Sashe 3
Ali Abbas Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wannan shafin nakine Bilqeess....Allahu ya saka miki da alkhairi keda dukkannin wanda suka yiwa yar uwata adu'a, ina roqon Allah ya baku me muku adu'a alokacin da kuke tsananin buqatar adu'ar, Allahu ya muku damu baki d'aya kyakyawan qarshe ya sanya kalmar shahada ta zamo kalma ta qarshe dazamu furta Ameennn....
02
Huddy bataji dad'in yanayin ALI Abbas ba kanya tafi gashi ko digit nata be karba ba sanda ya tafi, duk ta d'aura wannan laifin akan Manga shegiyar yarinya mayya,acewarta......
Gadanga kuwa seda yayi satinsa d'aya sannan ya dawowa gidan, Ya hadu da mahaifin huddy suka gaisa yake tambayarasa dalilin tafiyarsa cikin gaggawa ya shaida masa mahaifiyarsa ce batada lafiya,dama tun farko daukar sa aikin koyarwa da wankin motoci da baiwa fulawa ruwa ya sanar masa,yanada mara rafiya akai akai zena riqa zuwa gida zariya domin ya dubota......
A bangaren Ali Abbas kuwa sam shi bayasan halayyar Huddy, ya kula tanada tsauri akan talaka shi kuwa yafi tsanar wannan fannnin fiyeda komai,mace komai kissarta ze rayu da ita muddin tanada san Allah da manzansa, amma yana kyamatar masu kyamatar na qasa dasu, ba yanda zeyi sa zab'in iyaye dolenshi ya aureta......duk yanda yaso ya yakice tunanin Manga a ranshi gabaki d'aya abin ya faskara, gabaki d'aya wawtarta na bashi sha'awa beqi ya sanyata agaba ya dinga saurarar wawtar ta yana dariya ba, da zaran ya tuna sanda tace mai wai yaya me rawani se dariya ta taso masa, bare yanda tace dashi "Da lunch box nake zuwa skul" da zaran ya tuna girmanta da yanda zata rarumi kula zuwa skul seyayi murmushi, har mamakin kanshi yakeyi abune mawuyaci ka ganshi yana murmushi bawai yanada baqin rai bane nooo yakan jima beyi magana bane bare yayi murmushin ma.....
Zaune gadanga yake akan tebur dake tacikin harabar ajiye motocin gidan sanda Manga ta rugo da gudu tazo ta tsuguna kusa dashi tace
"Yaa mu'allim gadanga barga da safiya" kallonta yayi yana murmushi dayake jimawa yanayi idan ya soma sannan yace
"Manga ni wannan sunan yanamun tsawo, ki zab"a ko yaa mu'allim ko kuma yaa Gadanga" murmushi tayi
"Tunda baban Manga yace ze baka aurena gwara kawai ince yaa gadanga Ango" kallon mamaki ya mata sannan da qyar labb'ansa suka iya furta
"Aure kuma Mangan Innoh?" murmutayi
"Ea mana, haka yace da Innoh a gabana,wai soyayyya muke kuma kai malamine, dan haka kuwa ze bakani ka aura, yaa Gadanga ni qawayena sunada saurayi suna bani labarinsu amma ni banida saurayi, ance da saurayi ake soyayya tonikam kaine saurayina tunda Baban Manga da kanshi yace muna soyayya" kallonta ya tsayayi harta idar sannan ya kawadda kanshi gefe d'aya ya soma magana a hankali
"Manga banasan shirmen kinnan, kije ki nutsu kiyi karatu, bakince lauya zaki zamaba? Karna qarajin zancen soyayya a bakinki ko wani aure a yanzu, komai kikaji an fad'a sekinzo kina fad'a kokuma shi Baban Manga shine yace kizo ki sanar dani zancen da sukayi da Innoh?" narai narai tayi da ido sannan tace
"Baya so na fad'a ya gaya a gabana, aiba komai bane kai kad'ai na gayawa se qawata Nana khadeejah, kuma tace mun dace da juna tunda kai kyakyawane,nikam indai zamu aure ka dena tafiya kana barina tonama dena zuwa makarantar daga yau, bakaji yanda nake san in ganmu a tare ba" shiru yayi sabida ya fahimci yarinyar sanshi take batare datasan da hakan ba, sam batada wayo ko kad'an,shi tausayi take bashi sosai sabida ya kula duk inda zama ya had'a da mutane zatasha wahala kasancewar tanada surutu harna wawta,batasan meye sirri ba sam!!.....bece da ita komai ba harta bar wurin jin Innoh na qwala mata kira.....
Kwana bakwai kenan ta tafiyar Ali Abbas wani yammaci su gadanga sun idar da sallah a masallacin kofar gidan da isha,Ali Abbas ya qara dira a gidan, yau kam ajikin shigar qananun kaya yake dasukayi matuqar karb'ar fatar jikinshi....yayi kyau ainun yakuma qara haske da jiki ba laifi, Manga ce ta wangale masa gate d'in kasancewar Baban Manga yana masallaci har lokacin be fito ba, ita bata ganeshi ba shine ya ganeta yana parking ita kuwa harta qarasa rufe gate d'in zatai cikin gidansu tajiyo muryan shi
"Hafsatu Manga, zo mana" juyowa tayi babu wani duhu kamar yanda ba wadataccen hasken dazata ganeshi kai tsaye beside ranar cikin rawani yake,sedai muryan ya mata kamar ta wanda ta sani, takowa tayi tazo tace "Waye gani?" murmushi yayi yace
"Yayan kine Ali Abbas" washe baki tayi "Laa yaa me rawani yau kai kad'aine ina d'an banki to?" murmushi yayi yace
"Zance nazo gun Huddy ki kiramun ita" kallonshi ta d'anyi tana murmushi
"Nima nayi sabon saurayi sunanshi Gadanga yana masallaci, amma baya zuwar mun zance, zaku gaisa idan ka fito ko?"murmushin dai ya qarayi yace
"Lallai ma yarinya ke yanzu har wani saurayine dake, naji to idan na gama zanzo mu gaisa,yanzu maza kimun kiran huddy, ki sanar mata ina sauri ne" batace komai ba ta kwasa aguje zuwa cikin gidan, kowa yasan halinta dan haka ba wanda ya damu da yanda ta shigo aguje, ta daiyi sallama kanta isa parlor d'in, ba wanda ya ansa sallamar tata se Ummi datace
"Ke Mangan Inno me kikazoyi anan yanzu kuma,neman tsokana ko" kallonta tayi dama ita bawai ishashiyar nutsuwa ce da itaba tace
"Nikam dama mezan zo na muku yanzu, Wannan me rawaninne yace azo akira masa Aunty Hudaisa, kuma yace a sanara mata yana sauri ne karta dade" da sauri huddy ta miqe tsaye zuwa cikin dakin domin gyara kanta, ba wanda ya kuma bi ta kanta se kallon hujaima tayi tace
"Su hujaima musulman loko, ana nan ana karatun Allah badonshi ba sedon gudun bulalar yaa mu'allim" takaici hujaima taji tace
"Ummi kinji manga waiba dan Allah nake bitar karatu ba" kallonta ummi tayi zatai magana manga ta rigata
"kaji wawiya yo koni ai gudun bulala yake sanyawa nake bitar, ko babba kikaga yana zuwa makaranta yana bita idan dai beyi dan gudun duka ba dole zeyine dan gudun kar amar dariya" dariya ta baiwa ilahirin mutan parlor din ciki kuwa hadd hussy da farouk, suna shiri da hussy sosai kusan sa'anin junane, suna nan har huddy tafito ta wuce su....seda ta gama tsokana da sakasu dariya tukunna sannan ta fito a tsaye ta taddasu matsawa tayi kusa dasu tace
"yaa Ali kaga sarkin zagwad'i ta riga er aiken zuwa ko? Kan na gama fad'a ma ta miqe, kayi sa'an mace kyakyawa kam" mamakin surutunta yake sekace wacce aka aiko ji wani shirme,ya sani kuma huddy taji kunya danyama kula da hakan, se yace cikin siqar wasa
"Dama mana ina zagwad'i nazo ita me kikeso tayi ne? Nafita ai nida nazo" tab'e baki tayi
"To Allah shibar qauna,yaa Ali ni nayi nan" takama hanyar gidansu be tsaidata ba ya kalli huddy yace
"Huddy?" kallonshi tayi batai magana ba
"ki dena damuwa da maganganun manga idan kin kula batada nutsuwa kuma tanada tarin quruciya akanta, abu d'aya zan sanar miki shine ki dena dukanta,iyayenta bazasuji dad'i ba ina horonki daki girmama talaka, da wannan halin kadai zaki samu karbuwa a masarautar mu, da kuma birnin zuciyata" murmushi tayi har hushiryarta ta bayyana tace
"Zan kiyaye inshaa Allah" Mota ya bude ya dakko wata leda ya miqa mata, hannu biyu ta sanya ta karba sannan yace
" Akwai waya da sabon sim aciki, tawace ni kadai, koda wane lokaci ki kasance riqe da wayar banasan tarin msd calls ba'a daga ba, bana san ganin call waiting kuma gwara nini kadai, sauran kayan kuma duk nakine,kiyi hakuri ranar ina uzuri ban tsaya mun gaisa da ke ba" fara'arta ta fad'ad'a sannan tace
"yaa Ali nagode Allah ya qara girma da d'aukaka,Kariyar mahalicci tabika a duk inda kake, Allah ya sanya Alkhairi acikin tarayyarmu dakai, nagode sosai ba adadi Allah ya qara bud'i" murmushi yayi har cikin ranshi yanajin dad'in adu'ar huddy, yasani bezo da shiri. Santa ba, be kuma zo da shirin qiyayyarta ba sedai fa ya kula sosai soyayyar ta naso ta rinjaye shi,kyaunta yana burgeshi, kalamanta masu hikima na masa dad'i,tanada girmama mutane wannan ma ya masa...... A haka sukai sallama ya juya ya tafi......
Shiru gadanga yayi bayan ya gama jin bayanin Baban manga, tabbas baze iya yiwa baban manga musuba akan auren manga, kazalika sam baze iya cewa tsakanin santa da rashin santa wanne ne yakejiba, shidai abu daya ya sani bayasan rawar kan yarinyar,da uban surutun datake dashi, anso mutum ya auri mace me sirri yaya zeyi da auren Manga????? Da qyar ya iya tattaro nutsuwarshi yace
"Ba laifi Baban Manga, ina godiya sosai da karamci Amma ina roqon alfarma abani lokaci kasancewar takamammen wurin dazan ajiyeta banida shi gashi kuma se anyi suturu da sauransu, zanso kuma ta kammala karatunta tukunna" murmushi Baban manga yayi
"Babu komai gadanga, Allah yashige mana gaba,ya hore abin lalura, nidai alqawari d'aya zakamun shine ko bayan raina zaka auri manga, kadaiga manga batada wadatacciyar nutsuwa nayi mata sha'awarka ne sabida na kula duk abinda ka lurar da ita to tanabi, kaga kuwa zaka saisaita nutsuwarta inshaa Allahu" gadanga yaji tamkar an daura mai wani dutse aka, nauyin ya masa yawa matuqa,ina zeje da girman alqawari,kalmar aminta da qudurin baban manga tamasa nauyin fad'a a harshe wanda harya sanya yai shiru....
"Malam Gadanga kayi shiru, ina fatan baka tunanin inaso na maka dole ne?" murmushi gadanga yayi yaji kunya matuqa tamkar me koyon magana haka ya furta
"Ba haka bane Baban Manga, nayi alqawarin Inshaa Allahu zan auri Manga ko bayan ranka" dad'i yaji matuqa yashi masa albarka sannan suka shiga masallaci domin gabatar da sallah isha.....
Ko kad'an Gadanga be shirya aure ba yanzu, badan bayason manga ba sedan kawai yana ganin lokacin aurenshi beeyiba, mema ze cewa iyayenshi? Kodai kawai ya bari se an daura ya sanar dasu? Haka gadanga ya zauna cikin rashin sanin abinyi,tunaninshinya tsaya cak, yana matuqar dana sanin abubuwa da yawa, ya zanyi da manga???" wannan itace tambayar dayakewa kanshi ba qaqqautawa.......
*Bayan wata hudu*
02
Huddy bataji dad'in yanayin ALI Abbas ba kanya tafi gashi ko digit nata be karba ba sanda ya tafi, duk ta d'aura wannan laifin akan Manga shegiyar yarinya mayya,acewarta......
Gadanga kuwa seda yayi satinsa d'aya sannan ya dawowa gidan, Ya hadu da mahaifin huddy suka gaisa yake tambayarasa dalilin tafiyarsa cikin gaggawa ya shaida masa mahaifiyarsa ce batada lafiya,dama tun farko daukar sa aikin koyarwa da wankin motoci da baiwa fulawa ruwa ya sanar masa,yanada mara rafiya akai akai zena riqa zuwa gida zariya domin ya dubota......
A bangaren Ali Abbas kuwa sam shi bayasan halayyar Huddy, ya kula tanada tsauri akan talaka shi kuwa yafi tsanar wannan fannnin fiyeda komai,mace komai kissarta ze rayu da ita muddin tanada san Allah da manzansa, amma yana kyamatar masu kyamatar na qasa dasu, ba yanda zeyi sa zab'in iyaye dolenshi ya aureta......duk yanda yaso ya yakice tunanin Manga a ranshi gabaki d'aya abin ya faskara, gabaki d'aya wawtarta na bashi sha'awa beqi ya sanyata agaba ya dinga saurarar wawtar ta yana dariya ba, da zaran ya tuna sanda tace mai wai yaya me rawani se dariya ta taso masa, bare yanda tace dashi "Da lunch box nake zuwa skul" da zaran ya tuna girmanta da yanda zata rarumi kula zuwa skul seyayi murmushi, har mamakin kanshi yakeyi abune mawuyaci ka ganshi yana murmushi bawai yanada baqin rai bane nooo yakan jima beyi magana bane bare yayi murmushin ma.....
Zaune gadanga yake akan tebur dake tacikin harabar ajiye motocin gidan sanda Manga ta rugo da gudu tazo ta tsuguna kusa dashi tace
"Yaa mu'allim gadanga barga da safiya" kallonta yayi yana murmushi dayake jimawa yanayi idan ya soma sannan yace
"Manga ni wannan sunan yanamun tsawo, ki zab"a ko yaa mu'allim ko kuma yaa Gadanga" murmushi tayi
"Tunda baban Manga yace ze baka aurena gwara kawai ince yaa gadanga Ango" kallon mamaki ya mata sannan da qyar labb'ansa suka iya furta
"Aure kuma Mangan Innoh?" murmutayi
"Ea mana, haka yace da Innoh a gabana,wai soyayyya muke kuma kai malamine, dan haka kuwa ze bakani ka aura, yaa Gadanga ni qawayena sunada saurayi suna bani labarinsu amma ni banida saurayi, ance da saurayi ake soyayya tonikam kaine saurayina tunda Baban Manga da kanshi yace muna soyayya" kallonta ya tsayayi harta idar sannan ya kawadda kanshi gefe d'aya ya soma magana a hankali
"Manga banasan shirmen kinnan, kije ki nutsu kiyi karatu, bakince lauya zaki zamaba? Karna qarajin zancen soyayya a bakinki ko wani aure a yanzu, komai kikaji an fad'a sekinzo kina fad'a kokuma shi Baban Manga shine yace kizo ki sanar dani zancen da sukayi da Innoh?" narai narai tayi da ido sannan tace
"Baya so na fad'a ya gaya a gabana, aiba komai bane kai kad'ai na gayawa se qawata Nana khadeejah, kuma tace mun dace da juna tunda kai kyakyawane,nikam indai zamu aure ka dena tafiya kana barina tonama dena zuwa makarantar daga yau, bakaji yanda nake san in ganmu a tare ba" shiru yayi sabida ya fahimci yarinyar sanshi take batare datasan da hakan ba, sam batada wayo ko kad'an,shi tausayi take bashi sosai sabida ya kula duk inda zama ya had'a da mutane zatasha wahala kasancewar tanada surutu harna wawta,batasan meye sirri ba sam!!.....bece da ita komai ba harta bar wurin jin Innoh na qwala mata kira.....
Kwana bakwai kenan ta tafiyar Ali Abbas wani yammaci su gadanga sun idar da sallah a masallacin kofar gidan da isha,Ali Abbas ya qara dira a gidan, yau kam ajikin shigar qananun kaya yake dasukayi matuqar karb'ar fatar jikinshi....yayi kyau ainun yakuma qara haske da jiki ba laifi, Manga ce ta wangale masa gate d'in kasancewar Baban Manga yana masallaci har lokacin be fito ba, ita bata ganeshi ba shine ya ganeta yana parking ita kuwa harta qarasa rufe gate d'in zatai cikin gidansu tajiyo muryan shi
"Hafsatu Manga, zo mana" juyowa tayi babu wani duhu kamar yanda ba wadataccen hasken dazata ganeshi kai tsaye beside ranar cikin rawani yake,sedai muryan ya mata kamar ta wanda ta sani, takowa tayi tazo tace "Waye gani?" murmushi yayi yace
"Yayan kine Ali Abbas" washe baki tayi "Laa yaa me rawani yau kai kad'aine ina d'an banki to?" murmushi yayi yace
"Zance nazo gun Huddy ki kiramun ita" kallonshi ta d'anyi tana murmushi
"Nima nayi sabon saurayi sunanshi Gadanga yana masallaci, amma baya zuwar mun zance, zaku gaisa idan ka fito ko?"murmushin dai ya qarayi yace
"Lallai ma yarinya ke yanzu har wani saurayine dake, naji to idan na gama zanzo mu gaisa,yanzu maza kimun kiran huddy, ki sanar mata ina sauri ne" batace komai ba ta kwasa aguje zuwa cikin gidan, kowa yasan halinta dan haka ba wanda ya damu da yanda ta shigo aguje, ta daiyi sallama kanta isa parlor d'in, ba wanda ya ansa sallamar tata se Ummi datace
"Ke Mangan Inno me kikazoyi anan yanzu kuma,neman tsokana ko" kallonta tayi dama ita bawai ishashiyar nutsuwa ce da itaba tace
"Nikam dama mezan zo na muku yanzu, Wannan me rawaninne yace azo akira masa Aunty Hudaisa, kuma yace a sanara mata yana sauri ne karta dade" da sauri huddy ta miqe tsaye zuwa cikin dakin domin gyara kanta, ba wanda ya kuma bi ta kanta se kallon hujaima tayi tace
"Su hujaima musulman loko, ana nan ana karatun Allah badonshi ba sedon gudun bulalar yaa mu'allim" takaici hujaima taji tace
"Ummi kinji manga waiba dan Allah nake bitar karatu ba" kallonta ummi tayi zatai magana manga ta rigata
"kaji wawiya yo koni ai gudun bulala yake sanyawa nake bitar, ko babba kikaga yana zuwa makaranta yana bita idan dai beyi dan gudun duka ba dole zeyine dan gudun kar amar dariya" dariya ta baiwa ilahirin mutan parlor din ciki kuwa hadd hussy da farouk, suna shiri da hussy sosai kusan sa'anin junane, suna nan har huddy tafito ta wuce su....seda ta gama tsokana da sakasu dariya tukunna sannan ta fito a tsaye ta taddasu matsawa tayi kusa dasu tace
"yaa Ali kaga sarkin zagwad'i ta riga er aiken zuwa ko? Kan na gama fad'a ma ta miqe, kayi sa'an mace kyakyawa kam" mamakin surutunta yake sekace wacce aka aiko ji wani shirme,ya sani kuma huddy taji kunya danyama kula da hakan, se yace cikin siqar wasa
"Dama mana ina zagwad'i nazo ita me kikeso tayi ne? Nafita ai nida nazo" tab'e baki tayi
"To Allah shibar qauna,yaa Ali ni nayi nan" takama hanyar gidansu be tsaidata ba ya kalli huddy yace
"Huddy?" kallonshi tayi batai magana ba
"ki dena damuwa da maganganun manga idan kin kula batada nutsuwa kuma tanada tarin quruciya akanta, abu d'aya zan sanar miki shine ki dena dukanta,iyayenta bazasuji dad'i ba ina horonki daki girmama talaka, da wannan halin kadai zaki samu karbuwa a masarautar mu, da kuma birnin zuciyata" murmushi tayi har hushiryarta ta bayyana tace
"Zan kiyaye inshaa Allah" Mota ya bude ya dakko wata leda ya miqa mata, hannu biyu ta sanya ta karba sannan yace
" Akwai waya da sabon sim aciki, tawace ni kadai, koda wane lokaci ki kasance riqe da wayar banasan tarin msd calls ba'a daga ba, bana san ganin call waiting kuma gwara nini kadai, sauran kayan kuma duk nakine,kiyi hakuri ranar ina uzuri ban tsaya mun gaisa da ke ba" fara'arta ta fad'ad'a sannan tace
"yaa Ali nagode Allah ya qara girma da d'aukaka,Kariyar mahalicci tabika a duk inda kake, Allah ya sanya Alkhairi acikin tarayyarmu dakai, nagode sosai ba adadi Allah ya qara bud'i" murmushi yayi har cikin ranshi yanajin dad'in adu'ar huddy, yasani bezo da shiri. Santa ba, be kuma zo da shirin qiyayyarta ba sedai fa ya kula sosai soyayyar ta naso ta rinjaye shi,kyaunta yana burgeshi, kalamanta masu hikima na masa dad'i,tanada girmama mutane wannan ma ya masa...... A haka sukai sallama ya juya ya tafi......
Shiru gadanga yayi bayan ya gama jin bayanin Baban manga, tabbas baze iya yiwa baban manga musuba akan auren manga, kazalika sam baze iya cewa tsakanin santa da rashin santa wanne ne yakejiba, shidai abu daya ya sani bayasan rawar kan yarinyar,da uban surutun datake dashi, anso mutum ya auri mace me sirri yaya zeyi da auren Manga????? Da qyar ya iya tattaro nutsuwarshi yace
"Ba laifi Baban Manga, ina godiya sosai da karamci Amma ina roqon alfarma abani lokaci kasancewar takamammen wurin dazan ajiyeta banida shi gashi kuma se anyi suturu da sauransu, zanso kuma ta kammala karatunta tukunna" murmushi Baban manga yayi
"Babu komai gadanga, Allah yashige mana gaba,ya hore abin lalura, nidai alqawari d'aya zakamun shine ko bayan raina zaka auri manga, kadaiga manga batada wadatacciyar nutsuwa nayi mata sha'awarka ne sabida na kula duk abinda ka lurar da ita to tanabi, kaga kuwa zaka saisaita nutsuwarta inshaa Allahu" gadanga yaji tamkar an daura mai wani dutse aka, nauyin ya masa yawa matuqa,ina zeje da girman alqawari,kalmar aminta da qudurin baban manga tamasa nauyin fad'a a harshe wanda harya sanya yai shiru....
"Malam Gadanga kayi shiru, ina fatan baka tunanin inaso na maka dole ne?" murmushi gadanga yayi yaji kunya matuqa tamkar me koyon magana haka ya furta
"Ba haka bane Baban Manga, nayi alqawarin Inshaa Allahu zan auri Manga ko bayan ranka" dad'i yaji matuqa yashi masa albarka sannan suka shiga masallaci domin gabatar da sallah isha.....
Ko kad'an Gadanga be shirya aure ba yanzu, badan bayason manga ba sedan kawai yana ganin lokacin aurenshi beeyiba, mema ze cewa iyayenshi? Kodai kawai ya bari se an daura ya sanar dasu? Haka gadanga ya zauna cikin rashin sanin abinyi,tunaninshinya tsaya cak, yana matuqar dana sanin abubuwa da yawa, ya zanyi da manga???" wannan itace tambayar dayakewa kanshi ba qaqqautawa.......
*Bayan wata hudu*