Sashe 13
Hamdah Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gida ta koma ta É—auki laidar kayan jariri da take siya da É—ai-É—ai tana ajiye wa idan HAMDAH ta haihu za'asawa abun da ta haifa har na kwana bakwai,wato kala bakwai kenan kayane irin wan da mace da na miji zasu iya sawa,da É—an sauran kayakin bukatu na jariri a talakance.
tafito ta tari abun hawa tanufi asibitin.
ko da ta isa
ta kai musu kuÉ—in ta rokesu da Allah kan suyi mata ai kin idan Allah yakai rai gobe zata kawo musu ciko.
Nan suke sanar mata ai ammayi mata CS É—in sabo da ganin rayuwar ta da abun da ke cikin ta suna cikin haÉ—ari.
wasu nurse's ne guda biyu suka iso in da su Mama suke tsaye da É—aya daga cikin Dr É—in da sukayi wa HAMDAH CS,
É—aya daga cikin nurse É—in tadubi mama tace
"Tun É—azu muketa nemanki Ina kayan babys da sauri mama tamika musu ledan dake hannunta su shige labour room domin su kimtsa babyn.
Mama ta dubi Dr tace
"Likita ya ita mai jegon dai?".
Dr ta juya tashige room É—in dake gefe da labour room tana faÉ—in
"Babu komai in sha Allah har an fito da ita ma tana wannan room É—in".
wuf Mama tayi zatabi bayan ta tayi saurin cewa
"A'a tsaya tukun akwai likitoci a kanta suna ai kin su bari su gama tukun".
tafaÉ—a tana shigewa cikin room É—in.
ajiyar zuciya Mama ta sauke tanayiwa Allah godiya,
taja gefe ta tsaya idanunta akan kofar da akace HAMDAH na ciki.
Bayan wasu Æ´an mintuna likitoci'n suka fito Mama na ganin da sauri ta matso in da suke tana tambayar su ya jikin nata,
sukace zata iya shiga yanzu.
cikin hanzari ta juyo zata shiga cikin room ɗin tajiyo Muryar nurse's ɗin da suka karɓi kayan jariri suna faɗin
"Yauwa mun gama ga baby's É—in".
da sauri ta juyo da mamaki take kallon nurse's É—in dukan su rike da baby,
sai tasa hannu takarbi guda daya na hannun wacce take kusa da ita tajuya zata wuce,
sai É—ayan nurse din tace
"Baki da me taimaka miki ne ga É—ayan fa,
ko kin bar min ne".
tafaÉ—a tana murmushi É—ayar tace
"Ai kuwa nima yaran sun tafi da ni Wlh ni ban taɓa gyara kyawawan baby twin's irin waɗan nan ba kallesu fa wlh ko ƴaƴan turawa bazasu nuna musu komai ba kai ni sai nagama sunfi min ƴaƴan turawan".
da maki Mama ke kallon su da jin abun da suke faÉ—a
tace
"Kuna nufin yanbiyu ne ta haifa duka waÉ—an nan Æ´aÆ´an ta ne?".
tayi maganar cikin matukar mamaki.
dariya sukayi mata ganin yanda take maganar bilhakki,
Nurse É—in ta mika mata É—aya babyn tana faÉ—in
"Duk natane,yauwa na mijin shi aka fara cirowa kafin macen".
rungumar yaran mama tayi a kowani hannunta guda tajuya cikin tsananin farin ciki har da kwalla tanafadin "Alhamdullilahi Allah mun gode maka".
cikin hanzari tashige dakin da aka kai HAMDAH.
dasauri takarasa inda take kwance da yaran a hannunta tana fadin
"HAMDAH bude idon ki kiga abin da kika haifa".
jin Muryar mama yasani buÉ—e idanuna a hankali,
asannu nashiga juya kai na saiji nayi kamar an É—aÉ—É—aure ni,
dasauri mama tamatso kusada ni ta ajiye yaran dake rike a hannunta a gefe na,tana cigaba da faÉ—in
"Allah mai iko kai sannu HAMDAH sannu kinji".
asannu najuyo kaina da kyar kallon yaran da mama ta ajiye a gefe na nayi kana daƙyar nabude baki murya can kasa nace
"Mama waÆ´annan yaranfa?".
sai da ta maso sosai kafin ta iya jin abun da nake faÉ—a,
fuska É—auke da yelwataccen murmushi tace
"Dukkansu nakine".
cikin tsananin farin ciki da murna Mama ta É—ago É—aya daga cikin yaran ta karkato shi saitin fuskanta
tana faÉ—in
"Kalli kyakkyawar mai gidan nan nawa
da sukayi ta baki wuya,ga kawata ma nan".
ido na kurawa jaririn yayin da naji wani irin mummunar faÉ—uwan gaba ya ziyarci zuciyata,
fuskar Ya SALEEM kaÉ—ai nake hangowa kan fuskar jaririn,
idanuna na rumtse da karfi tare da kuma buÉ—e shi kan fuskar jaririn,
mai mugun kama da Ya SALEEM tamkar an tsaga kara.
Mama ta mai da yaron ta kwantar ta É—ago É—ayar tana faÉ—in
"Ga kawata nan tabar kallah masha Allah".
hancin babyn ta lakata tana washe baki da cigaba da faÉ—in
"Ikon Allah wannan girman ciki yayi yawa ashe dai kune kuka baje ciki".
kai na na rausayar gefe da kyar,
jin wasu zafafan hawaye sun zubo min kokarin danne zuciya ta daketa son fama min mikin dake cikin ta nake,
rumtse idanuna da karfi nayi duk yan da naso danne zuciya ta sai da na tuno.
fahimtar yanayin da na shiga yasa Mama tayi ta jana da hira duk da bana ammsa mata da ido kawai nake binta.
haka tayita kokarin gusar min da damuwar da take hangoshi cikin idona,
har sai da taga na saki raina,
har naÉ—an juyo da kaina ina kallon yaran,
Allah mai girma da É—auka wai duk waÉ—an nan Æ´aÆ´an a cikina a ka ciro su.
Mommyn twins ce
Ranan Azaune mama ta kwana rike kuma da yaran idan É—aya yayi motsi sai ta aje na hannunta taÉ—au ki É—ayan,
duk san da na farka sai na ganta zaune tausayin ta yakama ni,
na tabbata tun da rana dana fara labour batasa komai a bakinta ba har kuma yanzu, domin gabakinta abushe,
haka tayi-tayi dayaran har gari yawaye.
washegari da safe
Zainabu suka zo da ita da wata makociyar Mama,sukazo mana da abun karyawa niki-niki.
suna rike da yaran a hannunsu kowa sai sanbar ka yake,
Zaunabu data kurawa Æ´a macen ido tace
"Oh ikon Allah jibi waÉ—an nan yara wazai gansu yace tagwaye yara katin-katin dasu kamar haihuwar É—aya,
kai sannu HAMDAH gaskiya kinyi kokari waÉ—an nan kam ai sai dai CS É—in".
murmushi matar da sukazo da ita tayi tace
"Wlh kam yara tabar kallah ga wayo ni dai tun zuwan mu idanun su abuÉ—e suke".
Mama tayi dariya tana faÉ—in
"WaÉ—an nan awaye kazan birni ai tun jiya idanunsu a buÉ—e yake suna jin motsi zasu juya ido gun kamar masu jin magana,
kunga wannan bakyauyiyar kawar tawa idanunta a kan fanka, shi ko angon ido yakurawa kwan wuta".
dariya duk suka saka ai kuwa sai yaran suka shiga raba ido kamar sun san me ake faÉ—a,
Zainabu tace
"Ai kuwa yaran akwai wayo ga yan da suke kokarin juya kai suna jin magana"...
Haka suka yi ta kallon yaran cikin ban sha'awa.
nan mukata hira dasu sai kusan azahar sukatafi.
mama ta rakasu tadawo tana dawowa daga rakiyarsu nadubeta cikin yanayin gajiya da kwanciyar da tun jiya ban motsa daga in da aka kwantar da ni ba,
nace
"Mama dan Allah ki dagani nikam nagaji kokuma injuya gefe".
Mama tace
"Sunce bayanzu ba". dasaura nace
"To Mama kishin ruwa nakeji dan Allah kibani ruwa nasha".
dubana take cikin tausayawa da tsigar rarrashi tace
"Kiyi hakuri HAMDAH su sun fimu sanin dalilin da yasa suka ce kada a baki komai tun da ai kin sune ki kara hakuri dan Allah kibari likitocin suzo tukun".
kai kawai najuya cikin gajiya da kwanciyar guri daya gamugun ƙishin ruwan da nakeji...
karfe
huÉ—u na yamma har lokacin ina nan kwance duk yadda naso Mama ta É—agani ko taban ruwa nasha fir taki.
kuka nasaka mata ina faÉ—in
"Ni dai nagaji nagaji ƙishin ruwa nake ji".
Ido Mama ta zuba min tana jijjiga baby boy É—in dake ta zandara ihu tun É—azu,ta bashi ruwa yafi a kirga da zaran ta cire fida a bakin sa sai ya sa kuka.
Ana cikin haka sai ga É—aya daga cikin
Doctors É—in da sukayi min CS yashigo,
yace
"Mama mai kikayi wa pationt din mu ne haka take kuka".
yafaÉ—a da murmushi yana karaso wa bakin gadon da nake,
Mama tace
"Wallahi tuntini wai so take a ɗaga ta tagaji kuma wai kishin ruwa take ji shine nace tayi haƙuri sai kunzo".
murmushi Dr yakuma cikin kwarewa da iya tafiyar da mara lafiya ya dube ni yace
"Idan zaki iya tashi to tashi".
nayi yunƙurin tashi naji Nakasa sai ji nayi kamar cikina yana buɗewa in da aka min CS ɗin,
ido na matse sai ga hawaye sharr.
Ido yaÉ—an kura min kana yace
"Sorry bari nurse's suzo su tai maka miki".
yafita ba jimawa nurse suka shigo suka É—agani suka goge min jiki suka kimtsa ni,
kana suka cewa mama takawo ruwan zafi kadan a kofi akabani nasha,
sannan sukace na gwada kwanciya da kai na in zan iya,nan ma na kasa,su suka mai dani
suka kwantar dani. sukace wa mama taringa haÉ—a min milo inasha duk bayan awa daya domin zai taimaka
min yakawo min ƙarfi ajikina.
tace to insha'allahu nan suka fita...
Da daddare nurse's É—in suka kuma zuwa,
yanzu kam cewa sukayi na tashi da kai na daƙyar na iya mikewa zaune, bayan sun gama gyara min jikina sukace na kwanta da gefe in zan iya shima nakwanta,
Washegari ma da kaina na tashi nurse's suka gama ai kin su suka fita,
Mama tasa min pillow a baya na na jingina dashi,
bayan nagama shan tea mai zallar milo da Mama ta haÉ—a min,
tadube Ni tana faÉ—in
"To tun da kin koshi kibashi nono yanzu kam kin ga dai tun jiya kuka yake,
ga Æ´ar'uwar sa ma yau ta tashi da kukan, yunwa duk suke ji".
Baki na tura dan tun jiya take ta bina nabashi nono toma ni ta'ina ma zan fara,
miko shi tayi taÉ—aura shi kan cinya ta sai dai bata sake shiba tana rike dashi ta É—an gyara shi ta inda bazai fama min ciwo ba,
tace
"To É—an gyara sai ki bashi"...
yana kama nonon nayi saurin fizge nonon a bakin sa tare da sakin Æ´ar karamar kara,
na yarfe hannu ina faÉ—in
"Wayyo zafi".
ai ko shima sai ya saki kuka yana cusa hannunsa cikin baki,
Mama
tace "Daure ki bashi kinji".
sai da Mama tayi ta lallaɓi na kafin na yarna na maida masa nonon bakin sa ina matse ido harda kwalla.
bayan yasha ta kwantar da shi ta É—auko ta ita ma tasha.
kana tayi musu wanka
nan da nan kuwa sukayi bacci....★
tafito ta tari abun hawa tanufi asibitin.
ko da ta isa
ta kai musu kuÉ—in ta rokesu da Allah kan suyi mata ai kin idan Allah yakai rai gobe zata kawo musu ciko.
Nan suke sanar mata ai ammayi mata CS É—in sabo da ganin rayuwar ta da abun da ke cikin ta suna cikin haÉ—ari.
wasu nurse's ne guda biyu suka iso in da su Mama suke tsaye da É—aya daga cikin Dr É—in da sukayi wa HAMDAH CS,
É—aya daga cikin nurse É—in tadubi mama tace
"Tun É—azu muketa nemanki Ina kayan babys da sauri mama tamika musu ledan dake hannunta su shige labour room domin su kimtsa babyn.
Mama ta dubi Dr tace
"Likita ya ita mai jegon dai?".
Dr ta juya tashige room É—in dake gefe da labour room tana faÉ—in
"Babu komai in sha Allah har an fito da ita ma tana wannan room É—in".
wuf Mama tayi zatabi bayan ta tayi saurin cewa
"A'a tsaya tukun akwai likitoci a kanta suna ai kin su bari su gama tukun".
tafaÉ—a tana shigewa cikin room É—in.
ajiyar zuciya Mama ta sauke tanayiwa Allah godiya,
taja gefe ta tsaya idanunta akan kofar da akace HAMDAH na ciki.
Bayan wasu Æ´an mintuna likitoci'n suka fito Mama na ganin da sauri ta matso in da suke tana tambayar su ya jikin nata,
sukace zata iya shiga yanzu.
cikin hanzari ta juyo zata shiga cikin room ɗin tajiyo Muryar nurse's ɗin da suka karɓi kayan jariri suna faɗin
"Yauwa mun gama ga baby's É—in".
da sauri ta juyo da mamaki take kallon nurse's É—in dukan su rike da baby,
sai tasa hannu takarbi guda daya na hannun wacce take kusa da ita tajuya zata wuce,
sai É—ayan nurse din tace
"Baki da me taimaka miki ne ga É—ayan fa,
ko kin bar min ne".
tafaÉ—a tana murmushi É—ayar tace
"Ai kuwa nima yaran sun tafi da ni Wlh ni ban taɓa gyara kyawawan baby twin's irin waɗan nan ba kallesu fa wlh ko ƴaƴan turawa bazasu nuna musu komai ba kai ni sai nagama sunfi min ƴaƴan turawan".
da maki Mama ke kallon su da jin abun da suke faÉ—a
tace
"Kuna nufin yanbiyu ne ta haifa duka waÉ—an nan Æ´aÆ´an ta ne?".
tayi maganar cikin matukar mamaki.
dariya sukayi mata ganin yanda take maganar bilhakki,
Nurse É—in ta mika mata É—aya babyn tana faÉ—in
"Duk natane,yauwa na mijin shi aka fara cirowa kafin macen".
rungumar yaran mama tayi a kowani hannunta guda tajuya cikin tsananin farin ciki har da kwalla tanafadin "Alhamdullilahi Allah mun gode maka".
cikin hanzari tashige dakin da aka kai HAMDAH.
dasauri takarasa inda take kwance da yaran a hannunta tana fadin
"HAMDAH bude idon ki kiga abin da kika haifa".
jin Muryar mama yasani buÉ—e idanuna a hankali,
asannu nashiga juya kai na saiji nayi kamar an É—aÉ—É—aure ni,
dasauri mama tamatso kusada ni ta ajiye yaran dake rike a hannunta a gefe na,tana cigaba da faÉ—in
"Allah mai iko kai sannu HAMDAH sannu kinji".
asannu najuyo kaina da kyar kallon yaran da mama ta ajiye a gefe na nayi kana daƙyar nabude baki murya can kasa nace
"Mama waÆ´annan yaranfa?".
sai da ta maso sosai kafin ta iya jin abun da nake faÉ—a,
fuska É—auke da yelwataccen murmushi tace
"Dukkansu nakine".
cikin tsananin farin ciki da murna Mama ta É—ago É—aya daga cikin yaran ta karkato shi saitin fuskanta
tana faÉ—in
"Kalli kyakkyawar mai gidan nan nawa
da sukayi ta baki wuya,ga kawata ma nan".
ido na kurawa jaririn yayin da naji wani irin mummunar faÉ—uwan gaba ya ziyarci zuciyata,
fuskar Ya SALEEM kaÉ—ai nake hangowa kan fuskar jaririn,
idanuna na rumtse da karfi tare da kuma buÉ—e shi kan fuskar jaririn,
mai mugun kama da Ya SALEEM tamkar an tsaga kara.
Mama ta mai da yaron ta kwantar ta É—ago É—ayar tana faÉ—in
"Ga kawata nan tabar kallah masha Allah".
hancin babyn ta lakata tana washe baki da cigaba da faÉ—in
"Ikon Allah wannan girman ciki yayi yawa ashe dai kune kuka baje ciki".
kai na na rausayar gefe da kyar,
jin wasu zafafan hawaye sun zubo min kokarin danne zuciya ta daketa son fama min mikin dake cikin ta nake,
rumtse idanuna da karfi nayi duk yan da naso danne zuciya ta sai da na tuno.
fahimtar yanayin da na shiga yasa Mama tayi ta jana da hira duk da bana ammsa mata da ido kawai nake binta.
haka tayita kokarin gusar min da damuwar da take hangoshi cikin idona,
har sai da taga na saki raina,
har naÉ—an juyo da kaina ina kallon yaran,
Allah mai girma da É—auka wai duk waÉ—an nan Æ´aÆ´an a cikina a ka ciro su.
Mommyn twins ce
Ranan Azaune mama ta kwana rike kuma da yaran idan É—aya yayi motsi sai ta aje na hannunta taÉ—au ki É—ayan,
duk san da na farka sai na ganta zaune tausayin ta yakama ni,
na tabbata tun da rana dana fara labour batasa komai a bakinta ba har kuma yanzu, domin gabakinta abushe,
haka tayi-tayi dayaran har gari yawaye.
washegari da safe
Zainabu suka zo da ita da wata makociyar Mama,sukazo mana da abun karyawa niki-niki.
suna rike da yaran a hannunsu kowa sai sanbar ka yake,
Zaunabu data kurawa Æ´a macen ido tace
"Oh ikon Allah jibi waÉ—an nan yara wazai gansu yace tagwaye yara katin-katin dasu kamar haihuwar É—aya,
kai sannu HAMDAH gaskiya kinyi kokari waÉ—an nan kam ai sai dai CS É—in".
murmushi matar da sukazo da ita tayi tace
"Wlh kam yara tabar kallah ga wayo ni dai tun zuwan mu idanun su abuÉ—e suke".
Mama tayi dariya tana faÉ—in
"WaÉ—an nan awaye kazan birni ai tun jiya idanunsu a buÉ—e yake suna jin motsi zasu juya ido gun kamar masu jin magana,
kunga wannan bakyauyiyar kawar tawa idanunta a kan fanka, shi ko angon ido yakurawa kwan wuta".
dariya duk suka saka ai kuwa sai yaran suka shiga raba ido kamar sun san me ake faÉ—a,
Zainabu tace
"Ai kuwa yaran akwai wayo ga yan da suke kokarin juya kai suna jin magana"...
Haka suka yi ta kallon yaran cikin ban sha'awa.
nan mukata hira dasu sai kusan azahar sukatafi.
mama ta rakasu tadawo tana dawowa daga rakiyarsu nadubeta cikin yanayin gajiya da kwanciyar da tun jiya ban motsa daga in da aka kwantar da ni ba,
nace
"Mama dan Allah ki dagani nikam nagaji kokuma injuya gefe".
Mama tace
"Sunce bayanzu ba". dasaura nace
"To Mama kishin ruwa nakeji dan Allah kibani ruwa nasha".
dubana take cikin tausayawa da tsigar rarrashi tace
"Kiyi hakuri HAMDAH su sun fimu sanin dalilin da yasa suka ce kada a baki komai tun da ai kin sune ki kara hakuri dan Allah kibari likitocin suzo tukun".
kai kawai najuya cikin gajiya da kwanciyar guri daya gamugun ƙishin ruwan da nakeji...
karfe
huÉ—u na yamma har lokacin ina nan kwance duk yadda naso Mama ta É—agani ko taban ruwa nasha fir taki.
kuka nasaka mata ina faÉ—in
"Ni dai nagaji nagaji ƙishin ruwa nake ji".
Ido Mama ta zuba min tana jijjiga baby boy É—in dake ta zandara ihu tun É—azu,ta bashi ruwa yafi a kirga da zaran ta cire fida a bakin sa sai ya sa kuka.
Ana cikin haka sai ga É—aya daga cikin
Doctors É—in da sukayi min CS yashigo,
yace
"Mama mai kikayi wa pationt din mu ne haka take kuka".
yafaÉ—a da murmushi yana karaso wa bakin gadon da nake,
Mama tace
"Wallahi tuntini wai so take a ɗaga ta tagaji kuma wai kishin ruwa take ji shine nace tayi haƙuri sai kunzo".
murmushi Dr yakuma cikin kwarewa da iya tafiyar da mara lafiya ya dube ni yace
"Idan zaki iya tashi to tashi".
nayi yunƙurin tashi naji Nakasa sai ji nayi kamar cikina yana buɗewa in da aka min CS ɗin,
ido na matse sai ga hawaye sharr.
Ido yaÉ—an kura min kana yace
"Sorry bari nurse's suzo su tai maka miki".
yafita ba jimawa nurse suka shigo suka É—agani suka goge min jiki suka kimtsa ni,
kana suka cewa mama takawo ruwan zafi kadan a kofi akabani nasha,
sannan sukace na gwada kwanciya da kai na in zan iya,nan ma na kasa,su suka mai dani
suka kwantar dani. sukace wa mama taringa haÉ—a min milo inasha duk bayan awa daya domin zai taimaka
min yakawo min ƙarfi ajikina.
tace to insha'allahu nan suka fita...
Da daddare nurse's É—in suka kuma zuwa,
yanzu kam cewa sukayi na tashi da kai na daƙyar na iya mikewa zaune, bayan sun gama gyara min jikina sukace na kwanta da gefe in zan iya shima nakwanta,
Washegari ma da kaina na tashi nurse's suka gama ai kin su suka fita,
Mama tasa min pillow a baya na na jingina dashi,
bayan nagama shan tea mai zallar milo da Mama ta haÉ—a min,
tadube Ni tana faÉ—in
"To tun da kin koshi kibashi nono yanzu kam kin ga dai tun jiya kuka yake,
ga Æ´ar'uwar sa ma yau ta tashi da kukan, yunwa duk suke ji".
Baki na tura dan tun jiya take ta bina nabashi nono toma ni ta'ina ma zan fara,
miko shi tayi taÉ—aura shi kan cinya ta sai dai bata sake shiba tana rike dashi ta É—an gyara shi ta inda bazai fama min ciwo ba,
tace
"To É—an gyara sai ki bashi"...
yana kama nonon nayi saurin fizge nonon a bakin sa tare da sakin Æ´ar karamar kara,
na yarfe hannu ina faÉ—in
"Wayyo zafi".
ai ko shima sai ya saki kuka yana cusa hannunsa cikin baki,
Mama
tace "Daure ki bashi kinji".
sai da Mama tayi ta lallaɓi na kafin na yarna na maida masa nonon bakin sa ina matse ido harda kwalla.
bayan yasha ta kwantar da shi ta É—auko ta ita ma tasha.
kana tayi musu wanka
nan da nan kuwa sukayi bacci....★