Sashe 2
Ali Abbas Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Amma dai yaa mu'allim aiba kowane masu kud'in bane suke haka, Aunty huddy da maminta ne haka mu ai Ammin mu batawa talakawa wulaqanci kuma haka take gaya mata wulakanci ba kyau, meyi ma se an masa.... Murmushi ya sakarwa farouk yace
"Dama mana ai hakane farouk, ba kyau wulaqanta bayin Allah, kuma tunda kuke daraja d'an adam me kudi da talaka Aljannah zaku shiga inshaa Allah" narai narai hujaima tayi da ido tace
"To yaa mu'allim mu mamin mu fa? Wuta zataje itada da Aunty huddy sabida suna wulaqanci ko?" hannunta ya kamo duka biyu sannan yace
"Ba haka bane hujaima,Allah shine kad'ai yasan suwaye en wuta, sedai fa ana kyautata masu aikata kyawawan halaye samun rahamar ubangiji yayinda ake wa masu muna nan ayyuka zato mara kyau, yanada kyau d'an dama yasan meyakeyi, yakuma san yanda yake mu'amala da mutanen dake kewaye dashi, se kiga ana zatar masa shiga aljanna mad'aukakiya" shekarun hujaima sha uku amma tsaf ta gane me Gadanga ke nufii wannan ya sanya ta jinjina kanta ta furta a hankali
"Allah ka shiryar da mamina da Aunty hudaisa,ko zasu samu kyakyawan zato a wurin mutane" Ameen suka amsa gaba dayansu sannan sunaci gaba da karatun da sukeyi......
*Bayan wata biyu*
"Amma Ali Abbas zancen aure haka ze ci gaba dashan dukan ruwan sama bame rama masa, ayi haka kuwa, nidai na yanke shawarar had'aka da yarinyar gidan Aminina Alhj Mubarak hasan,dake garin kaduna sunanta Hudaisa kuma harna nema maka aurenta an kuma baka, seka shirya zuwa kaduna wani satin domin ku gaisa da kyau" lokaci d'aya Ali Abbas yaji ranshi ya baci, gashi sam baze taba iya yiwa Abin shi musu ba, murmushi ya qaqalo yace
"Mashaa Allah Abi,Allahu ya sanya Alkhairi ina matuqar godiya da karamci,Allah ya kara girma" sosai me martaba yaji dad'in wannan na'am da zabin shi da Ali yayi, ya dinga zuqaqa masa albarka ba iyaka......
Sosai gadanga kejin dad'in mu'amalar sa da Manga yarinya ta matuqar shiga ransa, yana matuqar ji da ita,tamkar wata qanwar sa haka ya dauketa, iyayenta ma suna girmamashi yana ganin qimarsu susan darajar d'an adam, kimanin watanninshi shida kenan agidan yana koyarda yara yana kuma baiwa fulawowin gidan ruwa, lokaci zuwa lokaci yakan tafi ganin gidan kuma baya tafiya seya kawo wakilinshi, duk kuwa sanda zeyi tafiyar to kuwa Manga da kuka suke rabuwa, da kyar take barin ya tafi wasu lokutan har qwalla take sakashi, ganin ita macece kuma gidan wani zata,wannan shine karonshi na 4 da zeyi tafiya tun bayan zuwan shi gidan, bazece ga ranar dazeyi tafiya batare datasha kuka ba harda majina, gashi dai ajinta 6 secondry amma wawta kamar me indai Manga ce.....
Yauma dai rigimar tafiyar akeyi, gabaki d'aya ta gama birkita masa lissafi, mahaifinta yazo yanata mata fad"a yayinda Inno se haquri take bashi, shi kamma ji yakeyi tamkar ya rufe ta da duka,yarinya tana girma tana cin qasa sekace wata er sha biyu kinada shekaru harsha bakwai amma bakisan inda ke miki ciwo ba,duk iya banbamin da Baba yayi dai manga seda gadanga ya mata dabara akn yafa kwana bakwai kwana biyu kacal zeyi sannan ta haqura ya tafi...
Kallon Innoh Baba yai yace "Indai Har wannan yaron gadanga ya dawo auren Manga zan bashi, bata yanda za'ayi ace ba soyayya a tsakanin su wannan lakuwar" kallon shi inno tayi sannan tace
"Banqi ta taka ba malam, amma fa bazeyu kabashi 'ya baka san dangin shiba ko d'aya"
"Amma ai inno kema kin shedi halin gadanga na qwarai, ke bakya ganin en manyan gidajennan ma se aiko masa suke da abin alkhairi suna saka yaransu yana koya musu karatun islama? Yaro me tsananin addini ina Manga zata samu irinshi?" shiru tayi sabida tasan halin Baban Manga indai ya tasarwa abu bame hanashi, tunda gashi ko zancen zuwa gidansu yaqi tunda ya samu matsala da en uwansa yau shekaru sha biyar kenan, ko Manga da sauran qannenta a nan aka haifesu,ko sunan Niger baya sanji........
Yaudai shirye shiryen tarar baqon Huddy akeyi, wanda zezo daga sokoto, d'an gidan sarkin musulmi, huddy se rawar kai akeyi, ana yadawa Ammin su faruk habaici a kaikaice,ita dai iya kacinta dariya kurun sabida tasan wannan tsarin Allah ne, kuma da Allah ya qaddari hussyn tace za'a aura ba makawa se anyi, da yardar Allah kuwa zata samu miji na gari ita d'inma subawai kwadayin su mulki ba......
Iya kwalliya da ado ansha su huddy, ba karya wani rantsatsen less ne a jikinta ruwan madara,an masa d'inkin gown play qasanta ya bude sosai,a saman wuyan anyi adon d'uwatsu pink colors da flowers masu kyau pink colors, dazeita tazo har gida tamata makeup, aka maka mata tauban aka mata lullub'i da mayafi pink color,tayi kyau matuqa......
Tunda yafito daga mota sanye da rawaninshi na saurata ya sungume imanin ilahirin mutanen dasuka fito waje tarbarsa ciki kuwa hadda uwar gayyar huddy, dukda yake acikin shiga ta saurata yake hadda rawani hakan baze hanaka ganin cikar hakittar saba da haiba, ga wani uban qwarjini daya ke dashi.. ...
Iso akai masa har cikin gidan bangaren masaukin baqi, aka wadatashi da kayan ciye ciye shida malam zuhair abokinshi, kallon ta yakeyi yyanda takeyin komai cikin nutsuwa a hankalo ta zauna a daya daga cikin kujerun dake parlor din,sannan cikin rausayar da kai tace dasu
"Muna muku barka da zuwa, muna kuma fatan hanya Alhamdulillah" kallonta yake yanaso ya hango inda takeda makusa har zuhair ya amsa mata gaisuwarta be ankare ba seda ya tabashi a hankali sannan ya saisaita nutsuwarshi yace
"Hudaisa mun sameku lapiya?" lumshe idanta tayi setaji tamkar fad'in duniyar nan babu wanda ya kaishi iya fadar sunanta
"Lapiya qalau Yaa Ali, yaya hanya da mutanen gida?" be ansataba se kallonta dayakeyi cikin nutsuwa yana nazartar halayenta, shiru ya ratsa parlor na kusan mintuna goma kan daga bisani yace da ita
"Mu zamu koma masauki se kuma gobe idan Allah ya kaimu, yanzu muna tattare da gajiyane, muna godiya da shimfid'ar fuska" murmushi tayi sannan tace
"Muke godiya da wannan ziyarar,Allah ya hutar da gajiya,ya kaiku masaukin ku lapiya" besan dalili ba seya tsinci kanshi da sakar mataurmushi har cikin ranshi yaji dad'in adu'arta agareshi, cikin qasaita ya miqe shima zuhair ya miqe, waje suka fito tayi musu rakiya har wurin motarsu, sunayin sallam sega Manga tazo ta tsaya tana kallonsu cikin quluwa Huddy tace
"ke mayyah wa kike kallo?" da sauri Manga ta shiga taitayinta shi kuma ALi seya ce akira masa ita, zuwa tayi ta duka tace dashi "Ina wuni yaa me rawani gani?" wani takaicine ya tarnaqe huddy jin wannan rainin hankalin datazo dashi wai yaa me rawani, yayinda shikam Yarima Ali da abokinshi zuhair dariya sosai ta basu suka kuwa dara abinsu, ya sake kallonta yace
"Sunana Ali amma mesa kika ce dani me rawani?" d'an d'ago kanta tayi ta kalleshi sannan tace
"Bansan sunanka yaa Ali ba ai, kuma naga rawanine akanka, shikamma wannan yaa d'an banki nake shirin ce dashi na ganshi sanye da suit" mamakin surutun ta zuhair keyi ba ruwanta da komai ita kam,da alama tanada quruciya,gyaran tsayuwarshi yayi yace
"Tokefa ya sunanki?" murmushi tayi sannan tace
"Hafsatu Manga sunana, amma kowa banda makarantar boko Manga yake kirana,kaima idan ka ganni kana kirana Manga kawai, sabida yaa Mu'allim gadanga kawai ke cemun Hafsat se en school kuma" dariya yayi yanzu kam har hakwaranshi suka bayyana gabaki daya yace
"To shi yaa m'uallim gadanga mesa bakice yadena ce miki hafsa ba?" wani far tai da idanta tace
"Shi d'in na dabanne ai, kowama yace Manga banda yaa gadanga yafi kowa iya fad'ar sunan" nanma dariya sukayi ta wawtarta huddy kawai ce taji wani bakin ciki, kasancewar ita se wani sha mata qamshi yake amma ji yanda yake biyewa Manga sakaryar yarinya yake biyewa haka....tsagaita dariyarsa yayi sannan yace
"To ni Hafsatu Manga zab riqa had'awa duka, ungo zoki karb'i na breakfast idan kinje skul" kallonshi tayi yana miqa mata kud'i sannan batare data karb'a ba tace
"Ni kullum Baba yana baiwa Innoh kud'in break ta bani, wani zubin ma da abincina nake zuwa, qawayena sutamun dariya waina girmi lunch boxx,niko ko'a jikina wlhy, kuma yaa gadanga ma yace kwad'ayi ba kyau, yana da kyau ka tsaya inda Allah ya ajiyeka, niba inda zankai wannan kud'in nagode sosai, zan gayawa Baba idan ka qara zuwa ya bud'e maka gate da wuri kanada kirki kaida yaa D'an banki" dariya gabaki dayansu suka saka, huddy se yaqe takeyi azuciyarta kamar ta shaqe shegiyar mangar can kuwa, ahaka sukai sallama suka bar gidan har sukaje masauki basu dena labarin Manga ba.....Manga ikon Allahh....
A b'angaren Manga kuwa suna wucewa huddy ta hau dukanta tana ce mata mayya, shegiyar yarinya in qara ganinki kusa da su baqina, yarinya sekace aljana,na tsani buzayennan wlhy, kune kuke kilewa kuna qwace mana mazaje me iyayin Tsiya lilis tamata kanta juya cikin gidan rai a bace.....
Washe gari kuwa su ALI na dira a qofar gidan manga ta kwaso a guje tana shesheka adaidai lokacin kuwa huddy ta dannowa wurin kai ta fito tararsu, bataga huddynba tasoma rattabe
"Yauwa yaa Ali,yaa Dan banki sannu da zuwa,dama zuwa nai na gayama ka, karkaga ban qara gaidaka ba, jiya naci duka a wurin anty huddy tace ba ruwana daku, karna qara gaidaku, abinda yasa na fada banso kuce banda kirki ne, gobe kona ganku bazan gaidaku ba kam inasan lafiyata" tsayawa kallonta kurun sukayi sega huddy tana zuwa ta bata kyakkyawan mari
"Bance karki qara zuwa kiwa mutane shirme anan ba,banza jaka?" kuka ta saka ta juya da gudu yayinda haka kawai Ali yaji ranshi ya matuqar b'aci yasha mur, bema shiga ciki ba suka gaisa yace sauri suke suka juya......
Vote If u enjoy this page.....ur comments are important than anything....
Mom Nu'aiym ce
[7/6, 8:07 AM] +234 706 571 7620: *Haske writer's Asso.(home of expert and perfect writer's)*
*👑ALI ABBAS 👑*
Billy galadanchi
Sadaukarwa gareki qawa ta gari *Fulany saddy*
"Dama mana ai hakane farouk, ba kyau wulaqanta bayin Allah, kuma tunda kuke daraja d'an adam me kudi da talaka Aljannah zaku shiga inshaa Allah" narai narai hujaima tayi da ido tace
"To yaa mu'allim mu mamin mu fa? Wuta zataje itada da Aunty huddy sabida suna wulaqanci ko?" hannunta ya kamo duka biyu sannan yace
"Ba haka bane hujaima,Allah shine kad'ai yasan suwaye en wuta, sedai fa ana kyautata masu aikata kyawawan halaye samun rahamar ubangiji yayinda ake wa masu muna nan ayyuka zato mara kyau, yanada kyau d'an dama yasan meyakeyi, yakuma san yanda yake mu'amala da mutanen dake kewaye dashi, se kiga ana zatar masa shiga aljanna mad'aukakiya" shekarun hujaima sha uku amma tsaf ta gane me Gadanga ke nufii wannan ya sanya ta jinjina kanta ta furta a hankali
"Allah ka shiryar da mamina da Aunty hudaisa,ko zasu samu kyakyawan zato a wurin mutane" Ameen suka amsa gaba dayansu sannan sunaci gaba da karatun da sukeyi......
*Bayan wata biyu*
"Amma Ali Abbas zancen aure haka ze ci gaba dashan dukan ruwan sama bame rama masa, ayi haka kuwa, nidai na yanke shawarar had'aka da yarinyar gidan Aminina Alhj Mubarak hasan,dake garin kaduna sunanta Hudaisa kuma harna nema maka aurenta an kuma baka, seka shirya zuwa kaduna wani satin domin ku gaisa da kyau" lokaci d'aya Ali Abbas yaji ranshi ya baci, gashi sam baze taba iya yiwa Abin shi musu ba, murmushi ya qaqalo yace
"Mashaa Allah Abi,Allahu ya sanya Alkhairi ina matuqar godiya da karamci,Allah ya kara girma" sosai me martaba yaji dad'in wannan na'am da zabin shi da Ali yayi, ya dinga zuqaqa masa albarka ba iyaka......
Sosai gadanga kejin dad'in mu'amalar sa da Manga yarinya ta matuqar shiga ransa, yana matuqar ji da ita,tamkar wata qanwar sa haka ya dauketa, iyayenta ma suna girmamashi yana ganin qimarsu susan darajar d'an adam, kimanin watanninshi shida kenan agidan yana koyarda yara yana kuma baiwa fulawowin gidan ruwa, lokaci zuwa lokaci yakan tafi ganin gidan kuma baya tafiya seya kawo wakilinshi, duk kuwa sanda zeyi tafiyar to kuwa Manga da kuka suke rabuwa, da kyar take barin ya tafi wasu lokutan har qwalla take sakashi, ganin ita macece kuma gidan wani zata,wannan shine karonshi na 4 da zeyi tafiya tun bayan zuwan shi gidan, bazece ga ranar dazeyi tafiya batare datasha kuka ba harda majina, gashi dai ajinta 6 secondry amma wawta kamar me indai Manga ce.....
Yauma dai rigimar tafiyar akeyi, gabaki d'aya ta gama birkita masa lissafi, mahaifinta yazo yanata mata fad"a yayinda Inno se haquri take bashi, shi kamma ji yakeyi tamkar ya rufe ta da duka,yarinya tana girma tana cin qasa sekace wata er sha biyu kinada shekaru harsha bakwai amma bakisan inda ke miki ciwo ba,duk iya banbamin da Baba yayi dai manga seda gadanga ya mata dabara akn yafa kwana bakwai kwana biyu kacal zeyi sannan ta haqura ya tafi...
Kallon Innoh Baba yai yace "Indai Har wannan yaron gadanga ya dawo auren Manga zan bashi, bata yanda za'ayi ace ba soyayya a tsakanin su wannan lakuwar" kallon shi inno tayi sannan tace
"Banqi ta taka ba malam, amma fa bazeyu kabashi 'ya baka san dangin shiba ko d'aya"
"Amma ai inno kema kin shedi halin gadanga na qwarai, ke bakya ganin en manyan gidajennan ma se aiko masa suke da abin alkhairi suna saka yaransu yana koya musu karatun islama? Yaro me tsananin addini ina Manga zata samu irinshi?" shiru tayi sabida tasan halin Baban Manga indai ya tasarwa abu bame hanashi, tunda gashi ko zancen zuwa gidansu yaqi tunda ya samu matsala da en uwansa yau shekaru sha biyar kenan, ko Manga da sauran qannenta a nan aka haifesu,ko sunan Niger baya sanji........
Yaudai shirye shiryen tarar baqon Huddy akeyi, wanda zezo daga sokoto, d'an gidan sarkin musulmi, huddy se rawar kai akeyi, ana yadawa Ammin su faruk habaici a kaikaice,ita dai iya kacinta dariya kurun sabida tasan wannan tsarin Allah ne, kuma da Allah ya qaddari hussyn tace za'a aura ba makawa se anyi, da yardar Allah kuwa zata samu miji na gari ita d'inma subawai kwadayin su mulki ba......
Iya kwalliya da ado ansha su huddy, ba karya wani rantsatsen less ne a jikinta ruwan madara,an masa d'inkin gown play qasanta ya bude sosai,a saman wuyan anyi adon d'uwatsu pink colors da flowers masu kyau pink colors, dazeita tazo har gida tamata makeup, aka maka mata tauban aka mata lullub'i da mayafi pink color,tayi kyau matuqa......
Tunda yafito daga mota sanye da rawaninshi na saurata ya sungume imanin ilahirin mutanen dasuka fito waje tarbarsa ciki kuwa hadda uwar gayyar huddy, dukda yake acikin shiga ta saurata yake hadda rawani hakan baze hanaka ganin cikar hakittar saba da haiba, ga wani uban qwarjini daya ke dashi.. ...
Iso akai masa har cikin gidan bangaren masaukin baqi, aka wadatashi da kayan ciye ciye shida malam zuhair abokinshi, kallon ta yakeyi yyanda takeyin komai cikin nutsuwa a hankalo ta zauna a daya daga cikin kujerun dake parlor din,sannan cikin rausayar da kai tace dasu
"Muna muku barka da zuwa, muna kuma fatan hanya Alhamdulillah" kallonta yake yanaso ya hango inda takeda makusa har zuhair ya amsa mata gaisuwarta be ankare ba seda ya tabashi a hankali sannan ya saisaita nutsuwarshi yace
"Hudaisa mun sameku lapiya?" lumshe idanta tayi setaji tamkar fad'in duniyar nan babu wanda ya kaishi iya fadar sunanta
"Lapiya qalau Yaa Ali, yaya hanya da mutanen gida?" be ansataba se kallonta dayakeyi cikin nutsuwa yana nazartar halayenta, shiru ya ratsa parlor na kusan mintuna goma kan daga bisani yace da ita
"Mu zamu koma masauki se kuma gobe idan Allah ya kaimu, yanzu muna tattare da gajiyane, muna godiya da shimfid'ar fuska" murmushi tayi sannan tace
"Muke godiya da wannan ziyarar,Allah ya hutar da gajiya,ya kaiku masaukin ku lapiya" besan dalili ba seya tsinci kanshi da sakar mataurmushi har cikin ranshi yaji dad'in adu'arta agareshi, cikin qasaita ya miqe shima zuhair ya miqe, waje suka fito tayi musu rakiya har wurin motarsu, sunayin sallam sega Manga tazo ta tsaya tana kallonsu cikin quluwa Huddy tace
"ke mayyah wa kike kallo?" da sauri Manga ta shiga taitayinta shi kuma ALi seya ce akira masa ita, zuwa tayi ta duka tace dashi "Ina wuni yaa me rawani gani?" wani takaicine ya tarnaqe huddy jin wannan rainin hankalin datazo dashi wai yaa me rawani, yayinda shikam Yarima Ali da abokinshi zuhair dariya sosai ta basu suka kuwa dara abinsu, ya sake kallonta yace
"Sunana Ali amma mesa kika ce dani me rawani?" d'an d'ago kanta tayi ta kalleshi sannan tace
"Bansan sunanka yaa Ali ba ai, kuma naga rawanine akanka, shikamma wannan yaa d'an banki nake shirin ce dashi na ganshi sanye da suit" mamakin surutun ta zuhair keyi ba ruwanta da komai ita kam,da alama tanada quruciya,gyaran tsayuwarshi yayi yace
"Tokefa ya sunanki?" murmushi tayi sannan tace
"Hafsatu Manga sunana, amma kowa banda makarantar boko Manga yake kirana,kaima idan ka ganni kana kirana Manga kawai, sabida yaa Mu'allim gadanga kawai ke cemun Hafsat se en school kuma" dariya yayi yanzu kam har hakwaranshi suka bayyana gabaki daya yace
"To shi yaa m'uallim gadanga mesa bakice yadena ce miki hafsa ba?" wani far tai da idanta tace
"Shi d'in na dabanne ai, kowama yace Manga banda yaa gadanga yafi kowa iya fad'ar sunan" nanma dariya sukayi ta wawtarta huddy kawai ce taji wani bakin ciki, kasancewar ita se wani sha mata qamshi yake amma ji yanda yake biyewa Manga sakaryar yarinya yake biyewa haka....tsagaita dariyarsa yayi sannan yace
"To ni Hafsatu Manga zab riqa had'awa duka, ungo zoki karb'i na breakfast idan kinje skul" kallonshi tayi yana miqa mata kud'i sannan batare data karb'a ba tace
"Ni kullum Baba yana baiwa Innoh kud'in break ta bani, wani zubin ma da abincina nake zuwa, qawayena sutamun dariya waina girmi lunch boxx,niko ko'a jikina wlhy, kuma yaa gadanga ma yace kwad'ayi ba kyau, yana da kyau ka tsaya inda Allah ya ajiyeka, niba inda zankai wannan kud'in nagode sosai, zan gayawa Baba idan ka qara zuwa ya bud'e maka gate da wuri kanada kirki kaida yaa D'an banki" dariya gabaki dayansu suka saka, huddy se yaqe takeyi azuciyarta kamar ta shaqe shegiyar mangar can kuwa, ahaka sukai sallama suka bar gidan har sukaje masauki basu dena labarin Manga ba.....Manga ikon Allahh....
A b'angaren Manga kuwa suna wucewa huddy ta hau dukanta tana ce mata mayya, shegiyar yarinya in qara ganinki kusa da su baqina, yarinya sekace aljana,na tsani buzayennan wlhy, kune kuke kilewa kuna qwace mana mazaje me iyayin Tsiya lilis tamata kanta juya cikin gidan rai a bace.....
Washe gari kuwa su ALI na dira a qofar gidan manga ta kwaso a guje tana shesheka adaidai lokacin kuwa huddy ta dannowa wurin kai ta fito tararsu, bataga huddynba tasoma rattabe
"Yauwa yaa Ali,yaa Dan banki sannu da zuwa,dama zuwa nai na gayama ka, karkaga ban qara gaidaka ba, jiya naci duka a wurin anty huddy tace ba ruwana daku, karna qara gaidaku, abinda yasa na fada banso kuce banda kirki ne, gobe kona ganku bazan gaidaku ba kam inasan lafiyata" tsayawa kallonta kurun sukayi sega huddy tana zuwa ta bata kyakkyawan mari
"Bance karki qara zuwa kiwa mutane shirme anan ba,banza jaka?" kuka ta saka ta juya da gudu yayinda haka kawai Ali yaji ranshi ya matuqar b'aci yasha mur, bema shiga ciki ba suka gaisa yace sauri suke suka juya......
Vote If u enjoy this page.....ur comments are important than anything....
Mom Nu'aiym ce
[7/6, 8:07 AM] +234 706 571 7620: *Haske writer's Asso.(home of expert and perfect writer's)*
*👑ALI ABBAS 👑*
Billy galadanchi
Sadaukarwa gareki qawa ta gari *Fulany saddy*