Sashe 46
Huriyya Part 1 And 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hajiya ta fada tana nuna Ruma da har lokacin bata ce komai ba, sai ma juyawa da ta yi ta koma sama, gaba daya ta canja tun bayan da ta dawo daga hannun masu garkuwa da mutane ta tsani gidan da mutanen cikinsa, ba kasafai zaka ganta a wani abu da kowa yake tarayya ba, wannan dalilin ya hanata zuwa birthday din Khairi kuwa da kusanci na kasancewarta yar'uwarta. Hajiya kamar wata gurguwa haka ta hau sama daker ta shiga nata dakin ta dauko mayafinta da jakarta sannan ta kira direba ta fasa masa ya kunna mota za su fita. Sai da ya shiga dakin Khairi sai ta same ta har lokacin kuka take tana zaune a kasa.
“Ba zaki je ba na tafi? Ba saboda zuwanki ne kadai ba ina son na kai kafar nan a duba min”
Cikin kuka Khairi ta kalleta ta ce
“Hajiya ba ki ga wulakanci da Hurriya taja aka yi min ba Wallahi, Yaya ya wulakanta ni gaban friends dina”
“Toh ya zaki yi sai ki yi hakuri munafurci daman ai ya cikawa Hurriya ciki, ganewa ne ba a yi sai yanzu amman na san maganinta ai, ke ma kuma fa baki kyauta ba ni Allah yasa dai Fadeel be ganki da wannan shigar ba, abu kamar karuwar Lagos haba Khairi”
Ta tashi tana kuka ta nufi gurin da tufafinta suke ta bude, cikin kuka ta canja tufafin sannan ta biyo bayan Hajiya Kaltume da tuni ta sauka kasa.
HURRIYA POV.
Tana tsaye a waje har Yasir ya fito ransa a bace ya sake shiga motarsa da kallo ta bishi har ya fice sannan ta dan leka bangaren Hajiya Kaltume kamar zata shiga wai dan ta wanke kanta ta fadawa Khairi da Hajiya Kaltume ba ita ta zugo shi ya shigo gurin ba, sanin ba za su kwashe da dadi ba ya saka ta juya ta fice daga bangaren ta nufi bangaren Momy. A hankali ta tura kofar falon ta shiga tsoron dake cikin cikinta ya hanata sallama har ta isa tsakiyar falon.
“Salon labe ne ko kuma rainin wayo? Zaki shigo min falo babu sallama?”
“Yi hakuri Momy mantawa na yi”
Ta fada da muryarta da bata gama fita ba.
“Daga ina kika?”
“Gurin Birthday din Yaya Khairi”
Momy ta dauke kai ta cigaba da latsa wayarta, Hurriya na ganin haka ta raba ta haye sama ta shiga dakinta. Sai kusan magariba Namra ta dawo gidan, tufafinta kawai ta cire ta shiga dakin Momy tana bata labarin abun da ya faru ita kanta ta cika da mamaki irin shigar da Khairi ta yi ga kuma wasu watsassun kawayenta da bata san a ina ta samo su ba.
“To ke me kike baki dawo gida da tun dazun ba?”
“Momy ina can ina jiran wanda zai dauko ni fa, gaba daya a hargitse aka watse taron saboda Yaya Yasir ni ma ba dan na boya ba Allah kadai ya san kalar dukan da zai min”
“Ya dokeki saboda shi ya haifa ki? Ai ba zan dauki wannan ba, ya taba dinka kala daya ya kawo miki? Sai yanzu da girmanki zai ce ya saka miki hannu ya dakeki saboda bikin da kanwarsa ta shirya?”
“Momy dan baki ga bikin ba ne, bari na nuna miki dress din Khairi kamar ba yar gidan nan ba”
Ta shiga gallery wayarta ta kama hotunan da ta yi ma Khairi tana nunawa Momy.
“Momy kalli fa, ni ma raina ya bace da abun da ta yi Wallahi, ai na jidadi da Hurriya ta fadawa Yaya Yasir ya zo ya watse taron nan”
“Au Hurriyar ce ma ta fada masa abun da ake yi? Ina ta ganshi to?”
“Oho mu ma kamar daga sama muka ganshi ina ganin ya fada jibgar Khairi na boya ban bari na gan ni ba”
page 10
“Ikon Allah yaushe kuma Hurriya ta fara zama munafuka? Hada yaya da kanwa? Wannan kam ba shi da kyau ai, ko bata fada masa ba ai ya san kanwarsa zata aikata yadda take jin ita sa'ar kowa ce kawaye babu na albarka ai dole ma ta aikata, kuma Alhaji ba zai ce komai ba duk abun da Kaltume ta yi ai shi ne daidai a gidan nan ita da yaranta yanzu basa laifi”
“Gaskiya Momy kawayenta gaba daya babu na gari, wani dayan frind dinta ya zo yana yi ma Hurriya liki da dollars”
“Rawa ta yi”
“Aa Momy kin san ai ba zata yi rawa ba, Momy kin san shi ma Adam ne fa, dan gidan Sarauta”
“Ba dai dan Hajiya Nana ba?”
“Shi fa, yaron nan yana wasa da kudi”
“A ina ta san shi?”
“Ni ma ban sani ba, bari ma na tafi na tambayeta”
Ta tashi da saurinta ta bar wayar a gurin ta fice daga dakin Momy bata zame ko'ina ba sai dakin Hurriya. Cikin natsuwa irin na masu son gulma ta tura kofar dakin ta shiga, Hurriya na tsaye jikin windows, dan kwalin abayarta ya sauko saman wuyanta hannunta kuma yana wuyanta tana shafawa zuciyarta kuma ta tafi wata duniyar karatu.
“Hurriya...”
Ta juyo ta kalli yayarta, Namra ta maida kofar ta rufe ta nufi gurin da Hurriya take tsaye.
“Me kike yi”
“Ba komai kawai ina tunanin Hamad ne”
Ta fada tana sauke idonta kasa.
“Ke dai kin saka Hamad a ranki Hurriya, idan yana raye Allah ya bayyana shi idan kuma ya mutu Allah ya jikansa da Rahma”
“Amin”
Hawaye ya sauko mata.
“Da ace yana nan kusa da mu, wata kila da yanzu muna son junanmu ba kamar baya ba, wani lokacin ina jin bukatar abokin tattaunawa, har yanzu na kasa sabawa da rashinsa ina jin kadaici sosai”
“Ki yi ta addu'a abun zai cire miki In Shaa Allah, amman shiga damuwar da kike ina tunanin shi ne silar daya kara jefa Amma cikin damuwa”
“Ina kokari Yaya Namra bana bari ta gane ina cikin damuwa”
“Haka na da kyau, yauwa Hurriya kin san wannan wanda yayi miki karin kudi dazu?”
Ta share hawayenta da gefen hannun rigar abayar.
“Aa ban san shi ba, dazun ne ma na fara ganinsa”
“Toh amman kuma yake miki karin kudin haka nan kawai?”
“Ni ma abun ya ba ni mamaki sunana ma ban san inda ya ji ba”
“Maybe ko ya sanki wani gurin ke ce baki san shi ba”
“Ni da ba fita nake ba, amman ni ma mamaki nake”
“Toh ki yi hankali da shi yaron nan dan shaye shaye ne”
Ta amsa mata kai kamin ta ce.
“Yaya Namra dan Allah zaki taimaka min na fadawa Hajiya ba ni na kira Ya Yasir ya shiga ciki ba?”
“To waya kira shi?”
“Ni amman na ce masa ya zo ya dauke ni ne kawai saboda wannan saurayin ya takura min kuma ba ni da wanda zai kai ni gida, amman WallahI ban ce ya shiga ciki ba”
“To ai ke kika yi kuskuren Hurriya kema kin san dole zai shiga ai, kuma yanzu babu mai wanke ki a gurin Hajiya”
“Ba Hajiya kadai nake tsoro ba, har da Yaya Khairi na san ni zata dorawa laifin”
“To kije ki ba su hakuri mana”
“Zan yi haka”
Ta fada cikin yanayin damuwa wasu hawayen na kara cika idonta. Namra ta fice tare da ja mata kofa. Hurriya ta kai hannu ta taba hancinta kamin ta dago ta sake juyawa top side view ta rumgume hannayenta.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
page 11
Misalin tara da rabi Hurriya na zaune dakinta ta ji an kwankwasa kofa, tana jin haka ta san wanda be saba shigowa dakin ba ne domin Momy ko Namra basa kwankwasa mata kofa balle kuma Miwan da Musib da basa gidan ma. Ta tashi da saurinta ta nufi kofar ta bude sai ta yi arba da Ruma.
“Appa na kiranki”
“Ni”
Ta nuna kanta, Ruma ta daga mata kai.
“Eh”
Ta juya ta bar kofar ta fara sauka kasa, Hurriya bata tsaya komai ba ta bi bayanta tana sanye da kayan bachi kanta sanye da hular saka. Ruma na gaba Hurriya na bayanta tana jin kamar ta tambaye ta me ya faru kuma dai bata tambaya ba. Cikin tsoro da fargaba ta shiga falon na Hajiya Kaltume gabanta na faduwa. Hankalinta be kara tashi ba sai da ta yi arba da fuskar mahaifinta dake hade babu annuri a tare da shi, bata yarda ta karasa cikin falon ba ta tsaya daga jikin kofa cike da ladabi ta ce
“Appa ga ni”
“Okay tasowa zan yi na iskoki can kenan? Ni zan same ki a inda kike na yi magana da ke ko?”
“Aa Appa ka yi hakuri dan Allah”
“Ba zaki je ba na tafi? Ba saboda zuwanki ne kadai ba ina son na kai kafar nan a duba min”
Cikin kuka Khairi ta kalleta ta ce
“Hajiya ba ki ga wulakanci da Hurriya taja aka yi min ba Wallahi, Yaya ya wulakanta ni gaban friends dina”
“Toh ya zaki yi sai ki yi hakuri munafurci daman ai ya cikawa Hurriya ciki, ganewa ne ba a yi sai yanzu amman na san maganinta ai, ke ma kuma fa baki kyauta ba ni Allah yasa dai Fadeel be ganki da wannan shigar ba, abu kamar karuwar Lagos haba Khairi”
Ta tashi tana kuka ta nufi gurin da tufafinta suke ta bude, cikin kuka ta canja tufafin sannan ta biyo bayan Hajiya Kaltume da tuni ta sauka kasa.
HURRIYA POV.
Tana tsaye a waje har Yasir ya fito ransa a bace ya sake shiga motarsa da kallo ta bishi har ya fice sannan ta dan leka bangaren Hajiya Kaltume kamar zata shiga wai dan ta wanke kanta ta fadawa Khairi da Hajiya Kaltume ba ita ta zugo shi ya shigo gurin ba, sanin ba za su kwashe da dadi ba ya saka ta juya ta fice daga bangaren ta nufi bangaren Momy. A hankali ta tura kofar falon ta shiga tsoron dake cikin cikinta ya hanata sallama har ta isa tsakiyar falon.
“Salon labe ne ko kuma rainin wayo? Zaki shigo min falo babu sallama?”
“Yi hakuri Momy mantawa na yi”
Ta fada da muryarta da bata gama fita ba.
“Daga ina kika?”
“Gurin Birthday din Yaya Khairi”
Momy ta dauke kai ta cigaba da latsa wayarta, Hurriya na ganin haka ta raba ta haye sama ta shiga dakinta. Sai kusan magariba Namra ta dawo gidan, tufafinta kawai ta cire ta shiga dakin Momy tana bata labarin abun da ya faru ita kanta ta cika da mamaki irin shigar da Khairi ta yi ga kuma wasu watsassun kawayenta da bata san a ina ta samo su ba.
“To ke me kike baki dawo gida da tun dazun ba?”
“Momy ina can ina jiran wanda zai dauko ni fa, gaba daya a hargitse aka watse taron saboda Yaya Yasir ni ma ba dan na boya ba Allah kadai ya san kalar dukan da zai min”
“Ya dokeki saboda shi ya haifa ki? Ai ba zan dauki wannan ba, ya taba dinka kala daya ya kawo miki? Sai yanzu da girmanki zai ce ya saka miki hannu ya dakeki saboda bikin da kanwarsa ta shirya?”
“Momy dan baki ga bikin ba ne, bari na nuna miki dress din Khairi kamar ba yar gidan nan ba”
Ta shiga gallery wayarta ta kama hotunan da ta yi ma Khairi tana nunawa Momy.
“Momy kalli fa, ni ma raina ya bace da abun da ta yi Wallahi, ai na jidadi da Hurriya ta fadawa Yaya Yasir ya zo ya watse taron nan”
“Au Hurriyar ce ma ta fada masa abun da ake yi? Ina ta ganshi to?”
“Oho mu ma kamar daga sama muka ganshi ina ganin ya fada jibgar Khairi na boya ban bari na gan ni ba”
page 10
“Ikon Allah yaushe kuma Hurriya ta fara zama munafuka? Hada yaya da kanwa? Wannan kam ba shi da kyau ai, ko bata fada masa ba ai ya san kanwarsa zata aikata yadda take jin ita sa'ar kowa ce kawaye babu na albarka ai dole ma ta aikata, kuma Alhaji ba zai ce komai ba duk abun da Kaltume ta yi ai shi ne daidai a gidan nan ita da yaranta yanzu basa laifi”
“Gaskiya Momy kawayenta gaba daya babu na gari, wani dayan frind dinta ya zo yana yi ma Hurriya liki da dollars”
“Rawa ta yi”
“Aa Momy kin san ai ba zata yi rawa ba, Momy kin san shi ma Adam ne fa, dan gidan Sarauta”
“Ba dai dan Hajiya Nana ba?”
“Shi fa, yaron nan yana wasa da kudi”
“A ina ta san shi?”
“Ni ma ban sani ba, bari ma na tafi na tambayeta”
Ta tashi da saurinta ta bar wayar a gurin ta fice daga dakin Momy bata zame ko'ina ba sai dakin Hurriya. Cikin natsuwa irin na masu son gulma ta tura kofar dakin ta shiga, Hurriya na tsaye jikin windows, dan kwalin abayarta ya sauko saman wuyanta hannunta kuma yana wuyanta tana shafawa zuciyarta kuma ta tafi wata duniyar karatu.
“Hurriya...”
Ta juyo ta kalli yayarta, Namra ta maida kofar ta rufe ta nufi gurin da Hurriya take tsaye.
“Me kike yi”
“Ba komai kawai ina tunanin Hamad ne”
Ta fada tana sauke idonta kasa.
“Ke dai kin saka Hamad a ranki Hurriya, idan yana raye Allah ya bayyana shi idan kuma ya mutu Allah ya jikansa da Rahma”
“Amin”
Hawaye ya sauko mata.
“Da ace yana nan kusa da mu, wata kila da yanzu muna son junanmu ba kamar baya ba, wani lokacin ina jin bukatar abokin tattaunawa, har yanzu na kasa sabawa da rashinsa ina jin kadaici sosai”
“Ki yi ta addu'a abun zai cire miki In Shaa Allah, amman shiga damuwar da kike ina tunanin shi ne silar daya kara jefa Amma cikin damuwa”
“Ina kokari Yaya Namra bana bari ta gane ina cikin damuwa”
“Haka na da kyau, yauwa Hurriya kin san wannan wanda yayi miki karin kudi dazu?”
Ta share hawayenta da gefen hannun rigar abayar.
“Aa ban san shi ba, dazun ne ma na fara ganinsa”
“Toh amman kuma yake miki karin kudin haka nan kawai?”
“Ni ma abun ya ba ni mamaki sunana ma ban san inda ya ji ba”
“Maybe ko ya sanki wani gurin ke ce baki san shi ba”
“Ni da ba fita nake ba, amman ni ma mamaki nake”
“Toh ki yi hankali da shi yaron nan dan shaye shaye ne”
Ta amsa mata kai kamin ta ce.
“Yaya Namra dan Allah zaki taimaka min na fadawa Hajiya ba ni na kira Ya Yasir ya shiga ciki ba?”
“To waya kira shi?”
“Ni amman na ce masa ya zo ya dauke ni ne kawai saboda wannan saurayin ya takura min kuma ba ni da wanda zai kai ni gida, amman WallahI ban ce ya shiga ciki ba”
“To ai ke kika yi kuskuren Hurriya kema kin san dole zai shiga ai, kuma yanzu babu mai wanke ki a gurin Hajiya”
“Ba Hajiya kadai nake tsoro ba, har da Yaya Khairi na san ni zata dorawa laifin”
“To kije ki ba su hakuri mana”
“Zan yi haka”
Ta fada cikin yanayin damuwa wasu hawayen na kara cika idonta. Namra ta fice tare da ja mata kofa. Hurriya ta kai hannu ta taba hancinta kamin ta dago ta sake juyawa top side view ta rumgume hannayenta.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
page 11
Misalin tara da rabi Hurriya na zaune dakinta ta ji an kwankwasa kofa, tana jin haka ta san wanda be saba shigowa dakin ba ne domin Momy ko Namra basa kwankwasa mata kofa balle kuma Miwan da Musib da basa gidan ma. Ta tashi da saurinta ta nufi kofar ta bude sai ta yi arba da Ruma.
“Appa na kiranki”
“Ni”
Ta nuna kanta, Ruma ta daga mata kai.
“Eh”
Ta juya ta bar kofar ta fara sauka kasa, Hurriya bata tsaya komai ba ta bi bayanta tana sanye da kayan bachi kanta sanye da hular saka. Ruma na gaba Hurriya na bayanta tana jin kamar ta tambaye ta me ya faru kuma dai bata tambaya ba. Cikin tsoro da fargaba ta shiga falon na Hajiya Kaltume gabanta na faduwa. Hankalinta be kara tashi ba sai da ta yi arba da fuskar mahaifinta dake hade babu annuri a tare da shi, bata yarda ta karasa cikin falon ba ta tsaya daga jikin kofa cike da ladabi ta ce
“Appa ga ni”
“Okay tasowa zan yi na iskoki can kenan? Ni zan same ki a inda kike na yi magana da ke ko?”
“Aa Appa ka yi hakuri dan Allah”