Sashe 3
Hamdah Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zaman sa ya gyara kana yasoma sanar musu duk abun da baba Mai gadi da Habu mai shara da Sani direver suka sanar masa, kana ya É—aura da ganin da Na'ima tace tayi mana a kan gado da wan da Habu shima yace yagani.
salati parlour'n ya kaure da shi tuni hawaye yashiga wanke fuskar Ummi,
cikin takai ci Abba ya dube ni yana faÉ—in
"Abun da zaki saka mana da shi kenan ki ɓata mana family kin tozarta shi tozarci mafi muni me kika nema kika rasa a rayu HAMDAH me muka gaza miki wacce gatace bamu baki ba sakayyar da zaki yi mana kenan!".
kai narika girgizawa hawaye na zuba a idona na buÉ—e baki zanyi magana Abba ya daka min tsawa.
kana ya dubi Ya SALEEM yace
"Tashi ka kaje hukuncin da ka yanke shine dai-dai ta haramta a gare ka kuwa tabbas".
a sannu ya mike yafita da sauri na mike tsaye kamar mai tashin aljanu na bi bayan sa kafin na iso shi har ya isa farfajiyar gida da gudu nasha gaban san sa na ruko hannunsa na É—aura kan cikina cikin muryar kuka da fizgar numfashi na da nake ji kamar zai É—auke, ina kallon fuskarsa nace
"Ya SALEEM Ya SALEEM wlh abun da ke cikin kinan nan naka ne kai ne uban sa, wlh babu wani na mijin da ya taɓa rike koda bakin mayafi nane bare har ya sanni ƴa mace bayan kai Ya SALEEM ɗan kane cikin kane wlh babu wani wan da yake zuwa guri na".
fizge hannunsa yayi kana ya dube ni da kyau yace
"Kada ki sake dan ganta abun da ke cikin ki da Ni ni ba uban sa bane, ke kinsan uban sa ai jeki haifa ki kai masa abunsa in yaso ki kashe shi tun a ciki tun kafin ya fito duniya a san halin da kike ciki, asan wacece ke mutum a fuska kawai,
In dai irin wannan É—an ne zai zamo nawa har abada bana so!".
yana kaiwa nan ya juya yashige motar sa yafice a gidan..
Dur kushewa nayi a gurin ina wani irin kuka mai tsuma rai, na daÉ—e durkushe jin jiri na fisgata na mike da kyar na koma parlour in da su Ummi suke har lokacin Ummi na hawaye sai dai ta kasa furta ko da kalma É—aya ce, goggo Hauwa da Aunty Halima sunyi jugum.
ina saka kafata cikin parlour'n Abba ya takatar da ni da faÉ—in
"Kada ki sake ki tako cikin parlour'n nan maza ki tafi kiyi nesa da mu domin zama da irin ki acikin family tamkar rugujewar ahali ce,
kisani idan zuciya ta tabuga to kece sila kuma bazan taɓa yafe miki ba,bana kaunar nakuma buɗe idanuna na ganki fita min a gida kitafi duk inda zakije amma ki sani ban yarda kije gidan ɗaya daga cikin dangi naba har in dangi nane fita min a gida nace!".
yafaÉ—a cikin karaji baya nashiga ja inajin maganar Abba tamkar saukar ruwan dalma a zuciya ta.
mikewa Ummi tayi hawaye taf idon ta tace
"Ina zataje Abba'n Fauzan ka bata lasisin shiga duniya kenan? bata da in da yafi nan in kuma kace ta tafi to sai dai mutafi tare".
Ummi ta nufo ni tana cigaba da faÉ—in
"ÆŠiyar ka mace zaka jefawa duniya sai dai in mutafi tare".
cikin fushi Abba yace
"Fatima idan kika fita daga cikin parlour'n nan to ki tabbata nayafe ki".
ido na waro cikin tsananin tashin hankali nashiga girgiza kai da karfi nace
"Ummi dan Allah dan Allah karki fita Ummi ki koma na rokeki Abba kayi hakuri ni zan tafi".
ganin tana ta daÉ—a matsoni yasani tahowa da gudu na rungume ta cikin muryar kuka nacigaba da faÉ—in
"Ummi ki koma dan Allah karki fita".
sai kuma na zame jikina da sauri na saka hannuna biyu na share hawaye na nakuma kai hannu kan fuskar ta nashare mata hawaye tare da yin wani murmushi ina duban ta yayin da wasu zafafan hawaye suka zubo min nace
"Ummi duk inda nake a faɗin duniyar nan ko a muce ko a raye addu'ar ki itace zata zame min garkuwa in nazamo silar fitar ki a gidan nan bazan taɓa yafewa kai na ba".
Najuya na dubi su goggo Hauwa da tuni suma hawaye yagama wanke musu fuska na haÉ—e hannaye na biyu nace
"Dan Allah goggo Hauwa Aunty Halima kada kubar Ummi na ta fita dan Allah".
da sauri na juya nafita a cikin parlour'n na É—au jakata dana yar dashi a tsakar gidan da sauri na nufi kofar fita ina waige ko Ummi na biyo ni.
sauri na rika yi har na fita daga layin mu.......!★
Mommyn twins ce
Sauri nake kamar zan tashi sama duk da nafita daga layin unguwar amma hankali na bai kwanta ba,tafiyar nake ina ta waige-waige,sai gani nake kamar Ummi zata biyo ni.
tafiyar kawai nake batare da nasan in da zani ba kokuma sanin in da na nufa ba.
Karar ababen hawa da naji ya karaÉ—e ko ta ina shine ya dawo dani cikin hayyaci na,nayi mamakin ganin in da nake
Duk da kuwa tazarar dake sakanin unguwar mu da in da nake yanzu
wato winte.
Gefen titi na zame nashiga cikin mutanen da nagansu zazzau ne kan bence wasu ko nata harkokin gaban su.yayin da zuciya ta keta azalzala ta ji nake idan naci gaba da jan numfashi acikin garinnan tabbas zuwa anjima numfashi'n kwacewa zaiyi yatafi abun sa.
maganar da naji kusa da nine yasani É—agowa wani É—an yuniyon ne tsaye a kanmu yana faÉ—in
"Yauwa motar ku yanzu kam yacika kowa ya kawo kuÉ—in sa".
gafen da nake ya kalla kana yace
"Ƴan mata ke ma a wannan motar kike?".
tsintar kaina nayi da gyaÉ—a masa kai,yace
"To kawo kuÉ—in ki mota ta cika".
idanuna na mai da kan akwatin da ke gaba na tabbas nasan bana da ko sisi dan ban fita da ko biyar daga gida ba, hasali ma babu abun da na iya É—auka in ba wannan akwatin ba,ganin yanata amsar kuÉ—in mutane sai na kai hannuna kan zip É—in bayan akwatin ina É—an wasa da shi a raina nake faÉ—in
"To ko ince masa yakarɓi akwatin a bakin kuɗin motar ne, Ni har da kayan cikin ma in dai zasu ɗauke Ni suraba ni da garin nan".
yadda nake wasa da zip É—in sai yana É—an zugewa da mamaki nakurawa aljuhun jakar ido ganin bakin kuÉ—i ya baiyana, da sauri na idda zuge zip É—in nazaro kuÉ—in ina juyashi a hannuna naira dubu biyu sabbi dar.
tunanin ta yadda akayi kuÉ—in yashigo cikin a kwatin nake,
nan take na tuno lokacin rasuwar Inna ina zaune a cikin bedroom É—in Ummi taciro kuÉ—i cikin wardrobe zatayi aika kasuwa daga cikin kuÉ—aÉ—en dubu biyu suka zubo,nakwashe ina mika mata tafita da sauri tana faÉ—in na ajiye bari tazo,a lokacin kuwa kasan cewar ina zaune ne kusa da akwatin sai naja zip É—in a kwatin nasaka ciki kan cewar in tashigo zan cire na bata,gaba É—aya nagama mance wa a she dai ban bata ba..
Numfashi na sauke a hankali na furta
"Alhamdulillah".
dai-dai lokacin kuwa É—an yuniyon É—in yake faÉ—in
"Kawo nake".
duka kuÉ—in na mika masa sai naga ya zare dubu É—aya yakai hannu aljuhu yazaro É—ari biyu sai ya haÉ—a da dubu É—ayan nan ya mika min dubu É—aya da É—ari biyu kenan.
karɓa nayi ina juya kuɗin a hannuna "Wato kuɗin motar garin da zasu ɗari takwas kenan?".
nayi tan bayar a raina,
ganin duk wan da yabada kuÉ—i sai ya shige cikin motar dake gaban mu sai nima na mike nashige cikin motar ina rungume da akwatina.
Ina alla-alla motar ta tashi duk da kuwa bansan motar wani gari zata ba ban kuma da mu da duk inda zaije ba ni dai burina nafita a cikin garin nan, bana kaunar na buÉ—e idanuna nakuma ganina cikin garin bana kaunar narika shakar iskar garin naji na tsani garin gaba É—ayan ta.
numfashi na sauke tare da yin hamdala lokacin da motar ta hau kan titin taɗau hanyar fita daga cikin garin......★
★★★
A nan cikin garin Bauchi kuwa,
kan kace me labarin abun da ya faru yakaraÉ—e Æ´an uwa,
su Aunty Jaleela duk sun taho gidan cikin tashin hankali,
Aunty Rafee'at da yanzu isowar su ita da Dr Farooq ko jiran ya dai-dai ta parking batayi ba tafito cikin tsananin tashin hankali tanufi ciki.
Nan ta iske Æ´an gidan dukan su zaune cikin parlour'n Ummi har da wasu Æ´an uwan su,
da sauri tashigo cikin parlour'n cikin muguwar tashin hankali tana faÉ—in
"Ummi ina HAMDAH tatafi ina tasani batasan ko ina ba".
Ummi da har lokacin kwalla basu dai na zuba a idon taba takai hannu ta share wasu zafafan hawaye,bata iya ce komai ba
sai kwallar da ta cigaba da sharewa.
cikin share kwalla goggo Hauwa tace
"Tatafi bamu san in da ta tafi ba".
tafaÉ—a tana sharce hanci.
Kuka Aunty Rafee'at ta sake da karfi cikin muryar kuka sosai tace
"Wlh cikin Ya SALEEM ne wlh cikin sane wlh na shaida HAMDAH bazata taɓa ai kata abun da ake zargin ta ai kata ba".
da sauri
tayi gun Dr Farooq da yanzu yashigo tariko hannunsa tare da faÉ—in
"Wlh Allah cikin nan na Ya SALEEM ne Abba'n Adeel kai shai da ne".
sai kuma tasaki hannunsa tayi gun goggo Hauwa tace
"Goggo Hauwa kema shai da ce Ya SALEEM shine mutum na farko da ya taɓa sanin ta ɗiya mace,wlh na rantse HAMDAH bata ai kata abun da ake zargi ba wlh sharri a ke mata".
takarasa maganar cikin shashsheka..
Aunty Jaleela ma nagefen Ummi takasa cewa komai sai kwallar da take ta share wa,
parlour'n yayi shiru cike da jimami da sautin kukan Aunty Rafee'at......★
salati parlour'n ya kaure da shi tuni hawaye yashiga wanke fuskar Ummi,
cikin takai ci Abba ya dube ni yana faÉ—in
"Abun da zaki saka mana da shi kenan ki ɓata mana family kin tozarta shi tozarci mafi muni me kika nema kika rasa a rayu HAMDAH me muka gaza miki wacce gatace bamu baki ba sakayyar da zaki yi mana kenan!".
kai narika girgizawa hawaye na zuba a idona na buÉ—e baki zanyi magana Abba ya daka min tsawa.
kana ya dubi Ya SALEEM yace
"Tashi ka kaje hukuncin da ka yanke shine dai-dai ta haramta a gare ka kuwa tabbas".
a sannu ya mike yafita da sauri na mike tsaye kamar mai tashin aljanu na bi bayan sa kafin na iso shi har ya isa farfajiyar gida da gudu nasha gaban san sa na ruko hannunsa na É—aura kan cikina cikin muryar kuka da fizgar numfashi na da nake ji kamar zai É—auke, ina kallon fuskarsa nace
"Ya SALEEM Ya SALEEM wlh abun da ke cikin kinan nan naka ne kai ne uban sa, wlh babu wani na mijin da ya taɓa rike koda bakin mayafi nane bare har ya sanni ƴa mace bayan kai Ya SALEEM ɗan kane cikin kane wlh babu wani wan da yake zuwa guri na".
fizge hannunsa yayi kana ya dube ni da kyau yace
"Kada ki sake dan ganta abun da ke cikin ki da Ni ni ba uban sa bane, ke kinsan uban sa ai jeki haifa ki kai masa abunsa in yaso ki kashe shi tun a ciki tun kafin ya fito duniya a san halin da kike ciki, asan wacece ke mutum a fuska kawai,
In dai irin wannan É—an ne zai zamo nawa har abada bana so!".
yana kaiwa nan ya juya yashige motar sa yafice a gidan..
Dur kushewa nayi a gurin ina wani irin kuka mai tsuma rai, na daÉ—e durkushe jin jiri na fisgata na mike da kyar na koma parlour in da su Ummi suke har lokacin Ummi na hawaye sai dai ta kasa furta ko da kalma É—aya ce, goggo Hauwa da Aunty Halima sunyi jugum.
ina saka kafata cikin parlour'n Abba ya takatar da ni da faÉ—in
"Kada ki sake ki tako cikin parlour'n nan maza ki tafi kiyi nesa da mu domin zama da irin ki acikin family tamkar rugujewar ahali ce,
kisani idan zuciya ta tabuga to kece sila kuma bazan taɓa yafe miki ba,bana kaunar nakuma buɗe idanuna na ganki fita min a gida kitafi duk inda zakije amma ki sani ban yarda kije gidan ɗaya daga cikin dangi naba har in dangi nane fita min a gida nace!".
yafaÉ—a cikin karaji baya nashiga ja inajin maganar Abba tamkar saukar ruwan dalma a zuciya ta.
mikewa Ummi tayi hawaye taf idon ta tace
"Ina zataje Abba'n Fauzan ka bata lasisin shiga duniya kenan? bata da in da yafi nan in kuma kace ta tafi to sai dai mutafi tare".
Ummi ta nufo ni tana cigaba da faÉ—in
"ÆŠiyar ka mace zaka jefawa duniya sai dai in mutafi tare".
cikin fushi Abba yace
"Fatima idan kika fita daga cikin parlour'n nan to ki tabbata nayafe ki".
ido na waro cikin tsananin tashin hankali nashiga girgiza kai da karfi nace
"Ummi dan Allah dan Allah karki fita Ummi ki koma na rokeki Abba kayi hakuri ni zan tafi".
ganin tana ta daÉ—a matsoni yasani tahowa da gudu na rungume ta cikin muryar kuka nacigaba da faÉ—in
"Ummi ki koma dan Allah karki fita".
sai kuma na zame jikina da sauri na saka hannuna biyu na share hawaye na nakuma kai hannu kan fuskar ta nashare mata hawaye tare da yin wani murmushi ina duban ta yayin da wasu zafafan hawaye suka zubo min nace
"Ummi duk inda nake a faɗin duniyar nan ko a muce ko a raye addu'ar ki itace zata zame min garkuwa in nazamo silar fitar ki a gidan nan bazan taɓa yafewa kai na ba".
Najuya na dubi su goggo Hauwa da tuni suma hawaye yagama wanke musu fuska na haÉ—e hannaye na biyu nace
"Dan Allah goggo Hauwa Aunty Halima kada kubar Ummi na ta fita dan Allah".
da sauri na juya nafita a cikin parlour'n na É—au jakata dana yar dashi a tsakar gidan da sauri na nufi kofar fita ina waige ko Ummi na biyo ni.
sauri na rika yi har na fita daga layin mu.......!★
Mommyn twins ce
Sauri nake kamar zan tashi sama duk da nafita daga layin unguwar amma hankali na bai kwanta ba,tafiyar nake ina ta waige-waige,sai gani nake kamar Ummi zata biyo ni.
tafiyar kawai nake batare da nasan in da zani ba kokuma sanin in da na nufa ba.
Karar ababen hawa da naji ya karaÉ—e ko ta ina shine ya dawo dani cikin hayyaci na,nayi mamakin ganin in da nake
Duk da kuwa tazarar dake sakanin unguwar mu da in da nake yanzu
wato winte.
Gefen titi na zame nashiga cikin mutanen da nagansu zazzau ne kan bence wasu ko nata harkokin gaban su.yayin da zuciya ta keta azalzala ta ji nake idan naci gaba da jan numfashi acikin garinnan tabbas zuwa anjima numfashi'n kwacewa zaiyi yatafi abun sa.
maganar da naji kusa da nine yasani É—agowa wani É—an yuniyon ne tsaye a kanmu yana faÉ—in
"Yauwa motar ku yanzu kam yacika kowa ya kawo kuÉ—in sa".
gafen da nake ya kalla kana yace
"Ƴan mata ke ma a wannan motar kike?".
tsintar kaina nayi da gyaÉ—a masa kai,yace
"To kawo kuÉ—in ki mota ta cika".
idanuna na mai da kan akwatin da ke gaba na tabbas nasan bana da ko sisi dan ban fita da ko biyar daga gida ba, hasali ma babu abun da na iya É—auka in ba wannan akwatin ba,ganin yanata amsar kuÉ—in mutane sai na kai hannuna kan zip É—in bayan akwatin ina É—an wasa da shi a raina nake faÉ—in
"To ko ince masa yakarɓi akwatin a bakin kuɗin motar ne, Ni har da kayan cikin ma in dai zasu ɗauke Ni suraba ni da garin nan".
yadda nake wasa da zip É—in sai yana É—an zugewa da mamaki nakurawa aljuhun jakar ido ganin bakin kuÉ—i ya baiyana, da sauri na idda zuge zip É—in nazaro kuÉ—in ina juyashi a hannuna naira dubu biyu sabbi dar.
tunanin ta yadda akayi kuÉ—in yashigo cikin a kwatin nake,
nan take na tuno lokacin rasuwar Inna ina zaune a cikin bedroom É—in Ummi taciro kuÉ—i cikin wardrobe zatayi aika kasuwa daga cikin kuÉ—aÉ—en dubu biyu suka zubo,nakwashe ina mika mata tafita da sauri tana faÉ—in na ajiye bari tazo,a lokacin kuwa kasan cewar ina zaune ne kusa da akwatin sai naja zip É—in a kwatin nasaka ciki kan cewar in tashigo zan cire na bata,gaba É—aya nagama mance wa a she dai ban bata ba..
Numfashi na sauke a hankali na furta
"Alhamdulillah".
dai-dai lokacin kuwa É—an yuniyon É—in yake faÉ—in
"Kawo nake".
duka kuÉ—in na mika masa sai naga ya zare dubu É—aya yakai hannu aljuhu yazaro É—ari biyu sai ya haÉ—a da dubu É—ayan nan ya mika min dubu É—aya da É—ari biyu kenan.
karɓa nayi ina juya kuɗin a hannuna "Wato kuɗin motar garin da zasu ɗari takwas kenan?".
nayi tan bayar a raina,
ganin duk wan da yabada kuÉ—i sai ya shige cikin motar dake gaban mu sai nima na mike nashige cikin motar ina rungume da akwatina.
Ina alla-alla motar ta tashi duk da kuwa bansan motar wani gari zata ba ban kuma da mu da duk inda zaije ba ni dai burina nafita a cikin garin nan, bana kaunar na buÉ—e idanuna nakuma ganina cikin garin bana kaunar narika shakar iskar garin naji na tsani garin gaba É—ayan ta.
numfashi na sauke tare da yin hamdala lokacin da motar ta hau kan titin taɗau hanyar fita daga cikin garin......★
★★★
A nan cikin garin Bauchi kuwa,
kan kace me labarin abun da ya faru yakaraÉ—e Æ´an uwa,
su Aunty Jaleela duk sun taho gidan cikin tashin hankali,
Aunty Rafee'at da yanzu isowar su ita da Dr Farooq ko jiran ya dai-dai ta parking batayi ba tafito cikin tsananin tashin hankali tanufi ciki.
Nan ta iske Æ´an gidan dukan su zaune cikin parlour'n Ummi har da wasu Æ´an uwan su,
da sauri tashigo cikin parlour'n cikin muguwar tashin hankali tana faÉ—in
"Ummi ina HAMDAH tatafi ina tasani batasan ko ina ba".
Ummi da har lokacin kwalla basu dai na zuba a idon taba takai hannu ta share wasu zafafan hawaye,bata iya ce komai ba
sai kwallar da ta cigaba da sharewa.
cikin share kwalla goggo Hauwa tace
"Tatafi bamu san in da ta tafi ba".
tafaÉ—a tana sharce hanci.
Kuka Aunty Rafee'at ta sake da karfi cikin muryar kuka sosai tace
"Wlh cikin Ya SALEEM ne wlh cikin sane wlh na shaida HAMDAH bazata taɓa ai kata abun da ake zargin ta ai kata ba".
da sauri
tayi gun Dr Farooq da yanzu yashigo tariko hannunsa tare da faÉ—in
"Wlh Allah cikin nan na Ya SALEEM ne Abba'n Adeel kai shai da ne".
sai kuma tasaki hannunsa tayi gun goggo Hauwa tace
"Goggo Hauwa kema shai da ce Ya SALEEM shine mutum na farko da ya taɓa sanin ta ɗiya mace,wlh na rantse HAMDAH bata ai kata abun da ake zargi ba wlh sharri a ke mata".
takarasa maganar cikin shashsheka..
Aunty Jaleela ma nagefen Ummi takasa cewa komai sai kwallar da take ta share wa,
parlour'n yayi shiru cike da jimami da sautin kukan Aunty Rafee'at......★