Sashe 29
Jininmu Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kusa da ummi suka zauna suka gaishe da Abban, da tambayar sa ya ya baro mutanan gida?.
Yace "Lafiya k'alau Abdul-Ahad ma yaso biyo ni to kuma sai ya koma gurin aiki jiya, ya banga Rufaida ba?". Ya karkare maganar da tambaya.
Rumaisa tace "tana sama".
Rufaida Da take zaune a carpet da littafi a gefenta da take yiwa Rafi'a assignment inda da ya kirata ta ajiye littafin ta dauki wayar da take kusa da ita sunan mai kiran Ra'uf ne Saida ta kusa katsewa ta daga suka gaisa
Shi kuwa yana falon 'dakinsa yana kallon TV da ya rage volume yake wayar
Ya nisa yace
" Allah Rufee na kosa naje su Dady su karaso yanzu suzo sunema min aurenki asa rana ayi komai"
Tace "haba dai yaya Ra'uf".
"Allah kuwa amma na san ba zaki fahimci 'kaunar da nake miki ba shi yasa".
Murmushi ta yi tace "ni kaina Yaya haka ne".
"Me kenan? Fa'di muji". Ya fa'di haka wanda dalili mai 'karfi kenan yake 'kara jin sonta a ransa saboda yarinya ce mai kunya Rufaida shi kuma mutum ne mai son mace mai kunya kuma wadda bata saurin furta abu koda tasan dai-dai ne sai tanemi izini.
Har da rufe fuskarta kafin tace
"ina kaunarka dan Allah har mamakin kaina na keyi".
"Rufee kenan kar kiyi mamaki da ikon Allah duk da dai nasan kurum fa'da ki kayi dan ki kwantar min da hankalin cewa kina 'kaunata da kika yi, amma na san nafi k'aunarki fiye da 'kaunar da kike min".
"Kar ka fadi haka yaya Ra'uf har cikin raina na fa'di haka".
"To Allah yasa"
Tace masa "Amin" Shiru ya ratsa tsakaninsu Karin Ra'uf yace
"Ammi ta ga photonki fa jiya ita da Momy Hannatu sun yaba dake sosai
Murmushi Rufaida tayi suka cigaba da hirarsu
*****
"Abba sannu da zuwa". Rufaida da ta shigo falon ta zauna 'kasan carpet tana gaishe sa wanda yake shi ka'dai zaune a falon ya na ta'ba abincin da aka kawo masa.
Gaisawa suka yi ganin shigowar Abba Aliyu yasa Rufaida mi'kewa ta bar falon.
Bayan sun gaisa ne
Abba bukar ya dubi Abba Aliyu yace "wato Ali kai ka zama babban kanka shikenan har za'a zo neman auren Rufaida ba zaka fa'da min ba ki?".
"Yaya da naga kace min zaka zo yau kuma ya yi dai-dai da zuwan su shi yasa ban fa'da maka ba, kuma dama niyyar da nayi suje can a nemi auren a can, sai kuma ranar zuwan nasu ya yi dai-dai da naka zuwan".
Wanda zullumin abinda Abba Bukar zaiyi tunanin ganin dansama yanasan Rufaidan idan yafadamasa maganar zuwan baisan ya zai dauki zancenba yasashi kin fadamasa zuwan ganin yayi dai dai da zuwansa.
"To ba laifi yaushe ne zasu zo 'din? Dan yau nake shirin komawa gida".
"Yanzu Alhaji Hashim ya kirani yacemin Ahmad ya kirasa yace sun taho shima Alhaji Hashim din yaso zuwa aiki gaggawane ya samesa a asibiti" Abba Aliyu ya karasa maganar yana kallon fuskar Abba Bukar
*********
Ra'uf ne ya sake kiranta ta mi'ka hannu ta 'dauki wayar da ke gefen gado
Rufee su Dady sun taho suna hanya yanzu haka na fa'da musu ace 2week za'a saka ranar bikin so nake kawai mu koma india tare bayan bikin,basai na sake dawowa"
Itadai murmushi tayi batace komaiba suka cigaba da wayarsu cikin nishadi da kaunar juna
______________________
Motoci ne guda biyu suka kunno kai cikin gidan nasu Rufaida
Dady Usman da sauran mutane uku Abdul ne ya yi musu iso cikin falon bakin a kujerun falon suka zazzauna Abdul ya gaishe su sannan ya bar falon da idon Abba Abdu yanakan Abdul har yabar falon yaron yana da nutsuwa ya fada aransa haka kums yake tama Abdul din kallon sani
********
Rufaida da ta koma ta kwanta bayan ta hango motocin da suka shigo ta taga haka nan ta ji jikinta ya yi sanyi ga kuma bugun zuciyarta da ya karu, Addu'a ta soma yi kafin ta rage jin haka.
*********
Ruwan da Dady Usman ya bu'de ya zuba a kofi ya ajiye a centre table Abba Salmanu ya dube shi yace Usman nifa zan tashi dubi fa zaman da mu kayi jiran shigowar mutanan nan tsabar rashin sanin darajar 'dan adam sun'ki koda kallonmu ni shi yasa ba ko wanne neman auren ake zuwa dani ba
Dady Usman ya duba agogon hannunsa yace" YAYA mudai kara musu hakuri har yau bamuyi minti ko talatin ba fa"
Abba Suleh ne ya mi'ke yana 'ko'karin tashi su Abba suka shigo falon da sallamarsu wanda yasa Abba sulehn komawa ya zauna
Cikin firgici a fuskarsu suke kallon juna
Abba Bukar da yake kallon fuskar mutanan falon ya mi'ke rai 'bace ya soma magana tare da nu na musu 'kofar fita
"Ba zan laminci wula'kanci a gidan 'dan uwa na ba sannan da nasan June masu Neman auren da buku wahalar da kanku zuwa ba domin dai koda 'dan ku shine ka'dai yayi saura a duniya Rufaida ba zata aure shi ba, indan har nine ma'daurin auren,haka ma indai Aliyu shine uba gareta.
Tun kafin ya kai aya a maganar suka mi'ke Abba Suleh ya fara maida martani cikin zafin rai"Ni kaina bana fata ahalina su ha'da jini da ku, koda bayan ranmu kuwa aure nina haramtasa a gare su, da a ce na san da ku 'dan 'kanina ke son ha'da auran nan da hatta wancen auren na baya kuna da ala'ka ta jini da su da bazan bari ahali na ya ha'da ji'ni da masu butulci masu muguwar sakayya irin ahalinku ba da halayyar ahalinku takesha shafar duk wanda ya hada iri daku,mayaudara
Maganganu masu zafi suke jifan junansu da shi
Da haka su Abba Suleh suka fice daga falon da gidanma baki daya vadan maganganun da suke jifan junansu dasu masu zafi sun kare ba sai dan busuga anfanin cigaba da zama a gidanba
__________________________
"Hauwa'u ban ta'ba tunanin da kanki zaki aikata haka ba, kuma daga ke har 'yar taki ku sani kamar yadda kuka turo da mijin da kuke so ta aura ba zata aure shi ba idan har da rayuwata a doron 'kasa Ahad zan aura mata kota naso ko bataso 'dan cikina kuma dan uwanta, domin ni ban manta ba idan ke kin manta" Abba Bukar yake maganar cikin bacin rai karara a fuskarsa da shigowarsa falon kenan da ko sallama ya gagarayi ya tari Ummi Hauwa'u da wa'dannan maganganun.
Rufaida da ta tsinci maganar tana 'ko'karin saukowa amsa kiran Ummi 'kafafuwanta ne suka yi mata nauyi kafin bugun zuciyarta ya tsawaita.
"ki karaso nan ke da uwarki muji wa ya kira wa'dannan mutanan zuwa ahalinmu,wadanda busu dauki dan adam a bakin komai bare suga darajarsa".
Tsintar muryar Abba Bukar da ta yi yasa ta 'karasowa falon ta tsugunna gabansa tana mai da kallonta 'kasa wanda take jin tsananin ciwan kai lokaci guda ya saukar mata.
"Kin bani mamaki da har kika biyewa wannan mara sanin mutuncin kanta bare musa ran ko zata san tamu ya nuna Ummi " Kuma ki sani indan kinyi hakan saboda tunaninki mun manta da wancen al'amarin to kin makara ki domin zuriyar Tafida bata canza daga ra'ayintaba har ya'u duk wanda yaketa mutuncin zuriyarmu babu sauran mutunci da zai sake samu a zuriyarmu kuma kiyi gaggawar canza shiri domin koda yaron nan shine ka'dai namiji to baza ta aure shi ba, sai ku sake ha'da wani 'kullin kuma,sannan ki kuka da kanki"
ya karasa maganar yana nuna Ummi Hauwa'u da ya tsa.
Abdul da ya tarar da zancen bai tsaya saurare ba ya bar gurin, dan shi ba ko wacce magana yake son ji ba,bare shida tun fil-azal Ra'uf bai kwanta masa a raiba
"Yaya bukar bani da masaniya a kan Ra'uf ban ta'ba ganin shi ba" cewar Ummi Hauwa'u
"Dakata banason sake jin maganar ki amma ki sani ahalinmu ba zasu hada aure da wannan kaskantaccen ahalinba idan da kaddara ta hadamu dasu to yanzu bazan laminta ba matukar ina raye zuriyar Tafida ba zata hada iri da ahalin 'Danbatta ba masu son zuciya da tauye gaskiya ta ko ina akwai banbanci a tsakaninmu"
Ummi Hauwa'u da take jin kalaman har cikin kwanyar kanta falon ta bari tana zubda hawaye batasan maiyasa ake ta allaka haduwar Rufaida da Ra'uf tanada masaniya ba.
Rufaida ma bayanta tabi.
Abba Bukar ya cigaba da fadansa
_______________________
Ra'uf da ke falo zaune shi da Momy Hannatu da ya zuba tagumi da hannu biyu , Momy ce ta kalle sa ta ce "lafiya kuwa, Ra'uf?".
"Momy zuciyata ce naji duk bata min 'dadi, gashi bugun zuciyar yana 'karuwa".
"Ka ri'ka addu'a insha Allah zai ragu, kuma zaka ji komai yazo da sau'ki".
"To momy, yauwa Ammi ta ce cikin satin nan zata koma".
"Eh ta fa'damin jiya a waya".
Abba Sule da bai jira ya 'karasa rufe murfin motarsa ba ya fito ransa a matu'kar bace, Dady Usman da Abba Salmanu da Abba Abdu suna kiran sa amma ko saurarensu bai yi ba ya 'kara sa 'kofar falon ya bu'de ta da karfinsa.
SADIYA KHALIL😊🖊️*JININMU DAYA*
NA SADIYA IBRAHIM KHALIL
SHAFINA 31
Momy Hannatu ta maida dubanta ga Abba Sule wadda take 'ko'karin canza tasha da remote a hannunta, shi kuma Ra'uf yana kwance kan doguwar kujera.
Magana ya fara cikin 'daga murya
"Wato kai Ra'uf har akwai ranar da kai da kanka zaka nemi wula'kanta mu to wallahi in dai har ka kafe da auran yarinyar nan sai dai mu raba hanya da kai kuma hatta mahaifi a gare ka sai dai ku raba hanya da shi, ko da zaka mutu babu aure haka ko da ita ta yi saura a mata a duniya ba zaka aure ta ba".
Su Dady da suke bayansa tsaye suka furta da mun san irin wula'kancin da zamu riska kenan da ba mu yi 'ko'karin zuwa ba, Momy da take 'kokarin furta wani abu, Abba bukar ya dakatar da ita ta hanyar cewa "dakata Hindatu ba na son maganar ki".
Ra'uf ba tare da ya furtawa kowa komai ba ya bar falon inda kansa ya yi masa nauyi, da wayarsa ya ci karo a 'dakinsa a centre table 'din falonsa wayar ya 'dauka ya shiga kiran Rufaida
Yace "Lafiya k'alau Abdul-Ahad ma yaso biyo ni to kuma sai ya koma gurin aiki jiya, ya banga Rufaida ba?". Ya karkare maganar da tambaya.
Rumaisa tace "tana sama".
Rufaida Da take zaune a carpet da littafi a gefenta da take yiwa Rafi'a assignment inda da ya kirata ta ajiye littafin ta dauki wayar da take kusa da ita sunan mai kiran Ra'uf ne Saida ta kusa katsewa ta daga suka gaisa
Shi kuwa yana falon 'dakinsa yana kallon TV da ya rage volume yake wayar
Ya nisa yace
" Allah Rufee na kosa naje su Dady su karaso yanzu suzo sunema min aurenki asa rana ayi komai"
Tace "haba dai yaya Ra'uf".
"Allah kuwa amma na san ba zaki fahimci 'kaunar da nake miki ba shi yasa".
Murmushi ta yi tace "ni kaina Yaya haka ne".
"Me kenan? Fa'di muji". Ya fa'di haka wanda dalili mai 'karfi kenan yake 'kara jin sonta a ransa saboda yarinya ce mai kunya Rufaida shi kuma mutum ne mai son mace mai kunya kuma wadda bata saurin furta abu koda tasan dai-dai ne sai tanemi izini.
Har da rufe fuskarta kafin tace
"ina kaunarka dan Allah har mamakin kaina na keyi".
"Rufee kenan kar kiyi mamaki da ikon Allah duk da dai nasan kurum fa'da ki kayi dan ki kwantar min da hankalin cewa kina 'kaunata da kika yi, amma na san nafi k'aunarki fiye da 'kaunar da kike min".
"Kar ka fadi haka yaya Ra'uf har cikin raina na fa'di haka".
"To Allah yasa"
Tace masa "Amin" Shiru ya ratsa tsakaninsu Karin Ra'uf yace
"Ammi ta ga photonki fa jiya ita da Momy Hannatu sun yaba dake sosai
Murmushi Rufaida tayi suka cigaba da hirarsu
*****
"Abba sannu da zuwa". Rufaida da ta shigo falon ta zauna 'kasan carpet tana gaishe sa wanda yake shi ka'dai zaune a falon ya na ta'ba abincin da aka kawo masa.
Gaisawa suka yi ganin shigowar Abba Aliyu yasa Rufaida mi'kewa ta bar falon.
Bayan sun gaisa ne
Abba bukar ya dubi Abba Aliyu yace "wato Ali kai ka zama babban kanka shikenan har za'a zo neman auren Rufaida ba zaka fa'da min ba ki?".
"Yaya da naga kace min zaka zo yau kuma ya yi dai-dai da zuwan su shi yasa ban fa'da maka ba, kuma dama niyyar da nayi suje can a nemi auren a can, sai kuma ranar zuwan nasu ya yi dai-dai da naka zuwan".
Wanda zullumin abinda Abba Bukar zaiyi tunanin ganin dansama yanasan Rufaidan idan yafadamasa maganar zuwan baisan ya zai dauki zancenba yasashi kin fadamasa zuwan ganin yayi dai dai da zuwansa.
"To ba laifi yaushe ne zasu zo 'din? Dan yau nake shirin komawa gida".
"Yanzu Alhaji Hashim ya kirani yacemin Ahmad ya kirasa yace sun taho shima Alhaji Hashim din yaso zuwa aiki gaggawane ya samesa a asibiti" Abba Aliyu ya karasa maganar yana kallon fuskar Abba Bukar
*********
Ra'uf ne ya sake kiranta ta mi'ka hannu ta 'dauki wayar da ke gefen gado
Rufee su Dady sun taho suna hanya yanzu haka na fa'da musu ace 2week za'a saka ranar bikin so nake kawai mu koma india tare bayan bikin,basai na sake dawowa"
Itadai murmushi tayi batace komaiba suka cigaba da wayarsu cikin nishadi da kaunar juna
______________________
Motoci ne guda biyu suka kunno kai cikin gidan nasu Rufaida
Dady Usman da sauran mutane uku Abdul ne ya yi musu iso cikin falon bakin a kujerun falon suka zazzauna Abdul ya gaishe su sannan ya bar falon da idon Abba Abdu yanakan Abdul har yabar falon yaron yana da nutsuwa ya fada aransa haka kums yake tama Abdul din kallon sani
********
Rufaida da ta koma ta kwanta bayan ta hango motocin da suka shigo ta taga haka nan ta ji jikinta ya yi sanyi ga kuma bugun zuciyarta da ya karu, Addu'a ta soma yi kafin ta rage jin haka.
*********
Ruwan da Dady Usman ya bu'de ya zuba a kofi ya ajiye a centre table Abba Salmanu ya dube shi yace Usman nifa zan tashi dubi fa zaman da mu kayi jiran shigowar mutanan nan tsabar rashin sanin darajar 'dan adam sun'ki koda kallonmu ni shi yasa ba ko wanne neman auren ake zuwa dani ba
Dady Usman ya duba agogon hannunsa yace" YAYA mudai kara musu hakuri har yau bamuyi minti ko talatin ba fa"
Abba Suleh ne ya mi'ke yana 'ko'karin tashi su Abba suka shigo falon da sallamarsu wanda yasa Abba sulehn komawa ya zauna
Cikin firgici a fuskarsu suke kallon juna
Abba Bukar da yake kallon fuskar mutanan falon ya mi'ke rai 'bace ya soma magana tare da nu na musu 'kofar fita
"Ba zan laminci wula'kanci a gidan 'dan uwa na ba sannan da nasan June masu Neman auren da buku wahalar da kanku zuwa ba domin dai koda 'dan ku shine ka'dai yayi saura a duniya Rufaida ba zata aure shi ba, indan har nine ma'daurin auren,haka ma indai Aliyu shine uba gareta.
Tun kafin ya kai aya a maganar suka mi'ke Abba Suleh ya fara maida martani cikin zafin rai"Ni kaina bana fata ahalina su ha'da jini da ku, koda bayan ranmu kuwa aure nina haramtasa a gare su, da a ce na san da ku 'dan 'kanina ke son ha'da auran nan da hatta wancen auren na baya kuna da ala'ka ta jini da su da bazan bari ahali na ya ha'da ji'ni da masu butulci masu muguwar sakayya irin ahalinku ba da halayyar ahalinku takesha shafar duk wanda ya hada iri daku,mayaudara
Maganganu masu zafi suke jifan junansu da shi
Da haka su Abba Suleh suka fice daga falon da gidanma baki daya vadan maganganun da suke jifan junansu dasu masu zafi sun kare ba sai dan busuga anfanin cigaba da zama a gidanba
__________________________
"Hauwa'u ban ta'ba tunanin da kanki zaki aikata haka ba, kuma daga ke har 'yar taki ku sani kamar yadda kuka turo da mijin da kuke so ta aura ba zata aure shi ba idan har da rayuwata a doron 'kasa Ahad zan aura mata kota naso ko bataso 'dan cikina kuma dan uwanta, domin ni ban manta ba idan ke kin manta" Abba Bukar yake maganar cikin bacin rai karara a fuskarsa da shigowarsa falon kenan da ko sallama ya gagarayi ya tari Ummi Hauwa'u da wa'dannan maganganun.
Rufaida da ta tsinci maganar tana 'ko'karin saukowa amsa kiran Ummi 'kafafuwanta ne suka yi mata nauyi kafin bugun zuciyarta ya tsawaita.
"ki karaso nan ke da uwarki muji wa ya kira wa'dannan mutanan zuwa ahalinmu,wadanda busu dauki dan adam a bakin komai bare suga darajarsa".
Tsintar muryar Abba Bukar da ta yi yasa ta 'karasowa falon ta tsugunna gabansa tana mai da kallonta 'kasa wanda take jin tsananin ciwan kai lokaci guda ya saukar mata.
"Kin bani mamaki da har kika biyewa wannan mara sanin mutuncin kanta bare musa ran ko zata san tamu ya nuna Ummi " Kuma ki sani indan kinyi hakan saboda tunaninki mun manta da wancen al'amarin to kin makara ki domin zuriyar Tafida bata canza daga ra'ayintaba har ya'u duk wanda yaketa mutuncin zuriyarmu babu sauran mutunci da zai sake samu a zuriyarmu kuma kiyi gaggawar canza shiri domin koda yaron nan shine ka'dai namiji to baza ta aure shi ba, sai ku sake ha'da wani 'kullin kuma,sannan ki kuka da kanki"
ya karasa maganar yana nuna Ummi Hauwa'u da ya tsa.
Abdul da ya tarar da zancen bai tsaya saurare ba ya bar gurin, dan shi ba ko wacce magana yake son ji ba,bare shida tun fil-azal Ra'uf bai kwanta masa a raiba
"Yaya bukar bani da masaniya a kan Ra'uf ban ta'ba ganin shi ba" cewar Ummi Hauwa'u
"Dakata banason sake jin maganar ki amma ki sani ahalinmu ba zasu hada aure da wannan kaskantaccen ahalinba idan da kaddara ta hadamu dasu to yanzu bazan laminta ba matukar ina raye zuriyar Tafida ba zata hada iri da ahalin 'Danbatta ba masu son zuciya da tauye gaskiya ta ko ina akwai banbanci a tsakaninmu"
Ummi Hauwa'u da take jin kalaman har cikin kwanyar kanta falon ta bari tana zubda hawaye batasan maiyasa ake ta allaka haduwar Rufaida da Ra'uf tanada masaniya ba.
Rufaida ma bayanta tabi.
Abba Bukar ya cigaba da fadansa
_______________________
Ra'uf da ke falo zaune shi da Momy Hannatu da ya zuba tagumi da hannu biyu , Momy ce ta kalle sa ta ce "lafiya kuwa, Ra'uf?".
"Momy zuciyata ce naji duk bata min 'dadi, gashi bugun zuciyar yana 'karuwa".
"Ka ri'ka addu'a insha Allah zai ragu, kuma zaka ji komai yazo da sau'ki".
"To momy, yauwa Ammi ta ce cikin satin nan zata koma".
"Eh ta fa'damin jiya a waya".
Abba Sule da bai jira ya 'karasa rufe murfin motarsa ba ya fito ransa a matu'kar bace, Dady Usman da Abba Salmanu da Abba Abdu suna kiran sa amma ko saurarensu bai yi ba ya 'kara sa 'kofar falon ya bu'de ta da karfinsa.
SADIYA KHALIL😊🖊️*JININMU DAYA*
NA SADIYA IBRAHIM KHALIL
SHAFINA 31
Momy Hannatu ta maida dubanta ga Abba Sule wadda take 'ko'karin canza tasha da remote a hannunta, shi kuma Ra'uf yana kwance kan doguwar kujera.
Magana ya fara cikin 'daga murya
"Wato kai Ra'uf har akwai ranar da kai da kanka zaka nemi wula'kanta mu to wallahi in dai har ka kafe da auran yarinyar nan sai dai mu raba hanya da kai kuma hatta mahaifi a gare ka sai dai ku raba hanya da shi, ko da zaka mutu babu aure haka ko da ita ta yi saura a mata a duniya ba zaka aure ta ba".
Su Dady da suke bayansa tsaye suka furta da mun san irin wula'kancin da zamu riska kenan da ba mu yi 'ko'karin zuwa ba, Momy da take 'kokarin furta wani abu, Abba bukar ya dakatar da ita ta hanyar cewa "dakata Hindatu ba na son maganar ki".
Ra'uf ba tare da ya furtawa kowa komai ba ya bar falon inda kansa ya yi masa nauyi, da wayarsa ya ci karo a 'dakinsa a centre table 'din falonsa wayar ya 'dauka ya shiga kiran Rufaida