Sashe 4
Huriyya Part 1 And 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Bana son ki bar min komai duk wani abun da na siya miki tun daga kayan daki har tufafi da duk wani abun more rayuwa, mallakinki ne zan saka a kawo miki har gida, amman dan Allah ki bar min Yayana a hannuna ban yarda ki tafi da ko daya ba, cikin dake jikinki ma idan kin haihu zan dawo da abu na a gidana”
Sai a lokacin ta samu kuzarin bude bakin da yayi mata nauyi ta yi magana.
“Babu uwar da zata so wasu yayan kamar nata, kuma babu yayan da za su jidadin wata uwar kamar ta su, musamman a gida irinka”
“Kin fi kowa sanin yadda nake son ƴaƴana, da uwa ko babu uwa za su jidaɗin zama a gidan mahaifinsu, zan kula da su”
Ta haɗe wani abun da ya tsaya mata ta miƙe tsaye da tunani kala kala, ta bude takardar ta duba me ke ciki saki ne ko akasin haka? Idan sakin ne saki nawa ne? Ko kuma dai ta faɗi a ƙasa ta yi masa kuka ta roƙi ya maida ita bayan ya faɗa mata baya jin natsuwa da kwanciyar hankalin a zamansa da ita yanzu?
“Allah yasa hakan shi ne alheri, kuma ya baka ikon kula da su Hurriya da Hamad”
Ita kanta sautin murya mai kama da tata take jin tana fita a bakinta, domin bata da tabbacin tana da kuzarin furta masa wani abu a yanzu. Tana jan ƙofar ɗakin nasa ta ji ƙafafuwanta sun yi nauyi, mararta ta murɗa wani irin tashin hankalin da bata taɓa samun kanta a ciki ba ya baibayeta. Da gaske Appan Hurriya sakinta yayi? Anya zata iya tafiya ta bar ƴaƴanta? Ko dai wasa yake mata wata ƙila kuma wunin yau gaba ɗaya be faru ba. Tana tafiya jini na mata zuba amman bata sani ba zafin zaton sakin da bata tabbatar ba ya manta da ita zafin mararta dake murɗawa, ya hana hankalinta kusanto jikinta ya juya tunaninta a gurin abun da bata taɓa mafarkin faruwarsa ba.
Arzikinta ɗaya, ko wane part an yi masa corridor da zai sada ɓangaren da ɓangaren Alhaji Haruna ba sai ta gaban gidan ba. Kuma zaka iya fita ko shiga ba tareda sanin kowa ba, har sai idan mutum ya isa part ɗin. Kamar wadda ta sha giya haka ta isa ɓangarenta ta zarce bedroom ɗinta ta zauna a kan gadonta.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”
Ta furta daker tana kokarin dawowa hayyacinta.
“Haka ake ji? Haka saki yake? Ko dan ina da kurciya ne? Ko kuma saboda ban saka tsammanin zuwan sakin ba ne gaba daya a zaman rayuwata? Ko kuma saboda ina tsoron barin ƴaƴana ne? Allah ka sassauta min, ka saka min natsuwa da kwanciyar hankali, ka hallata aure ka hallata saki, Allah ka yaye min wannan damuwar da zata rufe ni, Ubangiji ka tsaya min”
Rahamar Allah ga bayinsa, da kuma dace ya ƴan amin a kusa, tana gama addu'ar ta ji natsuwa ta sauko mata, numfashin da take jin kamar zai danne mata kirji ya daga mata, mararta ta sake murdawa har sai da ta lumshe ido ta kai hannunta ta taba cikin dake jikinta na wata shida.
Kamar wadda aka yi ma allurar kuzari haka ta tashi ta aje takardun hannunta ta shiga bandaki ta gyara kanta ta fito ta gyara dakin inda ta ɓata ta cire Bedsheet din ta bar gadon a haka, ta dauki ruwa da tsumma ta bi tana goge jinin da bata san ya zuba ba sai a lokacin. Kamar mai shirin yin sata haka ta shiga ɓangaren ta goge jinin sannan ta juyo gabanta na tsananta faɗuwa ta fito daga ɓangaren. Ganin jinin yaƙi tsaya mata ya saka ta sake tsabtace jikinta ta saka pant da pad ta tare sannan ta kwanta saman gadon tana sauraren zuciyarta da ke bugawa da karfi, mararta kuma na cigaba da murdawa.
“Me na yi ma Appan Hurriya?”
Shi ne abun da take ta tambayar kanta, tambayar da bata da amsarta, mulmulawa ta yi saman gadon tana karewa katon dakinta kallo kamin ta tashi zaune ta fashe da kuka mai karfi, a rayuwarta bata taba fuskarta wani abu na tashin hankali irin yau ba. Cikin kuka da bakinciki ta dauko akwatunanta ta fara zuba kayanta ba tare da ta tsaya shiryasu ba, wani abun ma sai dai ta gwamatsa shi cikin wani talkaminta da atamfa ta saka su a kwati daya, sai da ta gama ta rufe ta kaisu gurin kofa ta aje ta dawo cikin dakin ta zauna kasa ta rasa me ya rage mata ta yi, kuma ta kasa fita daga dakin.
Misalin Karfe biyu da mintuna Bus dake dauko yaran makaranta ta shigo gidan, a harabar da aka tanada domin aje motoci direban ya faka motar. Sai da manyan suka fara fita sannan Hurriya ta fito, Hamad kan cikin manyan yayyunsu ya kutsa ya fita, daman shi yana daga cikin sarakunan kiriniya da rashin kunya na gidan, babu kalar dukan da basa masa ko hantara amman kowa yace masa kule zai ce chasss, Amma ta yi fada har ta gaji, Appa ma har baya son a kai masa kararsa domin ko ya masa fada ba zai hana gobe ya sake ba, Hamad irin yaran nan ne da ko kallonsu ka yi a karkace sai sun rama.
Hurriya na shiga part dinsu ta jefar da jakarta a kan kujera ta nufi bedroom din mahaifiyarta, a hankali ta tura kofar dakin ta shiga tsaye ta yi bakin kofar tana kallon kanenta Hamad dake ta fadawa Amma abun da ta yi masa a makaranta.
“Amma karya yake, karfe 1:30pm aka tashe mu shi ne na ce nasa yaje yayi sallah saboda bus din mu sai 2pm take zuwa ai, shi ne ya taso min fa masifa har zai yi dambe da ni gaban yan makaranta har da yan ajinsu fa”
Hamad ya juyo ya kalleta a fusace.
“Toh ina ruwanki da ni da zaki ce na tashi na yi sallah, kafiri ne ni ko bana sallah aka ce miki? Salon friends dina su fara tsokana ta suna cewa bana son sallah”
“Na ji ba zan sake maka magana ba, amman ni ma karka sake zuwa class dinmu ka ce na ara maka wani abu, ba ruwana da kai karka sake taba min komai kuma safata da ka saka yau ban yafe ba karka sake min taba min komai”
Amma ta mike tsaye tana kallonsu kowane zuciyarsa ta kawo kamar abokan gaba.
“Wannan fadan duk na minene wai? Ku kullum baku zaman lafiya? Kai kake binta amman kai da ita babu zaman lafiya, abinci ma ba zaku ci a plate daya ba, magana mai dadi babu tsakaninku kullum sai fada?”
Hamad ya ce.
“Ita ce bata ba ni respect ai”
“How? Kai ne babba or ni? Ni ce babba ai kai ya kamata ka ba ni respect”
“Ni ba zan taba baki respect ba i hate you kuma kika sake min wata maganar banza sai na ballaki”
Hamad na kaiwa nan ya juya ya fice rike da jakarsa har yana bankade Hurriya.
“Amma kin ga ko? Imagine”
Amma ta dafe kanta ta zauna bakin gadon tana fashewa da kuka.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”
A take jikin Hurriya yayi sanyi ta bar jikin kofar ta karasa inda Amma take ta zauna kusa da ita, domin suna yawan samun tsabani da Hamad saboda rashin jituwa dake tsakaninsu su yi fada wani lokacin har dambe suke, Amman Ammansu bata taba kuka ta zubar da hawaye ba akan haka ba sai yau.
[10/18, 5:34 PM] Nana 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲 1: https://chat.whatsapp.com/LimnMeG0kWvIfT6JQvVMh1
☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆
𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲
𝗣𝗮𝗴𝗲 3️⃣
“Amma I'm sorry laifin fa duk na Hamad ne shi ba a masa magana ya ji”
Amma ta dago da idanuwanta da suka kumbura ta kalleta.
“Ke ai kina ji? Kuma ke ce yayarsa ki daina biye masa mana, ki zauna lafiya da dan'uwanki dan Allah, kullum ina fada muku haka amman baku ji, Hurriya ki daina biye masa kina kallon ba sonku ake a gidan nan ba, a madadin ku so kanku kullum sai rigima da junanku”
Amma na magana Hurriya na yawo da idonta akan akwatunan da suke tsaye gefen kofar dakin da bata lura da su ba sai a yanzu.
“Amma kayan miye a akwaitinki?”
“Tafiya zan yi”
Hurriya ta dubeta da sauri tana kallonta da ya kumbura sosai.
“Amma ina zaki je?”
“Gida zan koma gurin Gwaggo”
“Saboda me?”
Amma ta yi murmushi hawaye na sauko mata.
“Hurriya abincina ya kare a gidan mahaifinku”
“Kamar Yaya? Toh ba sai ya kawo wani ba? Amma me ya faru kika yi kuka? Me yasa zaki tafi?”
Amma ta rufe ido ta dantse baki.
“Je ki kira Hamad”
Hurriya da bata gama fahimtar abun da yake faruwa ba idonta ya cika da hawaye har ya zubo ta kasan gilashin da shi ne rayuwarta. Ta mike tsaye ta fice daga dakin kamin ta isa dakin Hamad ta cire hijabin dake jikinta ta rike a hannu tana tafe tana hawaye har ta isa bakin kofar dakin. Murda kofar dakin ta yi ta tura ta shiga, Hamad dake sanye da short yana kokarin cire safar kafarsa ya kalleta.
“What? Amma ta miki fada ko? That's good next time sai ki sake shiga min hanci”
Ya fada azatonsa Amma ta yi mata fada ne sosai, daman haka take sometime idan aka yi mata fada kuka take.
“Ba saboda haka ba ne, Amma ta ce na kira ka kuma kuka take yi, ban san abun da aka yi mata ba”
Be tsaya ya karasa cire safar daya ba ya sauko da kafar ya biyo bayan Hurriya da tuni ta juya bayan ta isar masa da sakon Amma. Hamad na shiga dakin ya karasa inda take zaune ya zauna bakin gadon babu abun da zuciyarsa take nuna masa sai fadan da suka yi da Hurriya.
“Amma saboda Hurriya ne ko?”
Amma ta share hawayenta ta kalleshi, sannan ta kalli Hurriya ta mika mata hannu. Hurriya dake tsaye jikin kofar dakin ta karaso da sauri hawaye na sauko mata ta kasan gilashin dake idonta. Amma ta kama Hamad ta dauki hannu Hurriya ta dora a saman hannun na Hamad.
Sai a lokacin ta samu kuzarin bude bakin da yayi mata nauyi ta yi magana.
“Babu uwar da zata so wasu yayan kamar nata, kuma babu yayan da za su jidadin wata uwar kamar ta su, musamman a gida irinka”
“Kin fi kowa sanin yadda nake son ƴaƴana, da uwa ko babu uwa za su jidaɗin zama a gidan mahaifinsu, zan kula da su”
Ta haɗe wani abun da ya tsaya mata ta miƙe tsaye da tunani kala kala, ta bude takardar ta duba me ke ciki saki ne ko akasin haka? Idan sakin ne saki nawa ne? Ko kuma dai ta faɗi a ƙasa ta yi masa kuka ta roƙi ya maida ita bayan ya faɗa mata baya jin natsuwa da kwanciyar hankalin a zamansa da ita yanzu?
“Allah yasa hakan shi ne alheri, kuma ya baka ikon kula da su Hurriya da Hamad”
Ita kanta sautin murya mai kama da tata take jin tana fita a bakinta, domin bata da tabbacin tana da kuzarin furta masa wani abu a yanzu. Tana jan ƙofar ɗakin nasa ta ji ƙafafuwanta sun yi nauyi, mararta ta murɗa wani irin tashin hankalin da bata taɓa samun kanta a ciki ba ya baibayeta. Da gaske Appan Hurriya sakinta yayi? Anya zata iya tafiya ta bar ƴaƴanta? Ko dai wasa yake mata wata ƙila kuma wunin yau gaba ɗaya be faru ba. Tana tafiya jini na mata zuba amman bata sani ba zafin zaton sakin da bata tabbatar ba ya manta da ita zafin mararta dake murɗawa, ya hana hankalinta kusanto jikinta ya juya tunaninta a gurin abun da bata taɓa mafarkin faruwarsa ba.
Arzikinta ɗaya, ko wane part an yi masa corridor da zai sada ɓangaren da ɓangaren Alhaji Haruna ba sai ta gaban gidan ba. Kuma zaka iya fita ko shiga ba tareda sanin kowa ba, har sai idan mutum ya isa part ɗin. Kamar wadda ta sha giya haka ta isa ɓangarenta ta zarce bedroom ɗinta ta zauna a kan gadonta.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”
Ta furta daker tana kokarin dawowa hayyacinta.
“Haka ake ji? Haka saki yake? Ko dan ina da kurciya ne? Ko kuma saboda ban saka tsammanin zuwan sakin ba ne gaba daya a zaman rayuwata? Ko kuma saboda ina tsoron barin ƴaƴana ne? Allah ka sassauta min, ka saka min natsuwa da kwanciyar hankali, ka hallata aure ka hallata saki, Allah ka yaye min wannan damuwar da zata rufe ni, Ubangiji ka tsaya min”
Rahamar Allah ga bayinsa, da kuma dace ya ƴan amin a kusa, tana gama addu'ar ta ji natsuwa ta sauko mata, numfashin da take jin kamar zai danne mata kirji ya daga mata, mararta ta sake murdawa har sai da ta lumshe ido ta kai hannunta ta taba cikin dake jikinta na wata shida.
Kamar wadda aka yi ma allurar kuzari haka ta tashi ta aje takardun hannunta ta shiga bandaki ta gyara kanta ta fito ta gyara dakin inda ta ɓata ta cire Bedsheet din ta bar gadon a haka, ta dauki ruwa da tsumma ta bi tana goge jinin da bata san ya zuba ba sai a lokacin. Kamar mai shirin yin sata haka ta shiga ɓangaren ta goge jinin sannan ta juyo gabanta na tsananta faɗuwa ta fito daga ɓangaren. Ganin jinin yaƙi tsaya mata ya saka ta sake tsabtace jikinta ta saka pant da pad ta tare sannan ta kwanta saman gadon tana sauraren zuciyarta da ke bugawa da karfi, mararta kuma na cigaba da murdawa.
“Me na yi ma Appan Hurriya?”
Shi ne abun da take ta tambayar kanta, tambayar da bata da amsarta, mulmulawa ta yi saman gadon tana karewa katon dakinta kallo kamin ta tashi zaune ta fashe da kuka mai karfi, a rayuwarta bata taba fuskarta wani abu na tashin hankali irin yau ba. Cikin kuka da bakinciki ta dauko akwatunanta ta fara zuba kayanta ba tare da ta tsaya shiryasu ba, wani abun ma sai dai ta gwamatsa shi cikin wani talkaminta da atamfa ta saka su a kwati daya, sai da ta gama ta rufe ta kaisu gurin kofa ta aje ta dawo cikin dakin ta zauna kasa ta rasa me ya rage mata ta yi, kuma ta kasa fita daga dakin.
Misalin Karfe biyu da mintuna Bus dake dauko yaran makaranta ta shigo gidan, a harabar da aka tanada domin aje motoci direban ya faka motar. Sai da manyan suka fara fita sannan Hurriya ta fito, Hamad kan cikin manyan yayyunsu ya kutsa ya fita, daman shi yana daga cikin sarakunan kiriniya da rashin kunya na gidan, babu kalar dukan da basa masa ko hantara amman kowa yace masa kule zai ce chasss, Amma ta yi fada har ta gaji, Appa ma har baya son a kai masa kararsa domin ko ya masa fada ba zai hana gobe ya sake ba, Hamad irin yaran nan ne da ko kallonsu ka yi a karkace sai sun rama.
Hurriya na shiga part dinsu ta jefar da jakarta a kan kujera ta nufi bedroom din mahaifiyarta, a hankali ta tura kofar dakin ta shiga tsaye ta yi bakin kofar tana kallon kanenta Hamad dake ta fadawa Amma abun da ta yi masa a makaranta.
“Amma karya yake, karfe 1:30pm aka tashe mu shi ne na ce nasa yaje yayi sallah saboda bus din mu sai 2pm take zuwa ai, shi ne ya taso min fa masifa har zai yi dambe da ni gaban yan makaranta har da yan ajinsu fa”
Hamad ya juyo ya kalleta a fusace.
“Toh ina ruwanki da ni da zaki ce na tashi na yi sallah, kafiri ne ni ko bana sallah aka ce miki? Salon friends dina su fara tsokana ta suna cewa bana son sallah”
“Na ji ba zan sake maka magana ba, amman ni ma karka sake zuwa class dinmu ka ce na ara maka wani abu, ba ruwana da kai karka sake taba min komai kuma safata da ka saka yau ban yafe ba karka sake min taba min komai”
Amma ta mike tsaye tana kallonsu kowane zuciyarsa ta kawo kamar abokan gaba.
“Wannan fadan duk na minene wai? Ku kullum baku zaman lafiya? Kai kake binta amman kai da ita babu zaman lafiya, abinci ma ba zaku ci a plate daya ba, magana mai dadi babu tsakaninku kullum sai fada?”
Hamad ya ce.
“Ita ce bata ba ni respect ai”
“How? Kai ne babba or ni? Ni ce babba ai kai ya kamata ka ba ni respect”
“Ni ba zan taba baki respect ba i hate you kuma kika sake min wata maganar banza sai na ballaki”
Hamad na kaiwa nan ya juya ya fice rike da jakarsa har yana bankade Hurriya.
“Amma kin ga ko? Imagine”
Amma ta dafe kanta ta zauna bakin gadon tana fashewa da kuka.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”
A take jikin Hurriya yayi sanyi ta bar jikin kofar ta karasa inda Amma take ta zauna kusa da ita, domin suna yawan samun tsabani da Hamad saboda rashin jituwa dake tsakaninsu su yi fada wani lokacin har dambe suke, Amman Ammansu bata taba kuka ta zubar da hawaye ba akan haka ba sai yau.
[10/18, 5:34 PM] Nana 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲 1: https://chat.whatsapp.com/LimnMeG0kWvIfT6JQvVMh1
☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆
𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲
𝗣𝗮𝗴𝗲 3️⃣
“Amma I'm sorry laifin fa duk na Hamad ne shi ba a masa magana ya ji”
Amma ta dago da idanuwanta da suka kumbura ta kalleta.
“Ke ai kina ji? Kuma ke ce yayarsa ki daina biye masa mana, ki zauna lafiya da dan'uwanki dan Allah, kullum ina fada muku haka amman baku ji, Hurriya ki daina biye masa kina kallon ba sonku ake a gidan nan ba, a madadin ku so kanku kullum sai rigima da junanku”
Amma na magana Hurriya na yawo da idonta akan akwatunan da suke tsaye gefen kofar dakin da bata lura da su ba sai a yanzu.
“Amma kayan miye a akwaitinki?”
“Tafiya zan yi”
Hurriya ta dubeta da sauri tana kallonta da ya kumbura sosai.
“Amma ina zaki je?”
“Gida zan koma gurin Gwaggo”
“Saboda me?”
Amma ta yi murmushi hawaye na sauko mata.
“Hurriya abincina ya kare a gidan mahaifinku”
“Kamar Yaya? Toh ba sai ya kawo wani ba? Amma me ya faru kika yi kuka? Me yasa zaki tafi?”
Amma ta rufe ido ta dantse baki.
“Je ki kira Hamad”
Hurriya da bata gama fahimtar abun da yake faruwa ba idonta ya cika da hawaye har ya zubo ta kasan gilashin da shi ne rayuwarta. Ta mike tsaye ta fice daga dakin kamin ta isa dakin Hamad ta cire hijabin dake jikinta ta rike a hannu tana tafe tana hawaye har ta isa bakin kofar dakin. Murda kofar dakin ta yi ta tura ta shiga, Hamad dake sanye da short yana kokarin cire safar kafarsa ya kalleta.
“What? Amma ta miki fada ko? That's good next time sai ki sake shiga min hanci”
Ya fada azatonsa Amma ta yi mata fada ne sosai, daman haka take sometime idan aka yi mata fada kuka take.
“Ba saboda haka ba ne, Amma ta ce na kira ka kuma kuka take yi, ban san abun da aka yi mata ba”
Be tsaya ya karasa cire safar daya ba ya sauko da kafar ya biyo bayan Hurriya da tuni ta juya bayan ta isar masa da sakon Amma. Hamad na shiga dakin ya karasa inda take zaune ya zauna bakin gadon babu abun da zuciyarsa take nuna masa sai fadan da suka yi da Hurriya.
“Amma saboda Hurriya ne ko?”
Amma ta share hawayenta ta kalleshi, sannan ta kalli Hurriya ta mika mata hannu. Hurriya dake tsaye jikin kofar dakin ta karaso da sauri hawaye na sauko mata ta kasan gilashin dake idonta. Amma ta kama Hamad ta dauki hannu Hurriya ta dora a saman hannun na Hamad.