Sashe 42
Jininmu Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ruqayyan da kallon mamaki tabi Rufaida don tana da yakinin Rufaida ta fara cin ganye ne.
Girki Rufaida ta dora jallop din shinkafa da taji kayan lambu,da suke a fridge,sai kuma lemon abarba data hada,bata yi tsammanin Rukayya zata iya shigowa tayata ba yasa ita ma bata maida kai a hakan ba dan danan ta gama ta zubawa mijinta nasa daban da zai aiko a ansar masa yadda yake yi tun bayan aurensu daganan ta kawo musu nasu ta aje musu a dining ta karaso cikin falon ta sanar musu da ga abincinsu data samesu kowacce ta hakimce a kujera duk sun kwarkwanta suna kallo abinsu sanyin Ac na ratsasu
"Umma ga abincinku can a dining kona kawo muku nan" ta furta babu wacce ta kalleta saima dogon tsaki da suka ja mata
Ganin haka yasa ta barin inda suke ta ta shige dakinta tayi wanka ta shirya cikin atamfarta kalar lemon green da brown daganan tayi sallah falon dake dakinta ta dawo ta kunna TV ta fara kallo ta dauki wayarta ta kunna data suka fara chat da Nasiba Shehu Garba class mate din ta sosai suke chat suna labarin makaranta,bayan Nasiba ta gama cakakin bata fadamusu bikinta ba sai abakin Samiha suka ji can Nasiba tace
"Ke ban baki labari ba Sir Nura ashe Saliha Nasir budurwarsa ce har ankai kudin nagani ina so"
Emoji na mamaki Rufaida ta tura mata kafin tace
"Ke wai da gaske kike kawata,Saliha dai dana sani"
"Kwarai kuwa,Saliha Nasir mutuniya da suke dabi da Sir nura"
"To Allah ya sanya Alkhairi,idan sa ranar bikin yayi dai dai da zuwana gida zanje bikin ai Saliha nida ita da amana"
Rufaida ta rubuta ta tura mata
Nasiba ta turo mata Voice note ta bude taji Nasibar nace wa
"Kai da mun jidadi to Allah yasa,baki cemin ina Sir AbdulRahman ba"
Voice note din ta mayar mata ita ma da cewa
"Ya na ina badai har ansa ranar aurenku keda shi ba"
Zuwa can Nasiba ta dawo mata da amsa
"A'a ko 'daya,amma dai ansakamin rana a Adamawa zanyi aure, wata makwabciyarmu to dan Yayanta zan aura,da yazo gidanta muka hadu,shima anan Abujar yake aiki a central Bank"
Rufaida ta sake tura mata da voice note din
"Wow kice gidan kudi burinki ya cika"
"Murmushi Nasiba ta turo mata na emoji ta kara yi mata voice
"Rufaida kenan kudin da ba baka za" a rikayi kana yawo dasu ba,kedai kawai addu'ar samun miji nagari da kwanciyar hankali bayan auren,danta kudin miji ba kwanciyar hankali aina banza ne gwara ma ace talaka ka aura indai zai mutuntaka"
Voice Rufaida ta sake tura mata
"Haka ne kawata,Allah ya baku zaman lafiya ya tabbatar da Alkhairinsa"
Ganin wayarta na kara alamun kira yana shigowa Wahid ne mai kiran tana kokarin dagawa ta katse
" yasa tayi saurin cewa Nasiba zamuyi chat anjima" Nasiba ta rubuto mata
"OK akwai labari dama inason fada miki"
Da haka ta kashe data tana kokarin bin kiran wani wani ya sake shigowa
"Assalamu Alaikum matata"
Jin muryarsa ya sata murmushi
"Wa'alaikumus salam mai gida ya aiki"
"Alhamdulillah,yanzu kofur Bala ya tawo amsar abinci ki hado da Plat da yawa yau Kabir yace da abincin ki zaiyi launch,dafatan kingama aikin lafiya kuma baigaji dake ba"
"Murmushi tayi jin maganar mijin nata
"To sai yazo nagama komai"
"Yawwa farin ciki na da fatan kin Zubawa su Umma tun dazu"
Tayi saurin ce masa
"Eh ya mijina"
Yace ok take care bye ina aiki yanzu"
Tace masa"agama lafiya take care to u my regard to Yaya Kabir
Da ganan ta katse wayar ta mike ta nufi kitchen ta hada abincin a basket ta dawo falon inda tasa mesu nan ta barsu
"Sannu da hutawa Umma" Rufaida tace tana zama kujerar dake gefen tasu ta aje basket din kusa da ita batayi tunanin zasu amsa musu ba ita ma ta share su jin alamar kararrawar kofar falon na motsi ya sata zura hijabin da ta fito dashi a hannu ta dauki basket din sukw gaisa da kofur bala ta mika masa basket din ta dawo ciki ta zauna inda ta tashi tanaji suna yi mata habaici amma bata saurare su ba ta cigaba da kallonta
Ruqayya ce cikin tsawa ta fara magana tana kallon Rufaida
"Ke yar masu samu tafi iyawa ina ne matsugunnunmu,ko bamu da shi"
Rufaida ta kai muryarta kasa dan yanzu taga rashin kyautawar nuna musu masaukinsu amma dai bata ga fuska ba zata iya cewa tace
"Kiyi hakuri Ruqayya na manta wallahi da kin shiga ciki kin wuce wani corridor to daki na farko shine naku"
Tsaki Ruqayya taja ta mike ta shige ciki Rufaida ma mikewa tayi ta shige ciki,tanason tanbayar Umma ko sun ci abinci amma tana tsoron abinda zaije ya dawo"
Bayan wata 8
Haka rayuwa ta cigaba da tafiya da Rufaida da yanzu take da ciki Na Wata 6 , tsananin hakuri take duk a wannan lokacin da surikartata da kanwar mijinta zaman su da ita kullum dai cin mutunci ne gareta duk yadda take kyautata musu,dan har lokacin basu tafi ba,Ruqayya ce kawai taje gida yin jarabawar jamb tana gamawa kuma ta dawo
shikansa Wahid yana kallon abinda akewa matar tasa sau tari sai dai bai isa yace wani abu ba,ba tun hidima iya yi yana yi musu dan albashin na watan da mahaifiyartasa suka zo yana dauka dinkunan sawa yayi wa mahaifiyar tasa dasu,Ruqayya ko duk yadda ta kai da shishshige masa baya koda saurararta don shi soyayya ba ta damesa ba koda ma auren nata zaiyi matar da ya aura ma da yake sonta baiyi soyayya da ita ba ta azo a gani saboda rashin lokaci bare kuma yayi da Ruqayya,Rukayya kuwa tana kara jin son Wahid har ranta ganin yana da halin mai kyau zaman da suke yanzu take kara fahimtarsa, shiyasa take kokarin shige masa ko zai sota dukda tanada samari amma halayyar Wahid tana burgeta musamman yanzu da take ganin zaman su da matar shi tana nuna kulawarsa ga matar tasa,sau tari tana mamakin hakurin Rufaida dan ko ta tarar suna fira da Wahid din da ita suna zaune bata koda saurararsu zata koma ciki abinta wanda gaskiya da ita ce baza ta iya ba,ita ko Rufaida rashin zabi shike sawa ta koma ciki don tanada kishi da idan ta zauna ba zata hakura da abinda zata ga Ruqayya zata riqa ce masa ba a gabanta alhalin bata ga anfanin maganar ba idan tace ba zata hakuran ba don namiji ba'a shaidarsa ko kusa,ba zata ce nata bazai so wata ba bayan ita idan tayi hakan ba ta yiwa kanta adalci ba,yanzu ga cikin jikinta shiyasa ma bata son zama a cikin su saboda karsuyi abinda zai jawo mata bacin rai.
ABDULRA'UF
Sai a page na gaba zamu waiwaya bangaransa Insha Allah.
SadiyaKhalil.
Dan Allah Ku rika yin share,wani groups din.*JININMU 'DAYA*
By Sadiya Khalil❤️
43
Wannan page naku ne
Amina Muhammad baso
Safiyya Galadanci
Aisha Umar Ibrahim
Nagode da gudunmawarku gareni bisa son cigabana kuyi yadda kuke so da shafin nan Allah ya bar zumunci🖤
ABDULRA'UF
"Ra'uf meke damunka" Shureim yayi maganar da yake zaune a kujerar dake kallon ta Ra'uf a office din Ra'uf din
Kansa ya dago ya kalli Shureim da murmushinsa yace
"Mai ka gani?"
Shureim ya girgiza kansa kawai yace "komai ma Ra'uf ,kana tunanin zaka shiga wata damuwa na kasa fahimta,nasan komai damuwarka ta soyayya ce,Ahmad ya fadamin komai,Ra'uf dan Allah ka cire damuwarka,tunda Ahmad ya sanarmin ita ta riga da tayi aurema yarinyar,ka cire ta a zuciyarka please ka samu wata ka aura ga kanwata nan Ruwaydah kaje ka nemi aurenta indai kana santa"
Murmushi Ra'uf yayi ya maida dubensa kaco kam ga Shureim ya soma cewa
"Shureim ba soyayyar Rufaida ce damuwa ta ba illah iyaka sanin dalilin hanani aurenta shine damuwata,amma ni aure a yanzu haka baya gaba na,sai dai bazan ki Ruwaydah ba amma ba tsari aure yanzu a tsarina sai nan gaba
Tausayi Ra'uf ya bawa Shureim saboda shima yanajin zafin soyayya yanzu haka saboda yanasan Inteesar sosai saidai ya kasa furta mata saboda yana tsoron karta ki amincewa da soyayyarsa,ga soyayyarta da ke nuqurqusar zuciyarsa a kullum,dole ya tausayawa Ra'uf danshi sunyi soyayya ma suna da shirin aure aka rabasu ya dai daure ya kauda tunaninsa yace
" Eh aboki na nasan da ciwo ravuwa da masoyi amma hakuri zakayi ka cigaba dayi kuma Allah yasa rabuwar tafi zama alkhairi sannan ka cigaba da addu'ar neman zabin Allah a rayuwarka"
Ra'uf ya jidadin nasihar abokin nasa Shureim abokine nagari,shiyasa yake alfahari da abokin nasa da murmushi ya kalli Shureim yace
"Nagode aboki na"
"Haba babu komai aboki na damuwarka ta wace da zan iya fidda ma damuwarka da nayi wallahi amma zan cigaba da tayaka addu'a,tun sanda na fahimci baka da walwala a kwanakin nan kuma naji baka kara yimin maganar budurwarka ta kasarku ba,shine yasa nayi tunanin ko akwai abinda ya faru da soyayyarku shine yasa nakasa hakura har saida na tanbayi Ahmad ko yasan meke damunka ya fadamin shine yasanar dani komai,nasan zafin so Ra'uf nima kullum ina cikinsa zullumi na kar na fadawa Inteesar ta kasa amincewa dani" Shureim ya karasa maganar da rarraunar murya
Dafa sa Ra'uf yayi yace
"Haba abokina karka damu zata amince dakai yau zanje gidansu Inteesar na sanar mata da soyayyar da kake yi mata nasan zata amince"
Shureim ya murmusa yace
"Kai abokina ina godiya sosai"
"Haba aboki na karka damu komai nayi ma kacancanta da ayi ma ne"
Cewar Ra'uf
Da haka suka sauya fira ta aiyukansu har zuwa wani lokaci
Girki Rufaida ta dora jallop din shinkafa da taji kayan lambu,da suke a fridge,sai kuma lemon abarba data hada,bata yi tsammanin Rukayya zata iya shigowa tayata ba yasa ita ma bata maida kai a hakan ba dan danan ta gama ta zubawa mijinta nasa daban da zai aiko a ansar masa yadda yake yi tun bayan aurensu daganan ta kawo musu nasu ta aje musu a dining ta karaso cikin falon ta sanar musu da ga abincinsu data samesu kowacce ta hakimce a kujera duk sun kwarkwanta suna kallo abinsu sanyin Ac na ratsasu
"Umma ga abincinku can a dining kona kawo muku nan" ta furta babu wacce ta kalleta saima dogon tsaki da suka ja mata
Ganin haka yasa ta barin inda suke ta ta shige dakinta tayi wanka ta shirya cikin atamfarta kalar lemon green da brown daganan tayi sallah falon dake dakinta ta dawo ta kunna TV ta fara kallo ta dauki wayarta ta kunna data suka fara chat da Nasiba Shehu Garba class mate din ta sosai suke chat suna labarin makaranta,bayan Nasiba ta gama cakakin bata fadamusu bikinta ba sai abakin Samiha suka ji can Nasiba tace
"Ke ban baki labari ba Sir Nura ashe Saliha Nasir budurwarsa ce har ankai kudin nagani ina so"
Emoji na mamaki Rufaida ta tura mata kafin tace
"Ke wai da gaske kike kawata,Saliha dai dana sani"
"Kwarai kuwa,Saliha Nasir mutuniya da suke dabi da Sir nura"
"To Allah ya sanya Alkhairi,idan sa ranar bikin yayi dai dai da zuwana gida zanje bikin ai Saliha nida ita da amana"
Rufaida ta rubuta ta tura mata
Nasiba ta turo mata Voice note ta bude taji Nasibar nace wa
"Kai da mun jidadi to Allah yasa,baki cemin ina Sir AbdulRahman ba"
Voice note din ta mayar mata ita ma da cewa
"Ya na ina badai har ansa ranar aurenku keda shi ba"
Zuwa can Nasiba ta dawo mata da amsa
"A'a ko 'daya,amma dai ansakamin rana a Adamawa zanyi aure, wata makwabciyarmu to dan Yayanta zan aura,da yazo gidanta muka hadu,shima anan Abujar yake aiki a central Bank"
Rufaida ta sake tura mata da voice note din
"Wow kice gidan kudi burinki ya cika"
"Murmushi Nasiba ta turo mata na emoji ta kara yi mata voice
"Rufaida kenan kudin da ba baka za" a rikayi kana yawo dasu ba,kedai kawai addu'ar samun miji nagari da kwanciyar hankali bayan auren,danta kudin miji ba kwanciyar hankali aina banza ne gwara ma ace talaka ka aura indai zai mutuntaka"
Voice Rufaida ta sake tura mata
"Haka ne kawata,Allah ya baku zaman lafiya ya tabbatar da Alkhairinsa"
Ganin wayarta na kara alamun kira yana shigowa Wahid ne mai kiran tana kokarin dagawa ta katse
" yasa tayi saurin cewa Nasiba zamuyi chat anjima" Nasiba ta rubuto mata
"OK akwai labari dama inason fada miki"
Da haka ta kashe data tana kokarin bin kiran wani wani ya sake shigowa
"Assalamu Alaikum matata"
Jin muryarsa ya sata murmushi
"Wa'alaikumus salam mai gida ya aiki"
"Alhamdulillah,yanzu kofur Bala ya tawo amsar abinci ki hado da Plat da yawa yau Kabir yace da abincin ki zaiyi launch,dafatan kingama aikin lafiya kuma baigaji dake ba"
"Murmushi tayi jin maganar mijin nata
"To sai yazo nagama komai"
"Yawwa farin ciki na da fatan kin Zubawa su Umma tun dazu"
Tayi saurin ce masa
"Eh ya mijina"
Yace ok take care bye ina aiki yanzu"
Tace masa"agama lafiya take care to u my regard to Yaya Kabir
Da ganan ta katse wayar ta mike ta nufi kitchen ta hada abincin a basket ta dawo falon inda tasa mesu nan ta barsu
"Sannu da hutawa Umma" Rufaida tace tana zama kujerar dake gefen tasu ta aje basket din kusa da ita batayi tunanin zasu amsa musu ba ita ma ta share su jin alamar kararrawar kofar falon na motsi ya sata zura hijabin da ta fito dashi a hannu ta dauki basket din sukw gaisa da kofur bala ta mika masa basket din ta dawo ciki ta zauna inda ta tashi tanaji suna yi mata habaici amma bata saurare su ba ta cigaba da kallonta
Ruqayya ce cikin tsawa ta fara magana tana kallon Rufaida
"Ke yar masu samu tafi iyawa ina ne matsugunnunmu,ko bamu da shi"
Rufaida ta kai muryarta kasa dan yanzu taga rashin kyautawar nuna musu masaukinsu amma dai bata ga fuska ba zata iya cewa tace
"Kiyi hakuri Ruqayya na manta wallahi da kin shiga ciki kin wuce wani corridor to daki na farko shine naku"
Tsaki Ruqayya taja ta mike ta shige ciki Rufaida ma mikewa tayi ta shige ciki,tanason tanbayar Umma ko sun ci abinci amma tana tsoron abinda zaije ya dawo"
Bayan wata 8
Haka rayuwa ta cigaba da tafiya da Rufaida da yanzu take da ciki Na Wata 6 , tsananin hakuri take duk a wannan lokacin da surikartata da kanwar mijinta zaman su da ita kullum dai cin mutunci ne gareta duk yadda take kyautata musu,dan har lokacin basu tafi ba,Ruqayya ce kawai taje gida yin jarabawar jamb tana gamawa kuma ta dawo
shikansa Wahid yana kallon abinda akewa matar tasa sau tari sai dai bai isa yace wani abu ba,ba tun hidima iya yi yana yi musu dan albashin na watan da mahaifiyartasa suka zo yana dauka dinkunan sawa yayi wa mahaifiyar tasa dasu,Ruqayya ko duk yadda ta kai da shishshige masa baya koda saurararta don shi soyayya ba ta damesa ba koda ma auren nata zaiyi matar da ya aura ma da yake sonta baiyi soyayya da ita ba ta azo a gani saboda rashin lokaci bare kuma yayi da Ruqayya,Rukayya kuwa tana kara jin son Wahid har ranta ganin yana da halin mai kyau zaman da suke yanzu take kara fahimtarsa, shiyasa take kokarin shige masa ko zai sota dukda tanada samari amma halayyar Wahid tana burgeta musamman yanzu da take ganin zaman su da matar shi tana nuna kulawarsa ga matar tasa,sau tari tana mamakin hakurin Rufaida dan ko ta tarar suna fira da Wahid din da ita suna zaune bata koda saurararsu zata koma ciki abinta wanda gaskiya da ita ce baza ta iya ba,ita ko Rufaida rashin zabi shike sawa ta koma ciki don tanada kishi da idan ta zauna ba zata hakura da abinda zata ga Ruqayya zata riqa ce masa ba a gabanta alhalin bata ga anfanin maganar ba idan tace ba zata hakuran ba don namiji ba'a shaidarsa ko kusa,ba zata ce nata bazai so wata ba bayan ita idan tayi hakan ba ta yiwa kanta adalci ba,yanzu ga cikin jikinta shiyasa ma bata son zama a cikin su saboda karsuyi abinda zai jawo mata bacin rai.
ABDULRA'UF
Sai a page na gaba zamu waiwaya bangaransa Insha Allah.
SadiyaKhalil.
Dan Allah Ku rika yin share,wani groups din.*JININMU 'DAYA*
By Sadiya Khalil❤️
43
Wannan page naku ne
Amina Muhammad baso
Safiyya Galadanci
Aisha Umar Ibrahim
Nagode da gudunmawarku gareni bisa son cigabana kuyi yadda kuke so da shafin nan Allah ya bar zumunci🖤
ABDULRA'UF
"Ra'uf meke damunka" Shureim yayi maganar da yake zaune a kujerar dake kallon ta Ra'uf a office din Ra'uf din
Kansa ya dago ya kalli Shureim da murmushinsa yace
"Mai ka gani?"
Shureim ya girgiza kansa kawai yace "komai ma Ra'uf ,kana tunanin zaka shiga wata damuwa na kasa fahimta,nasan komai damuwarka ta soyayya ce,Ahmad ya fadamin komai,Ra'uf dan Allah ka cire damuwarka,tunda Ahmad ya sanarmin ita ta riga da tayi aurema yarinyar,ka cire ta a zuciyarka please ka samu wata ka aura ga kanwata nan Ruwaydah kaje ka nemi aurenta indai kana santa"
Murmushi Ra'uf yayi ya maida dubensa kaco kam ga Shureim ya soma cewa
"Shureim ba soyayyar Rufaida ce damuwa ta ba illah iyaka sanin dalilin hanani aurenta shine damuwata,amma ni aure a yanzu haka baya gaba na,sai dai bazan ki Ruwaydah ba amma ba tsari aure yanzu a tsarina sai nan gaba
Tausayi Ra'uf ya bawa Shureim saboda shima yanajin zafin soyayya yanzu haka saboda yanasan Inteesar sosai saidai ya kasa furta mata saboda yana tsoron karta ki amincewa da soyayyarsa,ga soyayyarta da ke nuqurqusar zuciyarsa a kullum,dole ya tausayawa Ra'uf danshi sunyi soyayya ma suna da shirin aure aka rabasu ya dai daure ya kauda tunaninsa yace
" Eh aboki na nasan da ciwo ravuwa da masoyi amma hakuri zakayi ka cigaba dayi kuma Allah yasa rabuwar tafi zama alkhairi sannan ka cigaba da addu'ar neman zabin Allah a rayuwarka"
Ra'uf ya jidadin nasihar abokin nasa Shureim abokine nagari,shiyasa yake alfahari da abokin nasa da murmushi ya kalli Shureim yace
"Nagode aboki na"
"Haba babu komai aboki na damuwarka ta wace da zan iya fidda ma damuwarka da nayi wallahi amma zan cigaba da tayaka addu'a,tun sanda na fahimci baka da walwala a kwanakin nan kuma naji baka kara yimin maganar budurwarka ta kasarku ba,shine yasa nayi tunanin ko akwai abinda ya faru da soyayyarku shine yasa nakasa hakura har saida na tanbayi Ahmad ko yasan meke damunka ya fadamin shine yasanar dani komai,nasan zafin so Ra'uf nima kullum ina cikinsa zullumi na kar na fadawa Inteesar ta kasa amincewa dani" Shureim ya karasa maganar da rarraunar murya
Dafa sa Ra'uf yayi yace
"Haba abokina karka damu zata amince dakai yau zanje gidansu Inteesar na sanar mata da soyayyar da kake yi mata nasan zata amince"
Shureim ya murmusa yace
"Kai abokina ina godiya sosai"
"Haba aboki na karka damu komai nayi ma kacancanta da ayi ma ne"
Cewar Ra'uf
Da haka suka sauya fira ta aiyukansu har zuwa wani lokaci