← Book details Ali Abbas Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 38

Sashe 9

Ali Abbas Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Yaa Ali inaga wannan da muke shirin yi ha'incine da zalunci, yanzu qaddara munyi nasarar yin hakan, se kawai bayan tayi wani auren tsohon mijinta ya dawo, kokuma misali ace tun wancen lokacin ma ya mutu se yanzu mukaji labari,me kake ganin zamu sanarda iyayenta da ita kanta? Kasani ko kotu aka raba auren tayi wani auren idan ya dawo sedai a bata zab'i ta zaba koshi ko sabon mijin, zancen gaskia Abbi ba haka ya dace muyi ba, anawa ganin kenan" nisawa yayi yace

"Kuma kema kinyi tunani me kyau, ba damuwa a ajiye wannan zanyi magana da ita" shiru tayi batace masa komai ba.

   Dare lokacin ba kowa a b'angaren se Ameer da yalwa se kuwa Manga, dama d'akin yalwa daban yake Ameer kuwa dama  wurin Manga yake kwana, baccine ya dauki manga batare da shirin yin shiba ko adu'a batayiba saboda gajiya, se wuraren sha d'aya ta farka, wanka taje tayi ta dauro alwala sannan tazo ta tanawa  Ameer adu'a jin an murd'o k'ofar d'akin ya sanya ta mayarda dubanta zuwa ga k'ofar zubara tayi sabifa kayan bacci ne kawai ajikinta, tasoma janyo hijab d'inta dake kan gado,sanyawa tayi sannan ta qura masa ido yaudai ta kasa ce masa komai

"Hilwa bakiyi bacci ba?" tsoratar da ita yake qarayi idan yana ambatar mata wannan sunan, murya na rawa tace dashi

"Yaa gadanga ya sanarmun cewa kalmar hilwa alarabce ma'anarshi kyakyawa mesa kake kirana da wannan sunan?" murmushi ya sakar mata me sanyi sannan yace

"Gobe kinada muhimmin abinda zakiyi?" kallonshibta sakeyi "Ba abinda zanyi" tabashi ansa a taqaice cikeda kasala

Takowa yayi ya masto inda take sosai, ya kamo hannayenta duka biyu ya riqe, jikintane ya soma rawa ta d'an zame hannunta daya,ya qara kamowa ya matso daf da ita har suna jiwo bugun da zuciyoyinsu keyi

"Gobe ki shirya da safe k'arfe 9 zamu fita, akwai maganar danakeso muyi wacce take buqatar sirri"  zuwa yanzu harta soma hawaye

"Wace magana yaa Ali daba zamuyita cikin gida ba kokuma tare da Aunty huddy" hannunshi ya sanya ya soma share mata qwallan da suka zubo mata sannan yace "Banasan kukannan kamar yanda banasan gaddama kinji hilwa" tsiratar da ita yake duk sanda yake murya ko d'abi'u irinna gadanga ,gyad'a masa kanta kurun yayi ya sake hannayenta

"kiyi adu'a kafin ki kwanta kinji" nanma gyad'a ma kanta kurun ta kumayi,be damuba ya juya kawai ya bar d'akin, zaman dirshan tayi saman tile tana tunanin wannan abin, waishi yaa Ali besan tanada aure bane? Ko kuma shibesan darajar aureba, koshi d'an iskane dai? Banda haka mesa yake taba ta? Koda batada aure ai wannan haramunnne bare kuma da auren a ka? Gaskia da sake.....

Duk yayinda gadanga ya runtse idanshi Manga yake gani, wannan ganin daya mata cikin kayan bacci ya firgitar da tunaninsa, babu abu mafi daukar hankalinsa irin lallausan gashin manga, yana tsananin buqatar yaji yakai hannunshi yana shafar kanta, runtse idan shi yayi yayinda qirjinshi ke tsananin doka masa sabida abinda yake shirin yi besan yaya ma za'ayi manga ta karb'eshi ba.....

    Washe gari kuwa da sassafe Manga ta shirya Ameer yaje wurin yalwa, itama tayi wankanta ta sanya abaya baqa da mayafinta tayi kyau ainun.....kai tsaye part d'insu taje tamasa knocking lokacin ma huddy ta dawo tun 7:am, itace ta bud'e mata k'ofar seta kasa ce mata Ali take nema kurun tace

"Zan wuce school ne" kallonta huddy tayi

"Ina kince yau bakuda lecture's?" wayancewa tayi

"Da akwai wanda ze koyamun karatu ne,kuma yau ammana fixing lecture har biyu ma" jinjina kanta tayi "To kudin kashewa fa akwai?" ta kuma tambayar manga

"Ea wannan karon 40k yaa Ali ya sakan a acc nawa"  murmushi tayi tace "Lallai er gata duk ina zakine dashi, nagano yayankinnan yana shagwab'aki da yawa" murmushi tayi har haqwaranta suka bayyana gefen kumatunta d'aya kawai ya lob'a sosai, ta juya kawai tana cewa ta tafi, gogan kuwa ya rogata waje tana zuwa wurin motoccin ta ganshi tsaye jikin motar data kula yafiya amfani da ita, da hannu yamata alama data zago ta shiga motar ba musu ta shiga suka bar harabar gidan, be zame da ita ko inaba se gues house d'inshi dake sama road.....

   Kallonshi tae bayan yayi parking tace dashi "yaa Ali nanfa?" murtuqe fuska yae tamau

"Kizo muje kinji,banson yawan tambayoyi tunda ba cinyeki zanyi ba" murmushi kurun tamasa tagano beji dadin tambayar ba ta sakkoo.....

A parlor bayan tasha ruwan daya sanya wata dattijuwa ta kawo mata ya umarceta data shiga bed room dake hade da parlor din wanda ta kula se an shiga wani lubby haka ake tadda kofar dakin, ba musu ta shiga shima ya rufa mata baya, mamakin ganin ya baiwa wannan dattijuwar umarnin kar wanda yashigo gidan yake sannan ya kawota dakin ya kuma qulle, batace masa komai ba ta dai sunne kanta qasa, wata jaka ya dakko ya zauna kusa da ita sosai har jikinsu na gogar na juna,bata daice masa komai ba harya zuge jakar, ya zaro wani zobe ya miqa mata

"Hilwa kin gane wannan?" karb'a tayi ta qurawa zoben ido se kuma ta mayarda dubanta zuwaga na hannunta, zare natan tayi ta had'a da wannan kai tsaye heart d'in dake half ta had'e,murmushi tayi ta kalleshi

"Kalar zoben da yaa Gadanga ya banine a ranar dazeyi tafiyan dabe dawo ba, yace dani in riqe yabani ajiyar rabin zuciyarsa yayinda yace nima rabin tawa na hannunshi harya dawo gareni,bangane dalilinshi namun wayo ya gudu ba bayan yace na shirya mutafi tare, wlhy danasan yaa gadanga ze mun nisa har haka dabazanje dauko kayan nanba sedai nabishi a yanda nake..." murmushi yayi yasake kallonta ya miqa mata pictures dake hannun shi yace "wa'ennan hotunan fa" da sauri tasoma kalla tana zare ido, kallon shi tayi murya na rawa ta soma magana

"Yaa Ali dama ka had'u da yaa gadanga shine baka sanar dani ba, nasan a hannunshi kawai za'a samu wannan zoben da wa'en nan hotunan, ranar daze tafi ya ebe su ya sanar dani ze nunawa en uwansa, ko d'aya bebar munba, dan Allah yaa Ali sanar dani wane halin yake ciki yanzu?" shiru yana yana jin matuqar tausayinta lokaci d'aya bugun zuciyarsa yayi mugun qaruwa, da qyar ya iya furta "ki kwantar da hankalinki muyi magana Hilwa zakiji komai" riqo hannunshi tayi harta soma hawaye

"To yaa Ali amma karka sanar dani cewar wai gadanga mutuwa yayi, nasan be mutuba wlhy yana raye ko yaa Ali?" shi kamma qara rud'ar dashi takeyi riqe hannunta ya qarayi shima yakula bata cikin yanayin hankali ma, mask d'in ya ciro agabanta ya daura akan fuskarsa dama yanayin sanya irin na gadanga yayi, miqewa tayi da sauri taja baya cikeda tsoro se sannan ta kula da yanayin shigarsa

"Idan tunani kake zaka iya siye zuciyata ka lalata mun rayuwa wlhy kayi kad'an kuma Allah yafika, kasani wannan hanyar daka d'akko bame dorewa bace kuma ka cutar da Aunty huddy kama da wane ai bata wane Yaa Ali, shiya sanya ka kawoni nan har kana rufe d'aki sabida kai lalata dani ko?" beyi tsammanin zuciyarta zataje mata canba, cire mask d'in yayi yaje kusa da ita ya riqo hannunta da sauri ta warce hannun, d'an had'e fuska yayi

"Ke a tunanin ki ko mata zan nema sena rasa wacce zan nema saike, shekaru nawa ina ganinki bansan zan neme kiba se yanzu, me kika d'aukeni? Cewa na miki zamuyi magana kuma maza ki zauna ki nutsu magana zamuyi ki kuma bude kunnuwanki ki saurareni da kyau" zama tayi tanata faman kuka yace cikin nutsuwa

"Kamar yanda kika sani Sunana*ALI ABBAS* muhammad Auwal, haifaffen garin sokoto ne kuma mune mukeda masarautar sokoto gabaki dayanta, Na taso ne gidanmu naga mahaifiyata itace Babba acikin matan sarki, ya dad'e bayan ya aureta be qara aure ba, kasancewar yana matuqar santa amma sedai Allah be basu haihuwa ba da wannan Allah ya bashi ikon qaro mata har biyu, Umma hasana da mama iya nasan duk kin sansu da 'ya'ya yensu, bayan yayi auren se matan suka dinga haifa masa yara amma duk mata to kuma kinsan duk wani sarki da bashida magaji hankalinshi baze kwantaba sabida mata basa sarauta sun shiga damuwa sosai katsam Fulani Adama ta samu ciki, cikin ikon Allah data tashi haihuwa seta haifeni!!! A wannan lokacin anga murna kasancewar sarki ya d'oki san duniya ya d'ora akaina, baya ganin kowa se ni kawai, sekuma na taso cikin tsananin tsana agidan wurin en uba, bayanni akwai qanina shamsudden da haris fulany ce ta haifemu mumu uku batada mace ko d'aya,yayinda sauran mata basuda maza a yaransu duk matane duk yawan haife haifen su kuwa, aduk yanayin tsanar danake gani daga gun en uwana babu wacce take damuna irin yanda fulani adama kemun, ba ruwanta dani ba'a dukana tai magana ko aci zalina itadai kurin kawai, bata bari na rab'e ta sam, duk azuwan dan fari nake, ko sunana bata kira!

Wannan abin datake mun yana cikin abubuwan dasuka janyo cabewar wasu al'a mura nawa gaba d'aya, ganin haka ya sanya ina gama primary school mahaifina ya daukeni zuwa saudiyya, a can nayi secondry school nakuma je jami'atul madeenah inda na karanci mechanical enginrng, har master's d'ina acan nayishi da phd da komai, kuma ina karatun addini sosai wannan ra'ayin mahaifinane, nikanyi shekaru banzo ba, dama sabida mahaifiyata nake zuwa to bata kulani gaisuwa kawai take ansamun shikenan, wannan ya qular da mahaifina sabida yashayi mata fada amma bata dena ba, wai a dole nine d'an fari, da wannan ya hanani zuwa gabaki daya nafi shekaru 14 banzo Niger ba sam seda na kammala duk abinda ya dace a saudi sannan na dawo Nigeria, Tun a airport na samu yanayin nutsuwa na dirata gida, kowa ya tarbeni cikin karamci en uwana ma da basa sona sena tarar dayawa daga cikinsu sun sauya hali sosai, amma abin haushi koda naje gun fulani Adama banda gaisuwa babu abinda ya kuma shiga tsakanina da ita, kece tafi shiri dake a gidannan nasha zuwa sashen ta kinacan kema shaidata ce akan yanda takemun tamkar wani d'an tsuntuwa. Shiru ya d'anyi kanyaci gaba
Chapter 9 · 0% Book details