Sashe 40
Jininmu Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
" Yanzu Yaya inaji ina gani 'dana ya auri wannan yarinyar ba yadda na isa nayi,kina gani ko waya raban da AbdulWahid ya kira ni yau ake kwanan sati don karna masa maganar Auren nan,ga uwa uba ubansa ya koreni daga gidansa"
Cewar Hajiya Jamila da take zaune a babban falon gidan shema'u take wannan maganar
Murmushi Aunty Shema'un tayi kana ta dubi Hajiya Jamila ta soma magana
"Ki kwantar da hankalinki Jamila ai idan sunsan wata basu san wata ba,dama nagama yanke shawarar ku tafi Abujar yau keda Rukayya ku zauna acan tunda shi Bukar baida mutunci idan yaji kina can zaice ki koma dakinki dan ba saurara mata zaki ba idan kuka je,tunda gashi Bukar din ya zuga gaba 'daya 'ya'yanki bama Wahid ba tunda kika zo nan waye cikinsu ya kira ki sai munafukan kishiyoyinki da ba kaunar zamanki suke a gidan ba bayan duk arzikin Bukar din dake akasha wahala gurin samu su da suka zo zuwan daga baya"
Murmushin jin dadin wannan shawarar da 'yar uwarta ta Hajiya Jamila ta mike tana cewa
"Ai Yaya yau ba sai gobe ba zamu tafi" da haka ta shige ciki tana murmushi
****
ABDULRA'UF
" Ra'uf anya kana da cikakken hankali kuwa"Ra'uf yayi saurin dago kansa daga kwanciyar da yayi saman kujerun falonsu jin maganar da Ammi tayi masa ya soma magana da cewa
"Ammi maina aikata kuma?"
"Kafi kowa sanin koma maikayi ace daga wannan lamarin yanzu ka daina hatta da zuwa aiki baka yi kadaina walwala bayan Ahmad ya sanarma ita hartayi aurenta ta manta dakai amma kai tana makale a ranka ,tunda muka dawo baka leqa gurin aiki ba"
Mikewa yayi daga kwanciyar da yayi ya maida kallonsa ga Ammin nasu yace
"Ammi sam yadda kike tunani ba haka bane,wannan maganar ba ita bace ta hanani zuwa aiki ba,kinsan hali na daban manta da itaba bazan hakura ta auri wani ba,kawai dai nasan inajinta a cikin jinin jikina har yanzu"
Ammi ta dan tabe baki kana tace
"Ai saikai tayi, Shureim ya kirani a waya na lallabeka ka koma gurin aiki dai"
Murmushi yayi yace
"Ammi kenan,eh gobe dama zan koma,dama hutun dana daukane bai kareba"
Murmushi tayi jin abinda Ra'uf ya anbata ta maida duk natsuwarta garesa tare da soma magana
" mai zai hana kaje kanemi Auren Inteesar Khan Dawud abokiyar karatun Sophie ina lura da yadda take nuna ma soyayya tun tuni,kaje gurinta a tsaida magana nasan su ba zasu yi mana haka ba"
Ido ya zaro Ra'uf tare da jin wata faduwar gaba lokaci guda taziyarcesa ,inteesar din zai nemi aurenta yarinyar da abokinsa Shureim yake fadamasa irin son da yake mata yadai kasa furta mata ne
"Ya kayi shiru Ra'uf ko ba kai maraba da shawarata ba"Ammi tayi maganar tana kokarin katse shirun Ra'uf kallon Ammi yayi yace
" Ammi shureim ne ke san Inteesar yanzu koda zanje gurinta saidai naje saboda na shigar da soyayyarta gareta"
Tsaki Ammin tayi jin gaba daya dan nata har yau hankalinsa baya ga duk zancen da zata yi masa ya karkata ne kawai ga Rufaida,banda haka ina zaice Shureim yana san Inteesar mikewa tayi ta bashi guri rai a bace
Da kallo Ra'uf ya bita dukda baya san bacin ran mahaifiyarsa amma dai gaskiya bazai amince da shawarar taba na ya auri Inteesar yarinyar da abokinsa ke so dukda ita bata sani ba amma shi ai ya sani idan yayi masa hakan bai kyauta ba ko 'daya, ga uwa uba shifa a tsarinsa bazai iya auren macen da ba 'yar kasarsa ba.
"Ya ko aminci da maganar da kikaje masa da ita"Dady ya tari Ammi da wannan maganar da take kokarin karasa zama gefen gado Da dady yake zaune akai shima
" ai dama na fadama bazai amince ba,kaima kasan halin yaron nan da gaddama,tunda ya nuna waccen yarinyar yakeso kuma bai same ta ba zai wuya a yanzu ya amince da wata macen"Ammi ta karasa maganar da alamun bacin rai a fuskarta
Dady ya girgiza kai tare da cewa
"Wallahi Asma'u ina san farin cikin yaron nan,sai dai a karo na farko nima ba zan amince ya auri yarinyar nan ba,ko ni kaina bama ga Yaya Sule da Yaya Abdu kadai ba suka hana auren ba harda ni kaina mutanan da sukai kokarin lalata mana suna sukai silar rabamu da farin cikinmu rabuwar da sai dai mu kira ta da ta har abada" daga nan Dady Jabir ya fashe da kuka kai kace karamin yaro ne"
Ammi ganin mijinta na kuka yasa hankalinta ya tashi da cewa
"Haba Abban Safiyya me yayi zafi haka kai ba karamin Yaro ba bakomai ba,addua zaku cigaba dayi tuno da abinda ya wuce ba shine mafita ba"
Da wannan kalaman ta cigaba da lallashinsa har ya hakura
*****
Yaya yayaa Safiyya take kwalawa Ra'uf kira da baccin ya fara daukarsa
Ra'uf da yaji maganar Safiyya kamar a mafarki ya vu'de idanunsa ya mike zaune ya dora idanunsa akanta ya dan harareta da cewa
"Sophie Khan ya akai ne,kike kokarin fasamin dodon kunne"
Zama tayi kusa dashi tare da cewa
"Yaya yanzu Intee ta kira ni sunje Us ita da yayanta ankafe suna taga sunanmu nida Husna"
Murmushin Ra'uf yayi tare da cewa
"Kai amma ina miki murna sister,kin fadawa Husnan?"
Safiyya tayi saurin cewa"A'a Yaya,zuwa nayi ka kira ta a wayarka a fada mata"
Ra'uf yace
"Ke ina kudin wayar taki?"
Safiyya tayi saurin cewa
"Yaya ai ba kudi a wayata kamanta ne"
Hararar wasa yayiwa Safiyya da cewa
"Dady jiya ya sa miki kudi ina kika kaisu"
Marairaicewa Safiyya tayi
"Na kira kawaye na tun jiyan"
Tsaki Ra'uf yayi ya mikamata wayar dan sarai ya gano kudin nata ne batasan kashewa na cikin wayar.
Lambar Husna ta kamo ta kira ta shaida mata samun makarantar da sukayi ba karamin murna Husna tayi ba ita ma,daga nan suka cigaba da firarsu saida Ra'uf ya gaji da surutun da Safiyya ke masa a kunne ya anshe wayarsa ya kashe
Sadiya Khalil🖤*JININM U 'DAYA*
By Sadiya Khalil❤️
42.
Ina yiwa masoya wannan littafin fatan alkhairi a kowanne lokaci ina kuma anfani da wannan damar gurin yiwa 'yar uwata Aisha Umar Ibrahim fatan alkhairi na gama littafinta mai suna ZAN JIRATA lafiya Allah ya hadamu da alkhairan cikin littafin ya kawar damu da akasinsa ya shiryar damu bisa tafarkin tsira ya bamu ikon rubuta abinda zai anfanardamu ko bayan bama raye.Amin
42.
ABDULWAHID
Cikin kwarewa yake aikinsa da kwanciyar hankali auren Rufaida,bakaramin farin ciki yake da shi ba,tana nuna kulawarta gare sa,aikin da yake ya ajiye gefe,ya dauki wayarsa da take ringing wanda tunaninsa Rufaida ce,ganin tunda ya tafi aiki busu yi waya ba yadda suka saba,sai tunaninsa ya basa ko itace da taga bai kira ta ba ko ta kirasa,duba screen din wayarsa da yayi ya kaudar masa da tunanin sa ganin sunan da yasa wa Ummansu akan screen din itace mai kiran nasa wata irin faduwar gaba yaji ta ziyarce shi tunda yaga kiran Ummansa yasan sai ta yi masa fada sosai don yasa koda bakin aurensa a ranta sai ta masa don rab. an da ya kira ta yau kwana 7,a bakin Abbansu yaji duk abinda ya faru ganin tana kokarin katsewa yasa shi saurin dagawa
"Assalamu Alaikum,Umma ina yini,ya su Aunty"
Yayi maganar a jere a kuma tsoro ce
"Kazo ka shiga damu barrack din ku munzo yanzu nida Ruqayya"ba tare da ta vashi waccen amsar ba ta tare sa da wannan maganar da haka ta katse wayarta
AbdulWahid da baida wani zabi da ya wuce yaje tararsu da haka ya mike daga office dinsa ya fito ya fito yaje tarar mahaifiyar tasa ba tare da ya tuna da kiran Rufaida a waya ba ya Shiga motarsa ya fito daga headquarter dinsu
RUFAIDA
Cewar Hajiya Jamila da take zaune a babban falon gidan shema'u take wannan maganar
Murmushi Aunty Shema'un tayi kana ta dubi Hajiya Jamila ta soma magana
"Ki kwantar da hankalinki Jamila ai idan sunsan wata basu san wata ba,dama nagama yanke shawarar ku tafi Abujar yau keda Rukayya ku zauna acan tunda shi Bukar baida mutunci idan yaji kina can zaice ki koma dakinki dan ba saurara mata zaki ba idan kuka je,tunda gashi Bukar din ya zuga gaba 'daya 'ya'yanki bama Wahid ba tunda kika zo nan waye cikinsu ya kira ki sai munafukan kishiyoyinki da ba kaunar zamanki suke a gidan ba bayan duk arzikin Bukar din dake akasha wahala gurin samu su da suka zo zuwan daga baya"
Murmushin jin dadin wannan shawarar da 'yar uwarta ta Hajiya Jamila ta mike tana cewa
"Ai Yaya yau ba sai gobe ba zamu tafi" da haka ta shige ciki tana murmushi
****
ABDULRA'UF
" Ra'uf anya kana da cikakken hankali kuwa"Ra'uf yayi saurin dago kansa daga kwanciyar da yayi saman kujerun falonsu jin maganar da Ammi tayi masa ya soma magana da cewa
"Ammi maina aikata kuma?"
"Kafi kowa sanin koma maikayi ace daga wannan lamarin yanzu ka daina hatta da zuwa aiki baka yi kadaina walwala bayan Ahmad ya sanarma ita hartayi aurenta ta manta dakai amma kai tana makale a ranka ,tunda muka dawo baka leqa gurin aiki ba"
Mikewa yayi daga kwanciyar da yayi ya maida kallonsa ga Ammin nasu yace
"Ammi sam yadda kike tunani ba haka bane,wannan maganar ba ita bace ta hanani zuwa aiki ba,kinsan hali na daban manta da itaba bazan hakura ta auri wani ba,kawai dai nasan inajinta a cikin jinin jikina har yanzu"
Ammi ta dan tabe baki kana tace
"Ai saikai tayi, Shureim ya kirani a waya na lallabeka ka koma gurin aiki dai"
Murmushi yayi yace
"Ammi kenan,eh gobe dama zan koma,dama hutun dana daukane bai kareba"
Murmushi tayi jin abinda Ra'uf ya anbata ta maida duk natsuwarta garesa tare da soma magana
" mai zai hana kaje kanemi Auren Inteesar Khan Dawud abokiyar karatun Sophie ina lura da yadda take nuna ma soyayya tun tuni,kaje gurinta a tsaida magana nasan su ba zasu yi mana haka ba"
Ido ya zaro Ra'uf tare da jin wata faduwar gaba lokaci guda taziyarcesa ,inteesar din zai nemi aurenta yarinyar da abokinsa Shureim yake fadamasa irin son da yake mata yadai kasa furta mata ne
"Ya kayi shiru Ra'uf ko ba kai maraba da shawarata ba"Ammi tayi maganar tana kokarin katse shirun Ra'uf kallon Ammi yayi yace
" Ammi shureim ne ke san Inteesar yanzu koda zanje gurinta saidai naje saboda na shigar da soyayyarta gareta"
Tsaki Ammin tayi jin gaba daya dan nata har yau hankalinsa baya ga duk zancen da zata yi masa ya karkata ne kawai ga Rufaida,banda haka ina zaice Shureim yana san Inteesar mikewa tayi ta bashi guri rai a bace
Da kallo Ra'uf ya bita dukda baya san bacin ran mahaifiyarsa amma dai gaskiya bazai amince da shawarar taba na ya auri Inteesar yarinyar da abokinsa ke so dukda ita bata sani ba amma shi ai ya sani idan yayi masa hakan bai kyauta ba ko 'daya, ga uwa uba shifa a tsarinsa bazai iya auren macen da ba 'yar kasarsa ba.
"Ya ko aminci da maganar da kikaje masa da ita"Dady ya tari Ammi da wannan maganar da take kokarin karasa zama gefen gado Da dady yake zaune akai shima
" ai dama na fadama bazai amince ba,kaima kasan halin yaron nan da gaddama,tunda ya nuna waccen yarinyar yakeso kuma bai same ta ba zai wuya a yanzu ya amince da wata macen"Ammi ta karasa maganar da alamun bacin rai a fuskarta
Dady ya girgiza kai tare da cewa
"Wallahi Asma'u ina san farin cikin yaron nan,sai dai a karo na farko nima ba zan amince ya auri yarinyar nan ba,ko ni kaina bama ga Yaya Sule da Yaya Abdu kadai ba suka hana auren ba harda ni kaina mutanan da sukai kokarin lalata mana suna sukai silar rabamu da farin cikinmu rabuwar da sai dai mu kira ta da ta har abada" daga nan Dady Jabir ya fashe da kuka kai kace karamin yaro ne"
Ammi ganin mijinta na kuka yasa hankalinta ya tashi da cewa
"Haba Abban Safiyya me yayi zafi haka kai ba karamin Yaro ba bakomai ba,addua zaku cigaba dayi tuno da abinda ya wuce ba shine mafita ba"
Da wannan kalaman ta cigaba da lallashinsa har ya hakura
*****
Yaya yayaa Safiyya take kwalawa Ra'uf kira da baccin ya fara daukarsa
Ra'uf da yaji maganar Safiyya kamar a mafarki ya vu'de idanunsa ya mike zaune ya dora idanunsa akanta ya dan harareta da cewa
"Sophie Khan ya akai ne,kike kokarin fasamin dodon kunne"
Zama tayi kusa dashi tare da cewa
"Yaya yanzu Intee ta kira ni sunje Us ita da yayanta ankafe suna taga sunanmu nida Husna"
Murmushin Ra'uf yayi tare da cewa
"Kai amma ina miki murna sister,kin fadawa Husnan?"
Safiyya tayi saurin cewa"A'a Yaya,zuwa nayi ka kira ta a wayarka a fada mata"
Ra'uf yace
"Ke ina kudin wayar taki?"
Safiyya tayi saurin cewa
"Yaya ai ba kudi a wayata kamanta ne"
Hararar wasa yayiwa Safiyya da cewa
"Dady jiya ya sa miki kudi ina kika kaisu"
Marairaicewa Safiyya tayi
"Na kira kawaye na tun jiyan"
Tsaki Ra'uf yayi ya mikamata wayar dan sarai ya gano kudin nata ne batasan kashewa na cikin wayar.
Lambar Husna ta kamo ta kira ta shaida mata samun makarantar da sukayi ba karamin murna Husna tayi ba ita ma,daga nan suka cigaba da firarsu saida Ra'uf ya gaji da surutun da Safiyya ke masa a kunne ya anshe wayarsa ya kashe
Sadiya Khalil🖤*JININM U 'DAYA*
By Sadiya Khalil❤️
42.
Ina yiwa masoya wannan littafin fatan alkhairi a kowanne lokaci ina kuma anfani da wannan damar gurin yiwa 'yar uwata Aisha Umar Ibrahim fatan alkhairi na gama littafinta mai suna ZAN JIRATA lafiya Allah ya hadamu da alkhairan cikin littafin ya kawar damu da akasinsa ya shiryar damu bisa tafarkin tsira ya bamu ikon rubuta abinda zai anfanardamu ko bayan bama raye.Amin
42.
ABDULWAHID
Cikin kwarewa yake aikinsa da kwanciyar hankali auren Rufaida,bakaramin farin ciki yake da shi ba,tana nuna kulawarta gare sa,aikin da yake ya ajiye gefe,ya dauki wayarsa da take ringing wanda tunaninsa Rufaida ce,ganin tunda ya tafi aiki busu yi waya ba yadda suka saba,sai tunaninsa ya basa ko itace da taga bai kira ta ba ko ta kirasa,duba screen din wayarsa da yayi ya kaudar masa da tunanin sa ganin sunan da yasa wa Ummansu akan screen din itace mai kiran nasa wata irin faduwar gaba yaji ta ziyarce shi tunda yaga kiran Ummansa yasan sai ta yi masa fada sosai don yasa koda bakin aurensa a ranta sai ta masa don rab. an da ya kira ta yau kwana 7,a bakin Abbansu yaji duk abinda ya faru ganin tana kokarin katsewa yasa shi saurin dagawa
"Assalamu Alaikum,Umma ina yini,ya su Aunty"
Yayi maganar a jere a kuma tsoro ce
"Kazo ka shiga damu barrack din ku munzo yanzu nida Ruqayya"ba tare da ta vashi waccen amsar ba ta tare sa da wannan maganar da haka ta katse wayarta
AbdulWahid da baida wani zabi da ya wuce yaje tararsu da haka ya mike daga office dinsa ya fito ya fito yaje tarar mahaifiyar tasa ba tare da ya tuna da kiran Rufaida a waya ba ya Shiga motarsa ya fito daga headquarter dinsu
RUFAIDA