Sashe 18
Ali Abbas Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Toni Auta niba likita ba ba komai, bansan meke damunki ba ko asibiti zamu je?" shagwab'e fuska tayi tace barinje in gayawa Aunty huddy ta dubani to kobe yiba?" murmushi ummun tayi
"Ki zauna anan barin wa huddyn waya, ai bakya riqa yawo ba bayan kince har jiri kike gani" kwantar da kanta tayi zaman jikin ummu, ta lumshe ido tanajin qaunar ummu har cikin ranta da ruhinta, mata me karamci da qaunarta..........Kallon ta sosai huddy tayi cikin dokawar qirji na kishi irin na mata bayan kwajin fitsarin daya mata ya fito kuma bincika yanayin al'adarta ta gano tayi tsallaken sati biyu be zoba ta kalli ummu tace
"Ummu juna biyu ne da ita na tsawon wata d'aya da satuka biyu" Washe baki ummu tayi aranta tace ashe an angwance a India" ta kalli huddy tace tana fad'ad'a murmushinta
"Lallai ma auta an gama girma, kije zanga en jikokina ta wurin auta, toki sani bana san kishiya,bazaku taru keda hudaisa kuna jeremun kishiyoyi ba muji zaki kawo, kinga yanzu me martaba bashida magana seta Ahasan yaga yarinya ze qyale tsohuwa" mayarda dubanta tayi zuwa ga huddy taci gaba "A rubuta mata magun gunan dazatasha tasamu sauqin wannan wahalan, tunda juna biyu beje ko ina ya kawo ba yasoma baiwa auta wahala, keni wannan koda mijine banayi,ze daddage yake baiwa Autan ummu wahala,ko Auta" sadda kanta tayi qasa qirjinta na wani irin mugun dokawa, harta ji jirin datakeji yana qaruwa, Innalillahi wa inna ilaihirraji'un itace kalmar data furta a hankali, huddy senyaqe takeyi tace aranta wato ni inacan ina fama da kaina duk ciwon danake shi kuwa honey moon yaje da matarshi dukda yake nice na kafe akan sena tafi da ita.......
"Zanje na rubuta sena baiwa abbin su Ahasan ya siyo mata, seta zauna anan kawai tunda ni bana zama" murmushi tayi tace
"Dama bazan bada autana ba, tana nan kusa dani inshaa Allah" murmushi tayi ta juya sabida basa wasa da ummu" a parlor ta sami Ali Abbas ta zauna kusa dashi ya kalleta
"Kin jima da yawa wani abinne?" murmushi tayi tace
"Kasan halin ummu indai akan sha'anin Manga ne, dukta tashi hankalinta amma nisam bazan gaya maka komai ba seka bani goro" murmushi yayi yace yana kallonta
"Zan bayar mana sanar dani menene? Wani abin farin cikinne ya samemu?" murmushi tayi itama tace
"Manga ce da ciki wata d'aya da sati biyu, kaga har strip dinma na pt nazo maka dashi,kace angwancewa akayi daga India?" wani kallo ya wurga mata wanda ta kasa fassara ma'anarsa,yace cikin mamakin
"Ciki kuma Manga kamar yaya?" murmushi tayi tace
"Kamar yanda kamata ciki mana Haba Abbin Ahasan sekace wani mugun labari kalli sauyawar fuskarka kodai kaso seka gama shan angwanci ciki yashiga,to wane angwanci kuma bayan wannan anje honey moon an dawo da goro" da qyar ya saisaita nutsuwar shi ya qaqaro murmushi cikin hikima ya wayance mata yasa dariya yace "Mamaki nake ciki da wuri haka" ita kuwa kasan zuciyarta ma takaicin sa takeji tace
"Kaine kayi shigar wuri baka jira ta tare ba, dole kaga ciki da sauri haka" murmushi yayi abinda be taba yiba fita da irin wannan jallabiyar dayake zaman gida da ita shi yayi, ya miqe kurun yayi ban garen fulani.....batanan da saurinta taje kaiwa sarki albishir shi kuwa ya shiga d'akin kai tsaye, kuka ya tarar tana yi ya cizgota ta miqe tsaye tana ganin yanayinshi ta shiga rudu murya na rawa ta furta
"Na rantse da girman wanda rayuwa ta take hannunsa ban taba sanin wani d'a namijiba, bansan inda aka samo wannan cikin ba" Wani mahaukacin mari Ali ya dire mata seda taga taurari ba adadi, yace
"Aruwa kika sha? Nace dan ubanki a ruwa kikasha cikin? Zaki kawomun hauka anan banza shegiya mara imani, dama duk shekarun nan maza kike bi ko? Se yanzu Allahu ya tona miki asiri, wlhy ki sani bazan tab'a lamuntar wannan jakancin ba, idan na karb'i cikin nan shege nake wlhy se duniya tasan abinda kika aikata, aini bawai wawa bane jahilar yarinya mara dangana kawai" kuka kawai tana bashi hakuri amma se fada yakeyi kallonshi ttayi
"Dan Allah ka dena daga murya yaa Ali kar bayi su jiyo mu, se maganan ya zam tsegumi acikin gidannan, wlhy ka yadda dani ban taba aikata wani abu ba da igiyar aurenka" wani marin ya kuma dire mata ya cafki wuyanta, seda taga mutuwa kusa sannan ya turata ta fad'i akasa ya juya, yana kawowa qofa ummu dataje me martaba na fada ta dawo ya gani a tsaye ta qura masa ido cikin tukuma, ze iya cewa wannan ne karonta na farko data tsoma idanuwan ta acikin nasa,murya a qasa tace
"Idan ka fitar da wannan maganar Allah ya isa ban yafe maka ba, ko zuhair ka sanarwa da zancen cikinnam cewar banaka bane ban yafe na, kuma bazan lamunci kace ba danka bane, da nakane kona waye kaji na gaya maka, wawa kawai dabesan ciwon kanshi ba" sadda kanshi yayi a qasa yawuce kawai batare da yayi magana ba sam......shiga cikin d'akin tayi ta zauna saman gado ta qurawa Manga ido tanaso ta gano gaskiyar ta, kallonta manga tayi tace tana kuka
"Wlhy Ummu bansan komai ba, ba abinda na sani ban tabayiba wlhy sharri ne kawai dan Allah ki taimakamun ki nuna masa gaskiaya ummuna dan Allah" Rungumeta kawai ummu tayi tana bubbuga bayanta a hankali.
Mom Nu'aiym
*HASKE WRITER'S ASSO. (Home of expert and perfect writer's)*
*👑ALI ABBAS👑*
*Billy Galadanchi*
*Sadaukarwa gareki qawa ta gari Fulany saddy*
13
D'agota tayi ta kalleta sosai tace "Auta kalleni nan dena kukan haka" d'agowa tayi ta kalleta sosai tace da ita
"Auta ki kwantar da hankalinki ki dena kukannan, ki nutsu ki gaya mun gaskia abinda nake san sani" gyad'a mata kanta tayi amar to taci gaba
"Sanar dani gaskia alokacin da yan fashi suka d'aukeku sun miki fyad'e?" tana kuka tace
"Wlhy Ummu basu samu nasara ba ko kad'an akaina, Humaira ce kawai suka samu sa'arta amma banda ita bakowa harni" jinjina kanta tayi tace
"Shirya tashi mu fita" ba musu suka fito a tare zuwa asibitin qwararru ta jiha, binciken dai ya nuna cikin watanshi d'aya da sati biyu kuka sosai Manga keyi harsuka dawo, wato dai ta tabbata cewar lallai cikinne da ita, to amma ta ina? Garin yaya hakan ta faru? Har suka isa bangaren su kuka takeyi, zama ummu ta qarayi ta fuskance ta tace
"Autan Ummu sanar dani gaskia tsakaninki da Allah, na miki alqawarin zan yadda da komai zaki fad'a ke kuma kiji tsoron Allah ki sanar dani iya gaskiyan ki,Waye mahaifin wannan cikin?" da sauri ta d'ago ta kalleta tace
"Wallahil Azeem ummu ban tab'a tarawa da wani namiji ba, ciki kuwa harda mijina *ALI ABBAS* bazan miki qaryaba ummu bansan mafarin wannan cikin ba, ban kuma san ubanshi ba" jinjina kai ummu cikeda al'ajabin wannan lamarin, indai har Manga ta haihu yaro ze bayyanar da ubanshi, amma tafi zargin Ali Abbas ne keson ya rabu da Manga yanzu kuma, qwafa tayi tace
"Maza jeki ki kwanta ki huta, domin kuwa bacci nakeso kiyi, kar inji kin sanarwa kowa wannan maganar domin Ali Abbas shine ze karbi wannan yaron......."
Batace komai ba se kurun ta kwanta badan tayi bacci ba sedan batasan mema zatayi ba. A b'angaren Ali Abbas kuwa yana zuwa d'aki wani baqin ciki datakaici ya tarnaqe shi, wato daga zuwansu india har wani ya hurewa Manga kunne harya la hanta mata rayuwa, shidai wlhy yaji gabaki daya ta sire masa arai, amma baze iya jayayya da hukuncin ummu ba....."
Yanda Manga taga rana haka garin Allah ya waye mata, koda aka kawo breakfast ma ko kallonshi batayi ba, tayi mamakin dalilin Ummu na qin zuwa ta dubata, tasani koda batazoba kullum takan aiko azo aduba ta, sabida main dakinta ba'a shiga da wuri wuri se ta fito....tana tsakiya da tunanin tajiyo sallamar wata hadima, d'agawa tayi ta kalleta ita kuwa ta zube a wurin
"Ranki ya dad'e Inji Fulany wai kifito zaku fita" Ba musu ta miqe ta sanya hijab d'inta ta fito tabi bayan hadimar har suka isa gun mota ganin Ali Abbas a mota ya mugun qara tayar mata da hankali, kallon Ummu tayi tace kanta aqasa
"Barka da kwana ummu" janyota ajiki ummu tayi dayake tana baya tace
"Lafiya qalau Autan Ummu Hafsatu Manga, Allah ya miki Albarka,yaya jikin kuma?" qwallah ne ya taru a idonta ta kasa magana, seda suka hau hanya tace
"Yaa Ali barka da kwana" A daqile ya amsa da "Lafiya" a tak'aice Ummu bataji dad'in yanda ya mata ba sam, gabaki d'aya tausayin Manga takeji sannan kuma batasan tonuwar asirin yarinyar, ta kasa gane kan wannan al'amarin amma sam batawa Manga tunanin bin maza, am mata shaidar halaye na gari sedai ko wani abin dabaze wuce qaddara ba, a yanda tayi lissafi ma da yan fashin sukai mata fyade da tuni cikin yakai wata biyar ai koma fi tunda aiba yau bane amma wannan daga ina, girgiza kanta tayi tana jinjina tunanin da me martaba yayi kai tsaye na kawar da wasu en Gulmace Gulmace daka iya tasowa acikin masarautar lallai wannan shikadaine mafita agaresu baki d'aya...... kai tsaye gidan Ali Abbas dake Arqillah gandu suka wuce, a babban parlor suka sauka dama babu wani na buqata a gidan sannan akwai hadimai, bayan sun zauna ummu ta kalleshi da kyau tace
"Agaban idanka me martaba ya gama zartar da wannan hukuncin lallai ka kula da matarka sosai da sosai, Banasan wannan maganar da qara tashi harseta haihu tukunna, alwai abinda muke zargi akan wannan cikin kuma ta hakanne kurin zamu kai ga gano me ake ciki menene ma'anar wannan cikin,tunda yake tanada hadimai kwanaki biyu zaka musu anan sekayi biyu acan d'inma kayi biyu kana dai jina ko?" gyad'a mata kanshi yayi cikeda takaici ta miqe kawai tace
"Ki zauna anan barin wa huddyn waya, ai bakya riqa yawo ba bayan kince har jiri kike gani" kwantar da kanta tayi zaman jikin ummu, ta lumshe ido tanajin qaunar ummu har cikin ranta da ruhinta, mata me karamci da qaunarta..........Kallon ta sosai huddy tayi cikin dokawar qirji na kishi irin na mata bayan kwajin fitsarin daya mata ya fito kuma bincika yanayin al'adarta ta gano tayi tsallaken sati biyu be zoba ta kalli ummu tace
"Ummu juna biyu ne da ita na tsawon wata d'aya da satuka biyu" Washe baki ummu tayi aranta tace ashe an angwance a India" ta kalli huddy tace tana fad'ad'a murmushinta
"Lallai ma auta an gama girma, kije zanga en jikokina ta wurin auta, toki sani bana san kishiya,bazaku taru keda hudaisa kuna jeremun kishiyoyi ba muji zaki kawo, kinga yanzu me martaba bashida magana seta Ahasan yaga yarinya ze qyale tsohuwa" mayarda dubanta tayi zuwa ga huddy taci gaba "A rubuta mata magun gunan dazatasha tasamu sauqin wannan wahalan, tunda juna biyu beje ko ina ya kawo ba yasoma baiwa auta wahala, keni wannan koda mijine banayi,ze daddage yake baiwa Autan ummu wahala,ko Auta" sadda kanta tayi qasa qirjinta na wani irin mugun dokawa, harta ji jirin datakeji yana qaruwa, Innalillahi wa inna ilaihirraji'un itace kalmar data furta a hankali, huddy senyaqe takeyi tace aranta wato ni inacan ina fama da kaina duk ciwon danake shi kuwa honey moon yaje da matarshi dukda yake nice na kafe akan sena tafi da ita.......
"Zanje na rubuta sena baiwa abbin su Ahasan ya siyo mata, seta zauna anan kawai tunda ni bana zama" murmushi tayi tace
"Dama bazan bada autana ba, tana nan kusa dani inshaa Allah" murmushi tayi ta juya sabida basa wasa da ummu" a parlor ta sami Ali Abbas ta zauna kusa dashi ya kalleta
"Kin jima da yawa wani abinne?" murmushi tayi tace
"Kasan halin ummu indai akan sha'anin Manga ne, dukta tashi hankalinta amma nisam bazan gaya maka komai ba seka bani goro" murmushi yayi yace yana kallonta
"Zan bayar mana sanar dani menene? Wani abin farin cikinne ya samemu?" murmushi tayi itama tace
"Manga ce da ciki wata d'aya da sati biyu, kaga har strip dinma na pt nazo maka dashi,kace angwancewa akayi daga India?" wani kallo ya wurga mata wanda ta kasa fassara ma'anarsa,yace cikin mamakin
"Ciki kuma Manga kamar yaya?" murmushi tayi tace
"Kamar yanda kamata ciki mana Haba Abbin Ahasan sekace wani mugun labari kalli sauyawar fuskarka kodai kaso seka gama shan angwanci ciki yashiga,to wane angwanci kuma bayan wannan anje honey moon an dawo da goro" da qyar ya saisaita nutsuwar shi ya qaqaro murmushi cikin hikima ya wayance mata yasa dariya yace "Mamaki nake ciki da wuri haka" ita kuwa kasan zuciyarta ma takaicin sa takeji tace
"Kaine kayi shigar wuri baka jira ta tare ba, dole kaga ciki da sauri haka" murmushi yayi abinda be taba yiba fita da irin wannan jallabiyar dayake zaman gida da ita shi yayi, ya miqe kurun yayi ban garen fulani.....batanan da saurinta taje kaiwa sarki albishir shi kuwa ya shiga d'akin kai tsaye, kuka ya tarar tana yi ya cizgota ta miqe tsaye tana ganin yanayinshi ta shiga rudu murya na rawa ta furta
"Na rantse da girman wanda rayuwa ta take hannunsa ban taba sanin wani d'a namijiba, bansan inda aka samo wannan cikin ba" Wani mahaukacin mari Ali ya dire mata seda taga taurari ba adadi, yace
"Aruwa kika sha? Nace dan ubanki a ruwa kikasha cikin? Zaki kawomun hauka anan banza shegiya mara imani, dama duk shekarun nan maza kike bi ko? Se yanzu Allahu ya tona miki asiri, wlhy ki sani bazan tab'a lamuntar wannan jakancin ba, idan na karb'i cikin nan shege nake wlhy se duniya tasan abinda kika aikata, aini bawai wawa bane jahilar yarinya mara dangana kawai" kuka kawai tana bashi hakuri amma se fada yakeyi kallonshi ttayi
"Dan Allah ka dena daga murya yaa Ali kar bayi su jiyo mu, se maganan ya zam tsegumi acikin gidannan, wlhy ka yadda dani ban taba aikata wani abu ba da igiyar aurenka" wani marin ya kuma dire mata ya cafki wuyanta, seda taga mutuwa kusa sannan ya turata ta fad'i akasa ya juya, yana kawowa qofa ummu dataje me martaba na fada ta dawo ya gani a tsaye ta qura masa ido cikin tukuma, ze iya cewa wannan ne karonta na farko data tsoma idanuwan ta acikin nasa,murya a qasa tace
"Idan ka fitar da wannan maganar Allah ya isa ban yafe maka ba, ko zuhair ka sanarwa da zancen cikinnam cewar banaka bane ban yafe na, kuma bazan lamunci kace ba danka bane, da nakane kona waye kaji na gaya maka, wawa kawai dabesan ciwon kanshi ba" sadda kanshi yayi a qasa yawuce kawai batare da yayi magana ba sam......shiga cikin d'akin tayi ta zauna saman gado ta qurawa Manga ido tanaso ta gano gaskiyar ta, kallonta manga tayi tace tana kuka
"Wlhy Ummu bansan komai ba, ba abinda na sani ban tabayiba wlhy sharri ne kawai dan Allah ki taimakamun ki nuna masa gaskiaya ummuna dan Allah" Rungumeta kawai ummu tayi tana bubbuga bayanta a hankali.
Mom Nu'aiym
*HASKE WRITER'S ASSO. (Home of expert and perfect writer's)*
*👑ALI ABBAS👑*
*Billy Galadanchi*
*Sadaukarwa gareki qawa ta gari Fulany saddy*
13
D'agota tayi ta kalleta sosai tace "Auta kalleni nan dena kukan haka" d'agowa tayi ta kalleta sosai tace da ita
"Auta ki kwantar da hankalinki ki dena kukannan, ki nutsu ki gaya mun gaskia abinda nake san sani" gyad'a mata kanta tayi amar to taci gaba
"Sanar dani gaskia alokacin da yan fashi suka d'aukeku sun miki fyad'e?" tana kuka tace
"Wlhy Ummu basu samu nasara ba ko kad'an akaina, Humaira ce kawai suka samu sa'arta amma banda ita bakowa harni" jinjina kanta tayi tace
"Shirya tashi mu fita" ba musu suka fito a tare zuwa asibitin qwararru ta jiha, binciken dai ya nuna cikin watanshi d'aya da sati biyu kuka sosai Manga keyi harsuka dawo, wato dai ta tabbata cewar lallai cikinne da ita, to amma ta ina? Garin yaya hakan ta faru? Har suka isa bangaren su kuka takeyi, zama ummu ta qarayi ta fuskance ta tace
"Autan Ummu sanar dani gaskia tsakaninki da Allah, na miki alqawarin zan yadda da komai zaki fad'a ke kuma kiji tsoron Allah ki sanar dani iya gaskiyan ki,Waye mahaifin wannan cikin?" da sauri ta d'ago ta kalleta tace
"Wallahil Azeem ummu ban tab'a tarawa da wani namiji ba, ciki kuwa harda mijina *ALI ABBAS* bazan miki qaryaba ummu bansan mafarin wannan cikin ba, ban kuma san ubanshi ba" jinjina kai ummu cikeda al'ajabin wannan lamarin, indai har Manga ta haihu yaro ze bayyanar da ubanshi, amma tafi zargin Ali Abbas ne keson ya rabu da Manga yanzu kuma, qwafa tayi tace
"Maza jeki ki kwanta ki huta, domin kuwa bacci nakeso kiyi, kar inji kin sanarwa kowa wannan maganar domin Ali Abbas shine ze karbi wannan yaron......."
Batace komai ba se kurun ta kwanta badan tayi bacci ba sedan batasan mema zatayi ba. A b'angaren Ali Abbas kuwa yana zuwa d'aki wani baqin ciki datakaici ya tarnaqe shi, wato daga zuwansu india har wani ya hurewa Manga kunne harya la hanta mata rayuwa, shidai wlhy yaji gabaki daya ta sire masa arai, amma baze iya jayayya da hukuncin ummu ba....."
Yanda Manga taga rana haka garin Allah ya waye mata, koda aka kawo breakfast ma ko kallonshi batayi ba, tayi mamakin dalilin Ummu na qin zuwa ta dubata, tasani koda batazoba kullum takan aiko azo aduba ta, sabida main dakinta ba'a shiga da wuri wuri se ta fito....tana tsakiya da tunanin tajiyo sallamar wata hadima, d'agawa tayi ta kalleta ita kuwa ta zube a wurin
"Ranki ya dad'e Inji Fulany wai kifito zaku fita" Ba musu ta miqe ta sanya hijab d'inta ta fito tabi bayan hadimar har suka isa gun mota ganin Ali Abbas a mota ya mugun qara tayar mata da hankali, kallon Ummu tayi tace kanta aqasa
"Barka da kwana ummu" janyota ajiki ummu tayi dayake tana baya tace
"Lafiya qalau Autan Ummu Hafsatu Manga, Allah ya miki Albarka,yaya jikin kuma?" qwallah ne ya taru a idonta ta kasa magana, seda suka hau hanya tace
"Yaa Ali barka da kwana" A daqile ya amsa da "Lafiya" a tak'aice Ummu bataji dad'in yanda ya mata ba sam, gabaki d'aya tausayin Manga takeji sannan kuma batasan tonuwar asirin yarinyar, ta kasa gane kan wannan al'amarin amma sam batawa Manga tunanin bin maza, am mata shaidar halaye na gari sedai ko wani abin dabaze wuce qaddara ba, a yanda tayi lissafi ma da yan fashin sukai mata fyade da tuni cikin yakai wata biyar ai koma fi tunda aiba yau bane amma wannan daga ina, girgiza kanta tayi tana jinjina tunanin da me martaba yayi kai tsaye na kawar da wasu en Gulmace Gulmace daka iya tasowa acikin masarautar lallai wannan shikadaine mafita agaresu baki d'aya...... kai tsaye gidan Ali Abbas dake Arqillah gandu suka wuce, a babban parlor suka sauka dama babu wani na buqata a gidan sannan akwai hadimai, bayan sun zauna ummu ta kalleshi da kyau tace
"Agaban idanka me martaba ya gama zartar da wannan hukuncin lallai ka kula da matarka sosai da sosai, Banasan wannan maganar da qara tashi harseta haihu tukunna, alwai abinda muke zargi akan wannan cikin kuma ta hakanne kurin zamu kai ga gano me ake ciki menene ma'anar wannan cikin,tunda yake tanada hadimai kwanaki biyu zaka musu anan sekayi biyu acan d'inma kayi biyu kana dai jina ko?" gyad'a mata kanshi yayi cikeda takaici ta miqe kawai tace