Sashe 4
Ali Abbas Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Su manga sunyi candy amma har yanzu ba hankali kam,se du'ayi kawai, Dama skul d'aya take zuwa dasu hussy, kuma tunda ga ranar da Baban manga yayiwa Gadanga maganar Manga be qarayiba shisa ma hankalinsa ya kwanta ya dena neman solution gaba daya.....yau yana zaune asaman bencin daya saba zama Baban Manga yamai sallama, suka gaisa cikeda girmama yace
"Gadanga dama zancen aurenka da Manga ne, kuma narigada na sanar da Alhj tuni, na sanar masa kaine ka zab'i seta kammala karatu gaba d'aya,tunda ta gama shine yamun zancen jiya akan na tuntub'eka aji ta bakinka" gabaki d'aya seda gadanga yaji tamkar ba'a duniya yake ba, sam be zata Baban Manga zewani gayawa me gidan su ba, yama rasa me zece seda yakuma cewa
"Gadanga kayi shiru" nisawa yayi yace
"Baban Manga ad'an qaramun lokaci, har yanzu ban gama had'awa manga kayan lefe ba, ban shirya wurin zamanmu a garinnan ba,tunda kaga ai nan nake aiki,bazeyiyu nakai Manga soba ba" nisawa yayi yace
"Gadanga na fahimci damuwarka amma Alhj yace anan bayan gidan zaku zauna tunda kaga ba samari ne dashiba se faruk kad'ai,kaga kanaci gaba da aikinka, yakuma ce bayasan ka mata komai shine ze muku har kai, A sanshima jibi juma'a daurin aure,sekayi haramar sanarwa iyayenka" qirjin gadangane yayi mugun dokawa yasani sarai iyayenshi bazasu tab'a amince masa auren manga ba, tayaya ma ze tunkaresu da wannan maganar tunda yanada zabinsu ajiye? Ina zekai girman alqawarin daya d'aukar wa Baban Manga? Ta ina ze soma juyawa kanshi? Gyaran zamanshi yayi yace
"Baban Manga, na sanar maka ni mutumin zaria ne a qauyen soba nake, banida kowa uwa ko uba duksun mutu, qanin mahaifinane zan masa waya yazo da kawuna, amma juma'a batai kadan ba, kuma ita Manga bata ra'ayin yin wani shagali ne? Zancen sadaqi dai zan biyawa kaina inada halin yin hakan" murmushi Baban Manga yayi yace
"Ka rabu da manga ba hankaline ya isheta ba,kuma ba wani bidi'a da za'ayi, iyayenka kuma ai badamuwa ko basu zoba dama nine waliyinka Alhj kuma shine waliyin Manga shine da kanshi ya fad'i hakan" murmushi Gadanga yayi ya masa godiya sannan ya wuce
Gadanga nasan Manga indan so,amma sam yasan aurenta babbar matsalane shida danginshi,juma'ar nan fa jibi ne? Saura kwana biyar aurenshi kenan yaya zeyi? Haka yayita saqawa da warwara harya daure dai ya sanarwa wanda ya dace suzo din.....
ALi Abbas ma da Huddy aurensu nanda 4 months masu zuwa, shirye shirye tsakanin sokoto da kaduna ba'a magana an shiryawa bukin auren ba kad'an ba komai yaji a yanayin shirye shirye lokaci kawai ake jira,dama huddy ba yarinya bace,itace 'ya babba acikin 'ya'yayen Alhj Tahir Maude,bashida manyan yara maza farouk ne kawai yaronshi namiji kuma qaramine sosai, yanzu haka huddy shekarunta 32 a duniya,mijin aurene bata samuba se yanzu........
*Rana Bata qarya*
Ranar juma'a kuwa kawun Gadanga da kuma qanin mahaifinshi sukazo daga soba aka d'aura auren Manga da gadanga, akan sadaki Naira dubu 30, duk yanda kike tunanin manga tashiga farin ciki abin ya wuce nan, sosai takeji da gadanga zama mu iya cewa tama fishi d'okin auren, anyi wuni ranar asabar batare da d'an uwan Baban Manga ko daya yazo ba kona Innoh kasancewar tunda ya baro gida be waiwaye su ba, Amarya tayi kyau ba laifi dama gata kyakyawa er jan buzu....a ranar aka miqa ta a BQ dake bayan gidan,wurin sahibinta gadanga.....
*Yazo mata da kaji na ban mamaki har guda uku gasassu da yoghurt,yakuma kawo mata sababbin kaya akwatuna guda uku wanda ta tsorata da gani, acewarshi shine yafi cancanta yawa matarshi suturu.....ranar dai duk surutu irinna manga batai masa shiba har tsokanarta yake yau ina bakin amma takasa koda kallonshi ne......
Duk yanda Gadanga yaso ya had'a jikinshi da Manga ya kasa, zancen gaskia yana mugun qyamar yanayin warin buzaye,kuma harya zamewa Manga halitta,duk kuwa dayake cewar sunada tsafta sosai wannan ne ya sanya yakecin abincin su,amma dai yana yin qmashin nasu be masa ba sam.....da wannan ya sanya bayama kwanciya wuri daya da ita....so kawai yakeyi ya zauna ya natsu seya riqa koyar da ita yanda zatayi amfani sa turarukan da yake so da kuma yanda zata riqa kwalliya kalar wacce yakeso ya shirya wayar da manga dan dai yana santa matuqa......haka suka rayu da juna cikin kulawa daso da qauna, zuwa yanzu gadanga ya gama sakankancewa yana qaunar mangan shi.....
*Bayan sati uku*
Waya akawa gadanga akan qanin mahaifinshi baida lafiya sosai, a haka ya shirya tafiya zuwa duboshi
Kallon shi Manga ta tsayayi tana kokarin tare hawayenta sabisa Inno ta sanar mata yanzu ta girma ta rage quruciya, amma sam ta kasa karo na farko daya rungumeta a jikinshi sosai yana bubbuga bayanta a hankali
"Kiyi hakuri Hilwa (sunan dayake kiranta dashi kenan tun bayan aurensu, kalmar Hilwa yana nufin kyakyawa kenan da Larabci) gobe zan dawo inshaa Allah" d'ago da kanta tayi tana hawaye tace
"Yaa Gadanga zan bika dan Allah,banaso ne ko kwana d'ayan kayi, ko masallaci kaje Allah Allah nake ka dawo, kuma idan ma kaje makarantar koyarwa har kuka nake,yaa gadanga kwana fa zakayi, dan Allah kaje dani" tausayinta yaji ba yanda za'ai ya tafi da ita duk yanda yaso,rungumeta ya qarayi
"Hilwa kiyi hakuri, daga zaran naje yau ni kad'ai duk inda zamu na miki alqawarin tare zamuje,bakya ganin nima zanyi kewarki sosai.... Girgiza masa kanta tayi
"yaa gadanga dan Allah kamun rai ka tafi dani, wlhy kewarka zata hallakani,bazan iya kwana gidan ni ka daibama" zuwa yanzu shima seda yayi kwallah, yace
"Haba Hilwa,kingafa abinda yasanya bazanje dake ba,banida kudin motan dazamuje mu biyu mu dawo shisa" d'ago kanta tayi "Zanje na karb'o kud'ad'ena dana baiwa Inno ajiya semu tafi tare" Hannayenshi duka biyu ya saka ya tallafi fuskarta yace
"Hilwa kinaso nayi fushi dake?" da sauri ta girgiza kai alamar aa, yace "Yauwa to idan bakyaso nayi,karna tab'aji kin dauki sirrinmu kin gayawa wani, idan inadashi sirrin mune, idan banidashi sirrin mune, idan muka samu sab'ani sirrin mune base kowa yajiba, idan muka tattauna matsalolin mu ma sirrin mune, ina fatar kin fahimceni sosai, banso koda su innoh kike gayawa sirrin mu,Zancen tafiya kuma kiyi hakuri namiki alqawarin wata rana tare zamuje" shiru tayi amma se kukan take haka ya saketa ya dauki jakarshi ya juya haryakai kofa taje ta rike mai kafa tana roqonshi
"yaa gadanga kewarka zata kasheni dan Allah kamun rai, kaje dani wlhy zanyi kewarka kuka bazemun magani ba" yaji tausayinta matuqa jiki a sanyaye yace
"Jeki dauki kayanki qwaya biyu kanna taro mana a daidaita sahun dazeje damu tasha kinji?" da sauri tayi ciki tana murna......
Sallama yawa Baban Manga ya wuce da sauri yabar unguwar akan babur...koda manga ta fito zatawa mahaifinta sallama seya sanar mata ai gadanga tuni ya wuce kuka kam tashashi, wayarta ta dauka tayi kiran wayar shi amma sam bata tafiya,tasha kuka kam a haka ta hakura tunda gadanga ya mata wayooo......
Ali Abbas yanata shirye shiryen zuwanshi kaduna gun huddy, ta isheshi da rigimar san zuwanshi akan tayi missing nashi sosai, duk yanda ya tuna huddynsa se yayi murmushi yarinyar tana burgeshi, banda halinta daya kula sam batasan talaka batada makusa a gunshi yana yabawa kyawawan d'abi'unta matuqa......kai tsaye gidansu ya wuce yana mamakin rashin samun wayarta dabayayi tunda ya taso, hakan ba d'abi arta bane indai yana hanya ta soma kiranshi kenan ba adadi...
Baban manga ya wangale mishi gate yana danna kanshi cikin gidan ya hangosu tsatsaye har huddynsu da maminsu,da amminsu su farouk dama Alhj tahir mahaifin su huddy....beyi qasa a gwiwa ba yaje ya gaidasu suka amsashi cikin sakin fuska, yanaso yayi shiru amma ganin Manga nata kuka ya sanya ya tsaya,yaga kuma kowa yayi cirko cirko ana kallonta bame magana har wacce yake tsammanin itace uwarta kasancewar suna matuqar d'iban kamanni....
"Hafsatu Manga lafiya dai kukan kuma na meye ne?" Alhj Tahir ne yace dashi
"Wlhy Ali mijintane ya b'ata yau sati uku, annemesa an sara, daga sunan zuwa gida gaida kawunsa da bashida lafiya yau sati uku,shine fa dukta tashi hankalinta haka" rike bakinshi yayi yace
"Manga tanada aurene dama?" murmushi yayi yace
"Dududu auren fa sati shida yanzu inaga, baka taba haduwa da mijin ba duk zuwanka,shine malamin dake koyar dasu karatun islama anan,yana kuma kula da shuke shuken gidan da wankin motoci" shiru ya d'anyi kanyace
"Naje gidansu kuwa?" cire hula daddyn huddy yayi yace "Nanfa d'aya mundai san dan Zaria ne a qauyen soba,amma babu wanda yasan gidansu, kawunsa ma da qanin mahaifinsa dasukazo daurin aure ni bazan shaidasu ba idan na gansu, Anan muka hadu yazo neman aikin koyarda yara islamiyyya kuma banan yake kwanaba, mundai yaba da halayyarshi ne muka baiwa manga shi a matsayin miji" nisawa yayi yace
"Hakane amma daddy mezai hana aje soban a bincika aji ai yafi ko kuwa?"
"Munje tashar motar dake kai mutum soba ma, babu zancen wai suna daukan record, yanzu zancenka zamubi muje soban tunda ba wani nisa zuwa zariya, akira idi direba" sosa kanshi yai yace
"Manga ai er gidanace, gwara nazo na biku daddy, na nemo mata mijinta kalli yanda take kuka hadda majina ko kunya" ya qarasa maganar cikin sigar tsokana, murmushi tayi kurin sabida tana cikin damuwa.....koda sukaje soba cewa aka musu babu wani suna me kamada wannan bare kawunnan shi ba wannan sunan a soba, kansu ya matuqar d'aurr suka juyo amma daddy ya hana a gayawa iyayenta kurin yace dasu dai basu gane iyayenshi ba a soba......
Haka dai Manga tayita hakuri tun ana jiran tsammanin dawowar gadanga har aka cire rai, kowa har daddy suka alaqanta b'atanshi da mutuwa, bazasu ce sun zagaye garin sobaba kuma a yanda malam gadanga yakeda sanin Allah baze tab'a yiyuwa ya aikata hakan ba, tunda da suka binciki yarinyar ba ba abinda ya tab'a shiga tsakaninsu idan ma mugunta ze mata aima shine ya nemi aurenta ba kumama ai daya ajiye takardar sakinta ya gudu, suna dai sakaran hatsari yayi bame kawo labarinshi, matsalar kuma har wanda yake kawowa ya wakilceshi idan baya nan ya sanar musu cewar baida labarin gadanga......
"Gadanga dama zancen aurenka da Manga ne, kuma narigada na sanar da Alhj tuni, na sanar masa kaine ka zab'i seta kammala karatu gaba d'aya,tunda ta gama shine yamun zancen jiya akan na tuntub'eka aji ta bakinka" gabaki d'aya seda gadanga yaji tamkar ba'a duniya yake ba, sam be zata Baban Manga zewani gayawa me gidan su ba, yama rasa me zece seda yakuma cewa
"Gadanga kayi shiru" nisawa yayi yace
"Baban Manga ad'an qaramun lokaci, har yanzu ban gama had'awa manga kayan lefe ba, ban shirya wurin zamanmu a garinnan ba,tunda kaga ai nan nake aiki,bazeyiyu nakai Manga soba ba" nisawa yayi yace
"Gadanga na fahimci damuwarka amma Alhj yace anan bayan gidan zaku zauna tunda kaga ba samari ne dashiba se faruk kad'ai,kaga kanaci gaba da aikinka, yakuma ce bayasan ka mata komai shine ze muku har kai, A sanshima jibi juma'a daurin aure,sekayi haramar sanarwa iyayenka" qirjin gadangane yayi mugun dokawa yasani sarai iyayenshi bazasu tab'a amince masa auren manga ba, tayaya ma ze tunkaresu da wannan maganar tunda yanada zabinsu ajiye? Ina zekai girman alqawarin daya d'aukar wa Baban Manga? Ta ina ze soma juyawa kanshi? Gyaran zamanshi yayi yace
"Baban Manga, na sanar maka ni mutumin zaria ne a qauyen soba nake, banida kowa uwa ko uba duksun mutu, qanin mahaifinane zan masa waya yazo da kawuna, amma juma'a batai kadan ba, kuma ita Manga bata ra'ayin yin wani shagali ne? Zancen sadaqi dai zan biyawa kaina inada halin yin hakan" murmushi Baban Manga yayi yace
"Ka rabu da manga ba hankaline ya isheta ba,kuma ba wani bidi'a da za'ayi, iyayenka kuma ai badamuwa ko basu zoba dama nine waliyinka Alhj kuma shine waliyin Manga shine da kanshi ya fad'i hakan" murmushi Gadanga yayi ya masa godiya sannan ya wuce
Gadanga nasan Manga indan so,amma sam yasan aurenta babbar matsalane shida danginshi,juma'ar nan fa jibi ne? Saura kwana biyar aurenshi kenan yaya zeyi? Haka yayita saqawa da warwara harya daure dai ya sanarwa wanda ya dace suzo din.....
ALi Abbas ma da Huddy aurensu nanda 4 months masu zuwa, shirye shirye tsakanin sokoto da kaduna ba'a magana an shiryawa bukin auren ba kad'an ba komai yaji a yanayin shirye shirye lokaci kawai ake jira,dama huddy ba yarinya bace,itace 'ya babba acikin 'ya'yayen Alhj Tahir Maude,bashida manyan yara maza farouk ne kawai yaronshi namiji kuma qaramine sosai, yanzu haka huddy shekarunta 32 a duniya,mijin aurene bata samuba se yanzu........
*Rana Bata qarya*
Ranar juma'a kuwa kawun Gadanga da kuma qanin mahaifinshi sukazo daga soba aka d'aura auren Manga da gadanga, akan sadaki Naira dubu 30, duk yanda kike tunanin manga tashiga farin ciki abin ya wuce nan, sosai takeji da gadanga zama mu iya cewa tama fishi d'okin auren, anyi wuni ranar asabar batare da d'an uwan Baban Manga ko daya yazo ba kona Innoh kasancewar tunda ya baro gida be waiwaye su ba, Amarya tayi kyau ba laifi dama gata kyakyawa er jan buzu....a ranar aka miqa ta a BQ dake bayan gidan,wurin sahibinta gadanga.....
*Yazo mata da kaji na ban mamaki har guda uku gasassu da yoghurt,yakuma kawo mata sababbin kaya akwatuna guda uku wanda ta tsorata da gani, acewarshi shine yafi cancanta yawa matarshi suturu.....ranar dai duk surutu irinna manga batai masa shiba har tsokanarta yake yau ina bakin amma takasa koda kallonshi ne......
Duk yanda Gadanga yaso ya had'a jikinshi da Manga ya kasa, zancen gaskia yana mugun qyamar yanayin warin buzaye,kuma harya zamewa Manga halitta,duk kuwa dayake cewar sunada tsafta sosai wannan ne ya sanya yakecin abincin su,amma dai yana yin qmashin nasu be masa ba sam.....da wannan ya sanya bayama kwanciya wuri daya da ita....so kawai yakeyi ya zauna ya natsu seya riqa koyar da ita yanda zatayi amfani sa turarukan da yake so da kuma yanda zata riqa kwalliya kalar wacce yakeso ya shirya wayar da manga dan dai yana santa matuqa......haka suka rayu da juna cikin kulawa daso da qauna, zuwa yanzu gadanga ya gama sakankancewa yana qaunar mangan shi.....
*Bayan sati uku*
Waya akawa gadanga akan qanin mahaifinshi baida lafiya sosai, a haka ya shirya tafiya zuwa duboshi
Kallon shi Manga ta tsayayi tana kokarin tare hawayenta sabisa Inno ta sanar mata yanzu ta girma ta rage quruciya, amma sam ta kasa karo na farko daya rungumeta a jikinshi sosai yana bubbuga bayanta a hankali
"Kiyi hakuri Hilwa (sunan dayake kiranta dashi kenan tun bayan aurensu, kalmar Hilwa yana nufin kyakyawa kenan da Larabci) gobe zan dawo inshaa Allah" d'ago da kanta tayi tana hawaye tace
"Yaa Gadanga zan bika dan Allah,banaso ne ko kwana d'ayan kayi, ko masallaci kaje Allah Allah nake ka dawo, kuma idan ma kaje makarantar koyarwa har kuka nake,yaa gadanga kwana fa zakayi, dan Allah kaje dani" tausayinta yaji ba yanda za'ai ya tafi da ita duk yanda yaso,rungumeta ya qarayi
"Hilwa kiyi hakuri, daga zaran naje yau ni kad'ai duk inda zamu na miki alqawarin tare zamuje,bakya ganin nima zanyi kewarki sosai.... Girgiza masa kanta tayi
"yaa gadanga dan Allah kamun rai ka tafi dani, wlhy kewarka zata hallakani,bazan iya kwana gidan ni ka daibama" zuwa yanzu shima seda yayi kwallah, yace
"Haba Hilwa,kingafa abinda yasanya bazanje dake ba,banida kudin motan dazamuje mu biyu mu dawo shisa" d'ago kanta tayi "Zanje na karb'o kud'ad'ena dana baiwa Inno ajiya semu tafi tare" Hannayenshi duka biyu ya saka ya tallafi fuskarta yace
"Hilwa kinaso nayi fushi dake?" da sauri ta girgiza kai alamar aa, yace "Yauwa to idan bakyaso nayi,karna tab'aji kin dauki sirrinmu kin gayawa wani, idan inadashi sirrin mune, idan banidashi sirrin mune, idan muka samu sab'ani sirrin mune base kowa yajiba, idan muka tattauna matsalolin mu ma sirrin mune, ina fatar kin fahimceni sosai, banso koda su innoh kike gayawa sirrin mu,Zancen tafiya kuma kiyi hakuri namiki alqawarin wata rana tare zamuje" shiru tayi amma se kukan take haka ya saketa ya dauki jakarshi ya juya haryakai kofa taje ta rike mai kafa tana roqonshi
"yaa gadanga kewarka zata kasheni dan Allah kamun rai, kaje dani wlhy zanyi kewarka kuka bazemun magani ba" yaji tausayinta matuqa jiki a sanyaye yace
"Jeki dauki kayanki qwaya biyu kanna taro mana a daidaita sahun dazeje damu tasha kinji?" da sauri tayi ciki tana murna......
Sallama yawa Baban Manga ya wuce da sauri yabar unguwar akan babur...koda manga ta fito zatawa mahaifinta sallama seya sanar mata ai gadanga tuni ya wuce kuka kam tashashi, wayarta ta dauka tayi kiran wayar shi amma sam bata tafiya,tasha kuka kam a haka ta hakura tunda gadanga ya mata wayooo......
Ali Abbas yanata shirye shiryen zuwanshi kaduna gun huddy, ta isheshi da rigimar san zuwanshi akan tayi missing nashi sosai, duk yanda ya tuna huddynsa se yayi murmushi yarinyar tana burgeshi, banda halinta daya kula sam batasan talaka batada makusa a gunshi yana yabawa kyawawan d'abi'unta matuqa......kai tsaye gidansu ya wuce yana mamakin rashin samun wayarta dabayayi tunda ya taso, hakan ba d'abi arta bane indai yana hanya ta soma kiranshi kenan ba adadi...
Baban manga ya wangale mishi gate yana danna kanshi cikin gidan ya hangosu tsatsaye har huddynsu da maminsu,da amminsu su farouk dama Alhj tahir mahaifin su huddy....beyi qasa a gwiwa ba yaje ya gaidasu suka amsashi cikin sakin fuska, yanaso yayi shiru amma ganin Manga nata kuka ya sanya ya tsaya,yaga kuma kowa yayi cirko cirko ana kallonta bame magana har wacce yake tsammanin itace uwarta kasancewar suna matuqar d'iban kamanni....
"Hafsatu Manga lafiya dai kukan kuma na meye ne?" Alhj Tahir ne yace dashi
"Wlhy Ali mijintane ya b'ata yau sati uku, annemesa an sara, daga sunan zuwa gida gaida kawunsa da bashida lafiya yau sati uku,shine fa dukta tashi hankalinta haka" rike bakinshi yayi yace
"Manga tanada aurene dama?" murmushi yayi yace
"Dududu auren fa sati shida yanzu inaga, baka taba haduwa da mijin ba duk zuwanka,shine malamin dake koyar dasu karatun islama anan,yana kuma kula da shuke shuken gidan da wankin motoci" shiru ya d'anyi kanyace
"Naje gidansu kuwa?" cire hula daddyn huddy yayi yace "Nanfa d'aya mundai san dan Zaria ne a qauyen soba,amma babu wanda yasan gidansu, kawunsa ma da qanin mahaifinsa dasukazo daurin aure ni bazan shaidasu ba idan na gansu, Anan muka hadu yazo neman aikin koyarda yara islamiyyya kuma banan yake kwanaba, mundai yaba da halayyarshi ne muka baiwa manga shi a matsayin miji" nisawa yayi yace
"Hakane amma daddy mezai hana aje soban a bincika aji ai yafi ko kuwa?"
"Munje tashar motar dake kai mutum soba ma, babu zancen wai suna daukan record, yanzu zancenka zamubi muje soban tunda ba wani nisa zuwa zariya, akira idi direba" sosa kanshi yai yace
"Manga ai er gidanace, gwara nazo na biku daddy, na nemo mata mijinta kalli yanda take kuka hadda majina ko kunya" ya qarasa maganar cikin sigar tsokana, murmushi tayi kurin sabida tana cikin damuwa.....koda sukaje soba cewa aka musu babu wani suna me kamada wannan bare kawunnan shi ba wannan sunan a soba, kansu ya matuqar d'aurr suka juyo amma daddy ya hana a gayawa iyayenta kurin yace dasu dai basu gane iyayenshi ba a soba......
Haka dai Manga tayita hakuri tun ana jiran tsammanin dawowar gadanga har aka cire rai, kowa har daddy suka alaqanta b'atanshi da mutuwa, bazasu ce sun zagaye garin sobaba kuma a yanda malam gadanga yakeda sanin Allah baze tab'a yiyuwa ya aikata hakan ba, tunda da suka binciki yarinyar ba ba abinda ya tab'a shiga tsakaninsu idan ma mugunta ze mata aima shine ya nemi aurenta ba kumama ai daya ajiye takardar sakinta ya gudu, suna dai sakaran hatsari yayi bame kawo labarinshi, matsalar kuma har wanda yake kawowa ya wakilceshi idan baya nan ya sanar musu cewar baida labarin gadanga......