← Book details Huriyya Part 1 And 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 90 OF 163

Sashe 90

Huriyya Part 1 And 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Daga haka be kara cewa komai ba ya fice daga office din, gafen hijabinta ta saka ta share hawayenta, sannan ta nufi gilashinta ta dauka ta cire wanda ya saka mata ta maida nata sannan ta nufi kofar ta bude. Taku daya biyu kamin ta yi na uku wanda ya kawo ta ya nuna mata hanyar da za su ba, ba wanda suka zo dazun ba. Ba musu ta bi bayansa har suka isa gurin motar ya bude mata ta shiga ta zauna, shi kuma ya shiga mazaunin tuki yayi ma motar key, amman shiru shiru ta ji yaja motar sun kama hanya ba, bata ankaro ba aka bude back seat inda take zaune, Captain ne ya shigo cikin motar ya zauna, tana kallonsa ta yi saurin maida idonta kasa, sai ya kai hannu ya dago fuskarta ya cire gilashin idonta ya saka masa nasan data cire ta aje masa a office, sannan ya bude motar ya fita da nata ya rufe motar.
Damdamdam.. Ya buga bayan motar sai sojan yaja motar suka fara tafiya.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
29
Sai da suka wuce sannan ya dawo office dinsa, yana shiga ya aje gilashin na Hurriya a saman teburinsa ya zagaya ya zauna ya cigaba da aikin da yake. Few minutes Namra ta kira wayarsa dake gaban teburin sai ya amsa ta bluetooth din dake kunnensa yana duba wasu takardun.

“Ni fa na zagaye garin nan kaf duk inda nake saka ran samu wannan turaren Kapter Bokur Perfume ance min babu shi, wasu sunce sai Abuja da Kaduna ake samunsa ko Kano, wasu ma cewa suke ba su sanshi ba”

Ya dago daga aikin da yake yana murmushi ya jingina da kujerar da yake zaune yana lilo, shi kanshi daman ya san ba za a samu turare ba domin abun da babu ne be ya fada mata, shi ya hada sunan turare and ya san babu turaren dake da exiting mai irin sunan.

“Okay, na baki zabi ki zabo min turare mai kamshi”

“Aa ka fada dai, kar sai na dauko maka turare ka zo kana min fada ko ka ce mai warin albasa ne, kasan wata rana ba a maka daidai, garin gwaninta sai a bata maka rai”

“Ssi ka ce ni nafi kowa muguwar zuciyar? Please select ina jiranki”

“Toh”

Ta kashe wayar, sai ya juyo kansa a hankali ya kalli gurin da Hurriya ta zauna, rabin abincin da ta zuba a duk a kasa yake garin sauri ta zuba kuma ta ci.

“Mtscheeeeee”

Yaja tsaki ya tsani guri da datti ko kadan ne balle kuma na abinci, telephone dinsa yayi using ya kira aka shigo aka gyara gurin aka maida komai gafe daya, bayan kamar awa daya Namra ta kira sai ya fada mata inda zata zo ta same shi, a lokacin da ta iso gurin ita kanta sai ta tsoro ya kama ta even though ta taba zuwa amman yadda aka gyara gurin aka canja komai da tsaurara tsaro ya fi na da, arzikinta daya ya aiko aka shiga da ita har ciki. Tana shigowa Office din ya dauke hannayensa daga aikin da yake yana murmushi.

“Allah yasa kin zabo mai kamshi”

“I try my best na ga na samu mai kamshi kuma mai dadi, shiyasa na siyo kala biyar ba daya ba”

Ta matso kusa da teburin ta dora bag din da turaren yake ciki ta fara cirowa tana nuna masa. Ba laifi duka suna da dadi kuma duka na maza ne, amman babu kalar nasa a ciki, haka yayi mata godiya ya karba ya aje, a lokacin da take kokarin dauke idonta daga teburin idanuwan nata suka yi arba da gilashin Hurriya dake kan teburin a take ta kai hannu ta dauka tana dubawa.

“Kamar gilashin Hurriya”

“Nata ne”

Ya amsa mata kai tsaye ba tare da tunanin komai ba.

Ta juya ta karewa ko'ina na office din kallo sai ta dora hasashenta akan abinci ta kawo masa saboda kulolin Momy da ta gani.

“Abinci ta kawo”

Ashe kuwa ta yi hasashenta daidaita, sai dai wani abun ne ya tsaya mata a rai da ta kasa hadewa har sai da ta tambaya.

“Me ya kawo gilashinta a nan?”

“Sato shi na yi kin san ni barawo ni”

Ta dan yi murmushi.

“Ni ban ce ba, na san bata gani sai da gilashin ne shiyasa”

“Na bata wani, ki zauna mana”

Ta zauna tana jin numashinta kamar zai shake zuciyarta na bugawa da mugun karfi.

“Kuma ta karba?”

“Da na yi mata ta karfi ba, kin san kanwar nan taki akwai musu da kafiya, amman kuma tana samun sa'a na duk fushin nan nawa na kanyi kokarin controlling kaina na daga mata kafa saboda kawai lalaurar da take tare da ita”

Yana aikin yana amsa nata da babu alamar wasa ko second thought a tare da shi.

“Ka taba bata wani abu kamin yau ta bata karba ba?”

Yayi shiru na wasu mintuna sannan ya amsa mata.

“Na taba bata kyautar gilashi a gabanki bata karba kin tuna? Kanenta ya hanata karba saboda ya fi ni iya fitina”

Ta yi murmushin karfin hali.
“Hamad din ne ya fika fitina? Anya akwai wanda ya fika fitina Captain”

“Yep ai shi yaro ne yake da wannan fitinar, yayarsa ce fa amman tsoronsa take”

“Kai ma ai kowa tsoronka yake saboda fitinarka Captain, gaskiya bana jin akwai wanda ya fi ka saurin fusata, fadar bakar magana, da kuma fitina”

Ya tsaya ya dubeta.
“Ashe haka kuke kallona, zan baku mamaki wata rana”

“Babu wannan ranar ai”

“Deal”

“Deal”

Ta amsa tana dariya, sai ya lumashe ido ya bude ya girgiza kai.

“Ki wuce da kulolin Momy, kuma ki fada mata na gode sosai”

Tana jin haka ta san ya sallame ta kenan, that's means yana bukatar ta tashi ta tafi.

“Okay”

Ta mike tsaye ta nufi gurin da kulolin suke ta dauki wadanda zata iya ta fara kaiwa a mota sannan ta dawo ta dauki sauran.

“Zaka shigo anjima?”

“No maybe gobe shi ma maybe”

“Okay sai anjima, a sha aikin lafiya”

“Thank you Sis, be a good girl please”

“I will.... See you soon”

Ta ja kofar ta rufe masa, tare da rakiyar wani sojan ta fita gurin zancen gilashin da ya bawa Hurriya ya tsaya mata a rai, kuma yana kokarin gushe mata duk wani farinciki da take ji na sakata neman turare da yayi. Amman what if shi ba da wata manufa yayi ba? Balle ma yadda yake da halinsa anya zai iya da tafiya da Hurriya?

“Yarinyar nan tana da shegen kyau zata iya jan hankalinsa kamar yadda ta ja hankalin Salim, gashi har yana fadar wai ta yi sa'a yana iya controlling kansa”

Ta amsawa kanta da kanta tana juya sitiyarin motar, zuciyarta na raya mata karya da gaskiya deep down inside her ta san she feels jealous why zai bata gilashi bayan ta ki farko few years back, and why ma zai ce ta kawo masa abinci?

“Saboda kin tafi siyo masa turare Namra, shi ma abun alfahari ne zai saka turaren da kika siya masa so wannan ma ba wani abun daga hankali ba ne”

Ta bawa kanta amsa a daidai lokacin da masu gadin gidan suka bude mata gate. Misalin karfe 8:30pm Hurriya na dakinta kwance ta soma jin kara kamar ana jifan gilashin windows dinta, bata saka ran wani zai yi haka, wannan ya sska bata damu ta tashi ta duba ba, har sai da ta ji jifan yayi yawa, sannan ta sauka daga kan gadon ta nufi windows, curtains din ta fara dagewa ta leka waje mutum ya hango sanye da kananan kaya komai fari, ta bude window tana kallon Captain dake kasa, sai ya jefar da dutsen dake hannunsa ya dago dayan hannunsa dake rike da karamin bokitin roba ya nuna mata sannan ya aje a kasa, ya nufi hanyar da kofar falon Momy yake, ta nan kam ba zaka iya hango wanda zai fito ko ya shiga falon na Momy ba. Kamar yadda wanda ke tsaye a bakin kofar baya iya ganin wanda ke sama har sai ya fito daga gurin. A bude ta bar window ta juyo da sauri ta bude karamin teburinta dake gurin ta dauko takardar da pen ta yi rubutu a jiki da girma yadda zai gani sannan ta nade takardar a hannunta ta nufi kofar fita ta bude ta sauka falon. Ko da wasa be kalli inda take ba yana ta magana da Momy dake tambayarta ya aiki.

“Aiki kam akwai shi kwana biyu nan, yanzu haka a gajiye nake i need to rest gobe ma da wuri zamu fara”

“Namra ta fada min ta same ka kana ta aiki dazun, daman kuna haka ne”

“Yeah idan ana karshen shekara da kuma canjin duty ana samun irin haka, lafiya kalau”
Chapter 90 · 0% Book details