake kwadaituwa da son tarawa da ke, yayinda gangar jikina ke sake fallasa mini muradinta na son yin nitso a kogon ni'imarki, shine
na ji a raina gara na zo mu sasanta, idan hagu ta ki sai a koma dama ko na haka ba yar shilata." Ya karashe maganar yana fitar da wata sautin murmushi mai cike da zallar iskanci.

Had'e girar sama da ta k'asa ta yi babu alamaun fara'a ko sassaci ko miskala zarratin a fuskarta, ta ce "Ta Allah ba taka ba mugu fasiki dan Akuya, da yardar Allah baza ka ta6a cin galaba a kaina ba, baza ka ta6a cimma mummunar nufinka a kaina ba har lokacina ya cika na bi bayan mijina, kuma ka fita kabar mini gidana bana bukatar taimakon daga wajenka ko wani naka, Allah da na rike zai kawo wanda zai tallafa mana." Takowa ya shiga yi gareta yana fadin "Haba mana balkisu, ya zaki yi mini haka, wannan harkar fa cudanni in cudeka ne, kan ki kawai zaki mallaka min na rana d'aya, ni kuma na jiyar take dad'in da babu wani namijin da ya ta6a jiyar take irinsa a duniya, tun daga kan kwaratanki har zuwa kan mataccen mjinki, iye yan mata kar ki yi mani rowa mana, nasan ai kema kina da muradi." Ya karashe maganar yana kokarin kai hannusa jikinta.

Da sauri ta ja baya hankali tashe take fad'in "Tanimu kar ka ta6a ni, ka fitar mini daga gida ni ba fasika bace irinka." Dariya ya kece da shi, ya ce "to muje cikin gidan mana ai nasan babu kowa daga ni sai ke sai Allah, kinga sai na cika tsohon muradina a kan ki ko ta karfi ne." Yana maganar yana dariya.

Jin hakan ya matukar daga mata hankali, take ta sake k'amk'ame hijabinta tana sake ja da baya, yayinda shi kuma ya ci gaba da biyota har suka shiga cikin gidan.
Zuciyarta ta dinga bata shawarwari shin ta juya ta runtuma da gudu ne zuwa dakinta ta datse kofa ko kuma ta nemi makami ta illata shi ko kuma dai ihu zata yi mashi.

Kamar ya shiga zuciyarta ya ga abinda take kitsawa sai ji ta yi yana cewa " Kina tunanin yi mini ihu ko? To bismillah, idan kika yi mini ihu na rantse miki da Allah k'aik'ayi ne zai koma kan mashek'iya don sai kin gwammace mutuwa da irin Sharrin da zan kulla miki."

"Mugu azzalumi dan Akuya Allah ya fika." Murmushi ya yi ya ja gemunsa ya ce "Balkisu taurin kai! Ni wallahi ko a yanzu kika bani kan ki na minti ashirin na miki Alkawarin a yau zan je na nemawa dan ki aure kuma na tsaya masa babu wanda zai san shege ne balle ayi masa gori, ba sai munje da nisa ba a tsakar gidan nan ma sai mu yi mu ta shi don ni ba bakon zafi bane." Ya fad'a yana murmushi tare da bin tsakar gidan da kallo.

Wannan kalle kallen daya tafi ne ya bata damar zarar wuka a jikin rufin din kitchen Inda suke ajiyewa, cikin zafin nama ta kai mishi yanka cike da shammata, da sauri ya saka hannu sa ya tare yankan hakan yaba wukar damar yankarsa a tafin hannu mugun yanka kuwa, take jini ya balle, razananniyar kara ya saki tare da rike hannun, tuni idanunsa sun kada sunyi jajur, rigar jikinsa tuni jini ya bata shi kaca-kaca.

Ganin yadda mini ke zirara kamar an yanka karamin dabba yasa jikin Ummi ya fara karkarwa take ta sake wukar dake hannunta, don ta tsorata ainun, tunda ta taso ita mai taushin zuciya ce ko kiyashi bata kashewa da gangan balle ace wai yau ita ce ta yanki mutum da wuka haka jina na zuba, hakan ya tayar Maya da hankalin ainun.

Bata yi aune ba taji ya shaki wuyar hijabinta tare da hed'e ta da bango kafin ya shiga wanka mata mari a fuskarta, karfi ya saka ya yage hijabinta jikinta ya damk'i wuyarta ya shake, a zuciye cikin zaro jajayen idanunsa yake cewa " Ni zaki jiwa ciwo! Ni za ki yi wa lahani! Wato don kinga ina bin ki ina da lalla6a ki ko, to bari na turmushe ki ta karfi da ya ji muga ta tsiya." Yana maganar ne cikin fitar hayyaci da tsananin fusata, yayinda ya shiga kokarin keta dogon rigar atamfar dake kijinta.

Babu zato wani irin wawan naushi ya sauka a gefe fuskasa wanda sai da jini ya yi tsartuwa daga bakinsa ya famtsama a fuskar Ummi, babu shiri ya sake ta tare da tallafe gefen fuskarsa ya furzar da miyan bakinsa mai gauraye da jini, saiga hakora uku turame sun biyo.

Kafin ya gama tantance meya faru, Al'ameen ya yi wa wuyarsa wata irin muguwar shaka, idanunsa a waje cikin tsananin fusata ya shiga dukansa ba tare da ya tsaya tantance wanene ba.

Cikin yan dak'ikai ya hada mishi mi shi jini da majina, nan ya zube kasa warwas kamar gawar sababi, bai bar shi ba ya zauna a ruwan cikinsa ya ci gaba da duka yana fadin "Mahaifiyata, Uwata ita za ka yi wa fyad'e kai waye, wallahi wallahi, sai na kashe ka, ni Muhammadul-Ameen yau sai an kashe ka."

Jin shirun Al'ameen ya yi yawa yasa Aliyu dake jiransa a kofar gidan ya miko masa sak'o, ya gaza hakuri ya kutso kai cikin gidan, tun daga Zaure ya fara jiyo sambatun Ameen hakan yasa ya k'arasa cikin gidan a guje, abinda ya tarar ne ya saka shi zare ido tare da runtumawa da gudu ya shiga kokarin bambare hannun Al'ameen a wuyar mutumin da yake duka kamar Allah ya aiko shiz sun yi kokawa sosai kafin ya samu nasarar daga shi daga kan mutumin.

Jijjigashi Aliyu ya shiga yi , yana fad'in" Ameen menene haka ka dawo cikin hayyacin mana." Sam Al'ameen ba ya jinsa, sai yunkurin kwacewa ya ke daga rikon da Aliyu ya yi masa yana kokarin sake kaiwa Yaya babba cafka, ganin haka yasa Yaya babba mikewa a daddafe ya fece daga gidan ba tare da ya tsaya ko neman takalmansa ba.

"Ka sake ni Aliyu, wallahi sai na kashe shi , bazan barshi ba, sai na raba shi da numfashin sa." A tsawace Aliyu yace "Ka nutsu Ameen, ka kalli halin da Ummi ke ciki."

Jin haka yasa shi saurin juyawa gareta, a kwance take sharaf a kasa kamar bata numfashi, da wani irin sauri ya karasa gareta ya dagota yana jijjigata tare da kiran sunanta, da kyar ta bud'e idanunta dake lumshewa ta kalle shi a kan la66anta ta furta "Ka kula da Fatima Ameen na bar maka ita amana nasan za ka iya.... Bata karkareba idanunta suka lumshe numfashita ya dauke cak! " Ummi!!!!!!!! Ya ambata da Iya dukkan karar muryarsa..............

Kunfa rage comment mutanen Joy😬

Oum ummeertah
09116099486
[12/29, 2:51 PM] AyshaNalado: 🌀🌀 *JOY* 🌀🌀

~FARHAT~

*PAGE 44*

Mikiya Writer's Association

Cike da tsananin tashin hankali Al'ameen ke safa da marwa a bakin d'akin bada agajin gaggawa na karamar asibitin dake unguwarsu, in da suka yi gaggawar kai Ummi bayan sun fahimci suma ta yi ba mutuwa ba, tunda suka kai ta kimanin awa hudu a tsaye yake kamar mashi, a k'ofar d'akin sallar magriba da ishsha ne kadai ya kau da shi daga wajen, Fatima na zaune a kan d'aya daga cikin bencinan da a ka tanada domin zama, sai kuka take yi idanunta sun kumbura sun yi jajur, dawowarta daga hadda ta tarar da wannan tashin hankalin ko gida bata kai ga shiga ba ta ga an fito da Umminta a sume kamar gawa, hakan ya daga mata hankali, a guje ta kutsa kai cikin napep din da aka sanya Ummi ta kamkameta tana kuka, tun lokacin take rusar kuka har zuwa yanzu da ake neman karfe goman dare. Yau dai kam kasa rarrashinta Al'ameen ya yi, Aliyu da Maman Amira wacce ta biyo su asibitin daga baya ne suke kokarin bata baki idan suka ga kukan nata ya yi yawa.
Chapter 45 · 0% Book details