Sashe 101
Huriyya Part 1 And 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Dan Allah ki bawa Rukayya hakuri, kuma ki lallaba Gwaggo kar ta yo fushi, ni kaina ban jidadin abun da ya faru ba, gaba daya na rasa gane abun da ke min dadi gidan nan ya rikice, mun rasa Salma, Hajiya ba zata karbi soyayya ta Rukayya ba, Hajiya kuma tana asibiti yanzu haka? Gaba dayana rasa ina zan saka kaina na ji sanyi”
“Asibiti bata da lafiya?”
“Suma ta yi, amman da sauki gobe ma Appa yace ba za'ayi zaman gaisuwa ba, shiyasa aka yi addu'a uku a yau”
An yi addu'an uku kuma bata sani ba? Ta tambayi kanta.
“Ban san an yi ba, kuma ban san an kai Hajiya asibiti ba”
“Kina cikin daki koda yaushe Hurriya ya za'ayi ki sani, kin zaman dabam”
“Bana jindadin shiga cikin mutane ne, wani lokacin ina tsarguwa”
Ta dora hannunsa biyu a sitiyarin motar.
“I understand your situation now...”
Daga haka be kara cewa komai ba, har suka isa gidan.
“Ki aje su ki dawo na maida ke”
“Toh”
Ta amsa sai a lokacin ta tuna da siyayyar da Captain yayi musu bata ba su ba, kuma bata isa tace Yasir ya koma su dauko ba. Haka ta shiga cikin gidan tare da yaran ta mika su hannun Gwaggo tana fada mata abun da Appa yayi musu a jiya, Amma ta kalleta yanayin fuskarta ya nuna akwai damuwa da magana mai yawa a tare da ita amman babu bakin fada.
“A da yardar Allah komai zai warware, sai ta ga Iyami ta tashi da idonta, amman zaman aure kam ko da ya dawo yace zai maida Iyami ba zan yarda ba, aure ya kare kenan Allah ya bata na gari, wannan wahala da ta sha ta isa haka, amman wai duk wannan abun Rukayya bata gani ba saboda rashin hankali da tunani take kokarin daukar kanta ta jefa a gurin Kaltume? Me ake da Kaltume me ake da jininta? Har abada ko ba ni da rayuwa Rukayya ba zaki auri Yasir ba, sai dai ki mutu babu aure, na Iyami ma kaddara ce da ba mu isa mu kauce mata ba”
Rukayya ta mike tsaye ta fice daga falon gudun hawayen da suka tarar mata kar su zubar mata a gaban Gwaggo ta sha fada, daman tun jiya take mata masifa har yau da dare. Hurriya ta kalli Gwaggo cikin yanayin rashin dadi ta ce.
“Gwaggo ko da tana son komawa? Yanzu idan Appa ya zo yace ta yi hakuri ta dawo ba zata dawo ba?”
“Bata ma so! Auren babanki da Iyami rabuwa ce ta har abada”
Hurriya bata saurari maganar Gwaggo ba, ta matsa kusa da Iyami ta kama hannunta ta rike.
“Amma wai baki son komawa ki zauna tare da mu? Idan kika ji sauki? Kowa yana da uwa a gidan mu kadai ne ba mu da”
Amma bata ce mata komai ba, daman kuma ba zata ce ba domin bata iya magana a yanzu.
“Amma ki matsa hannuna sau daya idan zaki koma, idan ba zaki koma ba ki matsa hannuna sau biyu”
Babu bata lokaci Amma ta matsa hannunta sau biyu ta girgiza mata kai. Gwaggo ta ce.
“To ki cire rai daga yau, ki dai fatan uwarki ta samu lafiya, kuma ta samu talaka irinta mai mutunci ta aura, kishi da Kaltume kam an gama har abada, miji dai take tutiya, to an bar mata shi ta dafa ta ci, wannan bakin kishin ya isa haka akan ƴata, tsabar hauka har Rukayya take son jajibo mana wani aiki, sakaryar yarinyar kawai”
Hurriya ta mike tsaye tana jin kamar ta fashe da kuka ta fice daga falon ba tare da tayi musu sallama ba. A lokacin da ta fito cikin gidan sai tausayinta ya kama Yasir ba dan ya san abun da ya gudana a tsakaninsu ba, sai dan a yanzu ya san yadda zafin rabuwar auren iyaye yake, saboda abun da ya faru tsakanin Appa da Hajiya Kaltume a yau, shi da yake babba kenan balle kuma ita da abun da ya faru tana karama, a yanzu ya kara yarda idan iyaye suka samu tsabani har ta kai ga rabuwa yara yake taɓawa fiye da yadda yake taɓa iyayen, ya ga halin da kanensa suka shiga da kuma mahaifiyarsa ga shi shi kansa abun ya haifar masa da damuwa balle kuma Hurriya da take karama da kanenta da su ma a yanzu suke tasowa.
Ta bude motar ta shiga ta rufe motar tana jin kamar ta fashe da kuka. Be mata uffan ba shi ma ta shi damuwar ta isheshi baya son ya tambaya ta fada masa Gwaggo ta fadi wata magana akansa ko ga Rukayya ko kuma ta mata fada saboda shi.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
34
𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘
Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660
𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲
After ya rufe motarsa ya bude back seat ya dauko katuwar ledar ya rufe motar ya nufi falon Momy. Sai da ya fara danna door bell sannan ya murda kofar ya shiga. Momy na zaune falon Namra ma kwance a doguwar kujera suna zancen Hajiya Kaltume, sai dai shigowar Captain ya saka duk suka yi shiru, Namra ta tashi zaune tana masa sannu da zuwa, but still yana jin babu dadi a yadda ya nunawa Hurriya kulawa a dazun.
“Captain yanzu ake tafe”
Momy ta fada, sai ya dora ledar a kujera yana daga tsaye yana murmushi ya amsa mata.
“Ni ma ban sa ran zan dawo yanzu ba, tafiya ce ta kama ni gobe da safe zan bar garin nan?”
“Lafiya dai?”
“Yanayin aikin ne, zan yi 1 week a Kaduna”
“Da sauki ai, gida zaka je”
“Da can nafi son Kaduna, yanzu kuma na fi son nan”
Namra ta yi murmushi.
“Gashi kuma ka kusan gama aikinka na nan ai, ka koma KD gaba daya”
“Ina tunanin Daddy zan yi ma magana, a san yadda za'ayi a bar ni garin nan, domin idan na koma Kaduna ba zan samu zuwa nan ba. Ina Hurriya?”
Momy ta sake dubansa bayan kallon da take masa da dan mamaki ta ce.
“Hurriya kuma?”
“Yea na siyawa twins dinta abu ne, kin san yadda nake son yara”
Ya amsa yana murmushi acting like bakin gaskiyarsa yaran ya kawo wa.
“Yaran ma ta tafi ta kai gida ai, ba nan suke zama ba”
“I know tsaraba ce bari na aje a dakinta”
Ya dauki ledar sai Namra ta mike tsaye.
“Let me help you”
“No please ajewa kawai zan yi na fito”
“To ai bata nan kuma yaran sun riga sun tafi”
Cewar Namra tana kallonsa da shakku a idonta. A take ransa ya bace ganin tana kokarin kure shi.
“That's right idan ta dawo sai ta zuba ashara”
Ya dauke kansa ya nufi stairs rike da ledar, har dakinta ya shiga ya aje mata ledar kan gado ya juyo zai fito sai kuma ya juya yana karewa dakin kallo, karamin gado ne daidai ita sai mirror da closet dinta daga gefe. Ya taka ya isa closet din ya bude yana kallo, can kuma ya rufe ya dawo gurin mirror yana duba kalolin mai da turare dake gurin, ya kai hannunsa ya bude durowar dake jikin mirror a nan kuma yan kunne da sarka ne sai agogo daga kasa kuma hotuna ne. Hotunan ya dauka ya shiga dubawa, wani gurin ita da Hamad ne wani da Amma wani kuma family pictures ne su hudu, wani kuma ita da Appa babu wanda take ita kadai sai wanda take karama, inda take rarrafe wani kuma ta fara tashi dayan lokacin da ta kare primary. Murmushi yayi ya juya ya kalli kofar dakin dake bude sannan ya dawo da idonsa gurin mirror ya sake dauko wasu hotunan dake aje gefe daya, su kan nata ne inda take ita kadai sai kuma wandanda ta yi ranar birthday ta sun yi kyau sosai ko'ina kuma tana sanye da abokin rayuwarta ne wato glasses. Hannunsa ya saka aljihu ya ciro wayarsa ya dora hotunan yana ta dauka hoto sai da ya gama sannan ya maida su a muhallinsu ya dauko awarwaronta ya duba ya dauki zoben dake tare da sarka ya duba sannan ya aje ya rufe mata gurin ya maida wayarsa aljihu ya fice daga dakin ya ja mata kofa. Da sassarfa ya sauko stairs din kana ganinsa ka san a hanzarce yake.
“Momy zan tafi sai mun yi waya, sauri nake akwai mai jirana”
Mamaki ya hana Momy ce masa komai har ya fice. Namra ta daki hannun kujerar.
“Me na gama fada miki yanzu Momy? Kin ga gani ko?”
“Asibiti bata da lafiya?”
“Suma ta yi, amman da sauki gobe ma Appa yace ba za'ayi zaman gaisuwa ba, shiyasa aka yi addu'a uku a yau”
An yi addu'an uku kuma bata sani ba? Ta tambayi kanta.
“Ban san an yi ba, kuma ban san an kai Hajiya asibiti ba”
“Kina cikin daki koda yaushe Hurriya ya za'ayi ki sani, kin zaman dabam”
“Bana jindadin shiga cikin mutane ne, wani lokacin ina tsarguwa”
Ta dora hannunsa biyu a sitiyarin motar.
“I understand your situation now...”
Daga haka be kara cewa komai ba, har suka isa gidan.
“Ki aje su ki dawo na maida ke”
“Toh”
Ta amsa sai a lokacin ta tuna da siyayyar da Captain yayi musu bata ba su ba, kuma bata isa tace Yasir ya koma su dauko ba. Haka ta shiga cikin gidan tare da yaran ta mika su hannun Gwaggo tana fada mata abun da Appa yayi musu a jiya, Amma ta kalleta yanayin fuskarta ya nuna akwai damuwa da magana mai yawa a tare da ita amman babu bakin fada.
“A da yardar Allah komai zai warware, sai ta ga Iyami ta tashi da idonta, amman zaman aure kam ko da ya dawo yace zai maida Iyami ba zan yarda ba, aure ya kare kenan Allah ya bata na gari, wannan wahala da ta sha ta isa haka, amman wai duk wannan abun Rukayya bata gani ba saboda rashin hankali da tunani take kokarin daukar kanta ta jefa a gurin Kaltume? Me ake da Kaltume me ake da jininta? Har abada ko ba ni da rayuwa Rukayya ba zaki auri Yasir ba, sai dai ki mutu babu aure, na Iyami ma kaddara ce da ba mu isa mu kauce mata ba”
Rukayya ta mike tsaye ta fice daga falon gudun hawayen da suka tarar mata kar su zubar mata a gaban Gwaggo ta sha fada, daman tun jiya take mata masifa har yau da dare. Hurriya ta kalli Gwaggo cikin yanayin rashin dadi ta ce.
“Gwaggo ko da tana son komawa? Yanzu idan Appa ya zo yace ta yi hakuri ta dawo ba zata dawo ba?”
“Bata ma so! Auren babanki da Iyami rabuwa ce ta har abada”
Hurriya bata saurari maganar Gwaggo ba, ta matsa kusa da Iyami ta kama hannunta ta rike.
“Amma wai baki son komawa ki zauna tare da mu? Idan kika ji sauki? Kowa yana da uwa a gidan mu kadai ne ba mu da”
Amma bata ce mata komai ba, daman kuma ba zata ce ba domin bata iya magana a yanzu.
“Amma ki matsa hannuna sau daya idan zaki koma, idan ba zaki koma ba ki matsa hannuna sau biyu”
Babu bata lokaci Amma ta matsa hannunta sau biyu ta girgiza mata kai. Gwaggo ta ce.
“To ki cire rai daga yau, ki dai fatan uwarki ta samu lafiya, kuma ta samu talaka irinta mai mutunci ta aura, kishi da Kaltume kam an gama har abada, miji dai take tutiya, to an bar mata shi ta dafa ta ci, wannan bakin kishin ya isa haka akan ƴata, tsabar hauka har Rukayya take son jajibo mana wani aiki, sakaryar yarinyar kawai”
Hurriya ta mike tsaye tana jin kamar ta fashe da kuka ta fice daga falon ba tare da tayi musu sallama ba. A lokacin da ta fito cikin gidan sai tausayinta ya kama Yasir ba dan ya san abun da ya gudana a tsakaninsu ba, sai dan a yanzu ya san yadda zafin rabuwar auren iyaye yake, saboda abun da ya faru tsakanin Appa da Hajiya Kaltume a yau, shi da yake babba kenan balle kuma ita da abun da ya faru tana karama, a yanzu ya kara yarda idan iyaye suka samu tsabani har ta kai ga rabuwa yara yake taɓawa fiye da yadda yake taɓa iyayen, ya ga halin da kanensa suka shiga da kuma mahaifiyarsa ga shi shi kansa abun ya haifar masa da damuwa balle kuma Hurriya da take karama da kanenta da su ma a yanzu suke tasowa.
Ta bude motar ta shiga ta rufe motar tana jin kamar ta fashe da kuka. Be mata uffan ba shi ma ta shi damuwar ta isheshi baya son ya tambaya ta fada masa Gwaggo ta fadi wata magana akansa ko ga Rukayya ko kuma ta mata fada saboda shi.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
34
𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘
Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660
𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲
After ya rufe motarsa ya bude back seat ya dauko katuwar ledar ya rufe motar ya nufi falon Momy. Sai da ya fara danna door bell sannan ya murda kofar ya shiga. Momy na zaune falon Namra ma kwance a doguwar kujera suna zancen Hajiya Kaltume, sai dai shigowar Captain ya saka duk suka yi shiru, Namra ta tashi zaune tana masa sannu da zuwa, but still yana jin babu dadi a yadda ya nunawa Hurriya kulawa a dazun.
“Captain yanzu ake tafe”
Momy ta fada, sai ya dora ledar a kujera yana daga tsaye yana murmushi ya amsa mata.
“Ni ma ban sa ran zan dawo yanzu ba, tafiya ce ta kama ni gobe da safe zan bar garin nan?”
“Lafiya dai?”
“Yanayin aikin ne, zan yi 1 week a Kaduna”
“Da sauki ai, gida zaka je”
“Da can nafi son Kaduna, yanzu kuma na fi son nan”
Namra ta yi murmushi.
“Gashi kuma ka kusan gama aikinka na nan ai, ka koma KD gaba daya”
“Ina tunanin Daddy zan yi ma magana, a san yadda za'ayi a bar ni garin nan, domin idan na koma Kaduna ba zan samu zuwa nan ba. Ina Hurriya?”
Momy ta sake dubansa bayan kallon da take masa da dan mamaki ta ce.
“Hurriya kuma?”
“Yea na siyawa twins dinta abu ne, kin san yadda nake son yara”
Ya amsa yana murmushi acting like bakin gaskiyarsa yaran ya kawo wa.
“Yaran ma ta tafi ta kai gida ai, ba nan suke zama ba”
“I know tsaraba ce bari na aje a dakinta”
Ya dauki ledar sai Namra ta mike tsaye.
“Let me help you”
“No please ajewa kawai zan yi na fito”
“To ai bata nan kuma yaran sun riga sun tafi”
Cewar Namra tana kallonsa da shakku a idonta. A take ransa ya bace ganin tana kokarin kure shi.
“That's right idan ta dawo sai ta zuba ashara”
Ya dauke kansa ya nufi stairs rike da ledar, har dakinta ya shiga ya aje mata ledar kan gado ya juyo zai fito sai kuma ya juya yana karewa dakin kallo, karamin gado ne daidai ita sai mirror da closet dinta daga gefe. Ya taka ya isa closet din ya bude yana kallo, can kuma ya rufe ya dawo gurin mirror yana duba kalolin mai da turare dake gurin, ya kai hannunsa ya bude durowar dake jikin mirror a nan kuma yan kunne da sarka ne sai agogo daga kasa kuma hotuna ne. Hotunan ya dauka ya shiga dubawa, wani gurin ita da Hamad ne wani da Amma wani kuma family pictures ne su hudu, wani kuma ita da Appa babu wanda take ita kadai sai wanda take karama, inda take rarrafe wani kuma ta fara tashi dayan lokacin da ta kare primary. Murmushi yayi ya juya ya kalli kofar dakin dake bude sannan ya dawo da idonsa gurin mirror ya sake dauko wasu hotunan dake aje gefe daya, su kan nata ne inda take ita kadai sai kuma wandanda ta yi ranar birthday ta sun yi kyau sosai ko'ina kuma tana sanye da abokin rayuwarta ne wato glasses. Hannunsa ya saka aljihu ya ciro wayarsa ya dora hotunan yana ta dauka hoto sai da ya gama sannan ya maida su a muhallinsu ya dauko awarwaronta ya duba ya dauki zoben dake tare da sarka ya duba sannan ya aje ya rufe mata gurin ya maida wayarsa aljihu ya fice daga dakin ya ja mata kofa. Da sassarfa ya sauko stairs din kana ganinsa ka san a hanzarce yake.
“Momy zan tafi sai mun yi waya, sauri nake akwai mai jirana”
Mamaki ya hana Momy ce masa komai har ya fice. Namra ta daki hannun kujerar.
“Me na gama fada miki yanzu Momy? Kin ga gani ko?”