Sashe 33
Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Da yamma ya samu ya fita don anyi masa waya ana nemansa, yana fita Jabeer yayo mata waya yana waje, nan ta shirya ta ja hannun Nawaz suka fita. Bayan sun gaisa Jabeer yace "Hibbah banji inda shawarar ku ta tsaya ba akan sa ranar nan, sauraronki nake yi na samu Aunty Aysha naji bakinku yazo d'aya itama tace wai zata tattauna da Umma, abinda yasa na dame ki ni mutum ne mai d'aukar abinda nake so da mahimmanci ban son shiririta a al'amurana, idan kina ganin abin bazai yiwu ba ki fad'a min gaskiya kawai kar ki b'oye min" tayi d'an murmushi "kasan ba nike da kaina ba kuma nayi maka bayanin komai bani zan aurar da kaina ba, amma ka samu Alhaji Ku tattauna kaji ta bakinsa," "to naji dad'in hakan, kar kiga zak'ewata ina sonki da yawa shi yasa nake nuna miki damuwata kuma nasan kema kina sona, zan sameshi in Allah ya yarda."
Faheem ya dawo ya huce su, Nawaz ya bishi don taryarshi, al'adarsa kenan komai yake yi da yaji motar Daddy'n shi ya dawo to saiya taro shi, Faheem ya saba mishi da hakan yakan ji dad'i aranshi sosai.
Tayi ajiyar zuciya Faheem mai sata cikin rud'ani in dai ta ganshi sai komai ya sauya mata in a parlor take ta gudu d'aki, in tana tafiya ne taji kamar anyi mata dabaibayi dole take tsayawa sai ya huce sannan ta cigaba, ya katse mata tunani "ina son mu gaisa da yayan nan namu amma naga kamar bai da son mu'amala da mutane, a k'alla ya sha wucemu anan yasan kuma ina zuwa wajenki ne don na aureki amma ko duban inda muke baya yi bare ko hannu ya d'aga min, ni kuma inason mu gaisa dashi ya sanni sosai don yasan shima yana da ruwa da tsaki a cikin maganar aurenki tunda a hannunsa kike zaune" "gaskiya ne kuma mutumin kirki ne, kawai dai allah ne bai nufa zaku gaisa d'in ba sannan na fahimci bai da wani ra'ayi akan shiga maganar aure na tunda bai tab'a yin magana akan hakan ba, amma nasan idan lokaci yayi zai yi."
Ya gyada kansa "shikenan Allah ya tabbatar da alkhari na gode" ya bata wani k'unshi a rufe a takarda. "Kai baka gajiya yau da gobe sai Allah," "Ana gajiya da masoyi ne?" Mutuminta ne ya huce su a mota, Faruq d'an rikicin duniya da da inda zata je data gudu sai ya tafi saita dawo domin zai sa ta a gaba ne kawai sai ya sata kuka.
Sukayi sallama ta shigo gida, ta huce shi a cikin motar kamar bata ganshi ba, ya dad'a k'uluwa kishi ke cinsa kamar masifa, wai wannan Jabeer da jaraba tsiya yake duk yadda ya tozarta Hibbah a gabansa bai hakuri ba.
Ya fito yana take mata baya ya janyo mayafinta ba shiri ta yo baya kamar zata fad'i ranta a b'axe ta kalleshi zallar masifa ta gani a idanunsa yau ta tab'o Faruq, mai cin zalinta a bulus bare da dalili. Ya nannad'e mayafin a hannusa tana ja ta kasa k'wacewa, ya kuwa murd'e hannunta ta rintse idanunta ji tayi kamar zai b'allata tayi wata 'yar k'ara "wayyo Allah na!" Abinda ta tsana kenan wannan rashin mutuncin da Faruq yake yi mata tana d'aukarsa tsabar tsana ce da rashin galihu. "Zan nuna miki mahaukacin kishi na akanshi zan iya komai tunda kika jawo mutumin nan duk da irin tozarcin da nayi miki a gabansa ashe tsugunno bata k'are ba, matuk'ar na k'ara ganinki dashi sai na miki rashin mutuncin da baki tab'a zato ba, don ji nayi kamar nasa bindiga na harbi k'ok'on kansa." Faheem ne ya fito yaji kuma furucin Faru$q sarai amma yayi kamar bai san su ba yayi wucewarsa, wani bak'in ciki taji ya k'ulleta kamar ta fad'i ta mutu wajen. Babu mutumin da a duniya bata son mutuncinta ya zube a wajensa kamar Faheem tana ganin girmansa, gashi a yau yaji ya gani hujja ce da zai d'ora zarginsa akan gaskiya tana mu'amala da Faruq bawai iyakar soyayya ba, wani tunanin zai yi don Faruq dai bashi da halin k'warai akan 'ya mace, gashi ya rik'e hannunta gam bata da wani sauran mutunci a idanun Faheem, wannan wace irin *RAYUWA* ce...............
*#JUMMA'AT MUBARAK TO YOU ALL😍😍🤝*
*by*
*Mamyn Najmah*
[10/26, 9:25 PM] Maman Najma Author P1: 📝🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓
*RAYUWA* page3⃣7⃣
*NA*
*MAMYN NAJMAH*
🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓
*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*
D.B.W.A
*DEDICATED TO AYSHA ALIYU GARKUWA*
Faheem ya dawo ya huce su, Nawaz ya bishi don taryarshi, al'adarsa kenan komai yake yi da yaji motar Daddy'n shi ya dawo to saiya taro shi, Faheem ya saba mishi da hakan yakan ji dad'i aranshi sosai.
Tayi ajiyar zuciya Faheem mai sata cikin rud'ani in dai ta ganshi sai komai ya sauya mata in a parlor take ta gudu d'aki, in tana tafiya ne taji kamar anyi mata dabaibayi dole take tsayawa sai ya huce sannan ta cigaba, ya katse mata tunani "ina son mu gaisa da yayan nan namu amma naga kamar bai da son mu'amala da mutane, a k'alla ya sha wucemu anan yasan kuma ina zuwa wajenki ne don na aureki amma ko duban inda muke baya yi bare ko hannu ya d'aga min, ni kuma inason mu gaisa dashi ya sanni sosai don yasan shima yana da ruwa da tsaki a cikin maganar aurenki tunda a hannunsa kike zaune" "gaskiya ne kuma mutumin kirki ne, kawai dai allah ne bai nufa zaku gaisa d'in ba sannan na fahimci bai da wani ra'ayi akan shiga maganar aure na tunda bai tab'a yin magana akan hakan ba, amma nasan idan lokaci yayi zai yi."
Ya gyada kansa "shikenan Allah ya tabbatar da alkhari na gode" ya bata wani k'unshi a rufe a takarda. "Kai baka gajiya yau da gobe sai Allah," "Ana gajiya da masoyi ne?" Mutuminta ne ya huce su a mota, Faruq d'an rikicin duniya da da inda zata je data gudu sai ya tafi saita dawo domin zai sa ta a gaba ne kawai sai ya sata kuka.
Sukayi sallama ta shigo gida, ta huce shi a cikin motar kamar bata ganshi ba, ya dad'a k'uluwa kishi ke cinsa kamar masifa, wai wannan Jabeer da jaraba tsiya yake duk yadda ya tozarta Hibbah a gabansa bai hakuri ba.
Ya fito yana take mata baya ya janyo mayafinta ba shiri ta yo baya kamar zata fad'i ranta a b'axe ta kalleshi zallar masifa ta gani a idanunsa yau ta tab'o Faruq, mai cin zalinta a bulus bare da dalili. Ya nannad'e mayafin a hannusa tana ja ta kasa k'wacewa, ya kuwa murd'e hannunta ta rintse idanunta ji tayi kamar zai b'allata tayi wata 'yar k'ara "wayyo Allah na!" Abinda ta tsana kenan wannan rashin mutuncin da Faruq yake yi mata tana d'aukarsa tsabar tsana ce da rashin galihu. "Zan nuna miki mahaukacin kishi na akanshi zan iya komai tunda kika jawo mutumin nan duk da irin tozarcin da nayi miki a gabansa ashe tsugunno bata k'are ba, matuk'ar na k'ara ganinki dashi sai na miki rashin mutuncin da baki tab'a zato ba, don ji nayi kamar nasa bindiga na harbi k'ok'on kansa." Faheem ne ya fito yaji kuma furucin Faru$q sarai amma yayi kamar bai san su ba yayi wucewarsa, wani bak'in ciki taji ya k'ulleta kamar ta fad'i ta mutu wajen. Babu mutumin da a duniya bata son mutuncinta ya zube a wajensa kamar Faheem tana ganin girmansa, gashi a yau yaji ya gani hujja ce da zai d'ora zarginsa akan gaskiya tana mu'amala da Faruq bawai iyakar soyayya ba, wani tunanin zai yi don Faruq dai bashi da halin k'warai akan 'ya mace, gashi ya rik'e hannunta gam bata da wani sauran mutunci a idanun Faheem, wannan wace irin *RAYUWA* ce...............
*#JUMMA'AT MUBARAK TO YOU ALL😍😍🤝*
*by*
*Mamyn Najmah*
[10/26, 9:25 PM] Maman Najma Author P1: 📝🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓
*RAYUWA* page3⃣7⃣
*NA*
*MAMYN NAJMAH*
🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓
*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*
D.B.W.A
*DEDICATED TO AYSHA ALIYU GARKUWA*