← Book details Huriyya Part 1 And 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 81 OF 163

Sashe 81

Huriyya Part 1 And 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Fararen curtains din ya saki ya saka hannunsa aljihu ya pistol ya bude jakar dake ka yi gado ya sakata a ciki, sannan ya dauki jakar System din da takardun ya saka talkamin Musib da suke dakin ya nufi kofar fita ya bude ya fito yaja kofar a hankali. One after the other ya rika bin dakunan da suke gefen dakin da Namra take yana budewa har ya ci karo da wanda yake kyautata zaton an Hurriya ne, tsaye yayi yana kallon dakin kamar mai nadar bayanai sannan ya ja kofar ya rufe ba tare da bari ta yi kara ba. Downstairs ya sauko ya zauna a sofa ya ja wani karamin tebur gabansa ya bude system dinsa ya aje a kai, takardunsa da wayarsa kuma ya da wallet dinsa da pistol ya dora sama gefen kujerar da yake zaune.

“Ranka ya dade kana bukatar wani abu?”

Inna Shatu ta tambaya tana mikewa tsaye.

“Aa na gode”

Ya amsa ba tare da ya kalleta ba.

“Toh”

Ta nufi kitchen domin ba zata iya fita cikin ruwa ba balle ta tafi gurin da suke zama, kuma ta san Momy tana hana su zama a falonta idan tana ciki ko bakinta suna nan. System din ya bude ya fara tabawa, yana tsaka da typing kofar falon da yi kara alamar da mutum a waje. Inna Shatu ta fito daga kitchen da saurin da nufin zata tafi ta bude.

“Lemme Handel it bari na bude”

“Tou”

Ta juya ta koma. Dauke hannunsa yayi daga typing din ya mike tsaye ya nufi kofar ya bude. He thought Hurriya zai gani domin ita ya san da shigowarta gidan, sai kuma yayi arba da Momy da Namra rike da umbrella suna mamakin ganinsa.

“Captain kai ne kuma?”

“Eh na zo baku nan ai”

Ya matsa jikin kofar suka shigo.

“Ka dade a nan?”

“Aa ban jima ba, Momy sannu da zuwa”

“Yauwa, ya aikin?”

“Alhamdulillah shi na zo na yi a nan ai”

“Captain sannu”

“Sannu Namra”

“Bari naje na canja”

“Okay”

Ya amsa mata ta siga biyu amfani da kai, da kuma furtawa. Momy ma ta bi bayanta tana fadin.

“Ai da na san zaka zo ba zan fita ba ma, gashi nan ruwa duk ya jika mu”

“Be kamata ai ka ki fita saboda ni ba”

“Babu wani abun da ya fi uwa ta saka danta a gaban ta yi ta kallo, da ka san irin dadin da nake ji idan ka zo gidan nan wata kila da kullum sai ka zo”

Murmushi kawai yayi ya bi su da kallo har suka haye stairs din. A madadin ya rufe kofar falon ya samu kansa ta takawa ya fita tare da janyo kofar ya rufe daga waje, balcony ya tsaya yana kallon yadda ni'imar Allah ke sauka ko'ina a gidan tana jika gidan. Dan matsawa yayi kadan yana takawa a hankali har ya isa gurin da ruwan yake zuba ya tara jikinsa ya saka hannunsa aljihu ya lumshe ido yana maida numfashi a hankali, sanyin ruwan saman dake sauka a kansa suna ratsa zuciyarsa da ilahirin jikinsa, da abun ya masa dadi sai ya daga kansa sama daga tsayen da yake ruwan na sauka a fuskarsa and the thing is so funny kana jin ruwa na sauka a fuskarka kamar an watsa maka wani abu. Haka ya jike kansa shakaf da ruwan saman hannayensa biyu duka cikin zube cikin aljihu daga ipod din dake kunnesa da wristwatch da wallet dinsa babu abun da be jike ba, shi ma ba wai ya shirya hakan ba ne, zuciyarsa ce ta ingiza shi har ya samun kansa da bukatar aikata abun da ya ga wata ta yi. Is he a teenager like her ya tambayi kansa kamin ya juyo ya kalli Namra dake masa magana...

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar  MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne  cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai  shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
26
“Ruwa duk ya jika ka fa”

Ya kalli jikinsa ya daga fadunsa.

“Na tuna baya ne”

Ya fita daga cikin ruwan ya karaso bakin kofar ruwan na siyaya a jikinsa. T-shirt din dake jikinsa na bayyana yadda Allah ya zuba hallita a jikinsa saboda jikewar da rigar ta yi da ruwan sama.

“Rayuwar baya kuma Captain? Ko dai akwai abun da yake damunka? Baka saba irin haka? Zuwa ka yi aiki a gidan nan, ga kuma tsaya a ruwan sama kamar wani karamin yaro kalli fa har wristwatch dinka ya jike”

Ya kalli agogon.

“Kudi ne nan ba zallar agogo ba, ruwa baya masa illa, lemme go and change set the table please ban ci abincin rana ba”

Yana fadar hakan ya nufo gurin da take tsaye sai ta masa ta ba shi hanya tana binsa da kallo gabanta na bugawa da mugun karfi, har sai da ta sauke ajiyar zuciya mai nauyi sannan ta samu sa'ida. Hakika Jameel ya kai namiji ya cika ta ko'ina irin cikar da ake so a jikin kowane jarumin namiji, Allah ya hada masa abubuwa da yawa ya bashi kyauta ba tare da ya roka ba. Da kallo ta bishi har ya haye sama sannan ta dauke idonta ta nufi dinning domin duba abun da babu. Abu na farko da ya fara yi bayan shiga dakin shi ne canja tufafinsa ya saka wadanda ke karamar jakarsa. Ya saka kai wadanda ya cire a toilet sannan ya bude kofar na saka kafarsa waje Hurriya ta juyo da sauri tare da ihu domin bata san da mutum a dakin na Miwan ba, ya janyo kofar a hankali ya rufe yana kallonta ko'ina na jikinta siyayarda ruwa yake.

“Aljani kika gani?”

Ta girgiza kai.

“Karki sake min ihu”

Ta daga mishi kai tana kallonsa ido kamar za su fado.

“Daina kallona”

Ta yi saurin sauke idonta kasa, ta juya ta bude kofar dakinta da sauri ta shige ciki ta rufe. Murmushinsa mai tsada yayi sannan ya taka ya fara sauka stairs din da sassarfa.

“Tafiya zan dafa maka, saboda na san baka cin tuwo, ni san na manta ma tuwo aka yi yau Wallahi”

Namra ta fada tun kamin ya karaso dinning din. And she's right baya son tuwo baya cin tuwo ko da yunwa zata kashe shi ba ya iya cin tuwo. Ya dafa kujerar yana kallonta

“Ina yarinyar nan kanwarki?”

Ta dan motsa ido gafe da gafe.

“Hurriya?”

“Yea kira ta ta girka min”

“I can cook for you”

“You don't have to stress yourself Pretty, kira ta girka”

The way he said kar ta yi stressed kanta ya saka ta ji she's special kuma hakan ya nuna har a gurinsa tana da muhimmanci.

“Okay”

Ta amsa da murmushi sannan ta nufi hanyar stairs, shi kuma ya nufi gurin da ya zauna dazun ya zauna. Ya cigaba da aikin da yake, Namra bata dauki lokaci ba ta sauko.

“Sallah take amman na fada mata zata sauko idam ta gama”

Ya amsa mata da kai hankalinsa da natsuwarsa gaba daya yana gurin aikin da yake a yanzu. Momy ce ta sauko tana sanye da bakar abaya tana murmushi.

“Captain aiki ake take yi”

“Aiki nake Momy akwai abun da ya kamata na yi typing na aika Abuja kamin gobe”

Ita ma dai ya amsa mata ba tare da dago kai ba.

“Amman ka ci abinci?”

“Za a dafa min yanzu”

Momy ta kalli Namra dake tsaye.

“Namra tafi ki sama masa wani abun yanzu mana, kin san fa baya son tuwo”

“Na ce zan yi yace kar na yi stressing kaina Hurriya zata dafa?”

“Hurriya kuma? Bata gidan ma fa”

“Ta dawo tana ciki, dazun ai Inna Shatu ta gama gage gurin data bata da ruwa saboda ta jika tufafinta”

“Okay to kin fada mata”

“Eh”

“Bari na shiga ciki har ka gama aikin Captain”

“Okay Momy”

Still be dago ba, Momy ta juya ta koma ciki, Namra kuma ta zauna kusa da shi tana duba wasu daga cikin takardun da yake aikin. Captain be dago ba har sai da ya ji karar talkamin Hurriya tana saukowa daga stairs din, yadda sautin takun tafiyar ke fita ya fahimci ita ce, kamar an saka hannu biyu an rika fuskarsa da karfi an juyar da ita zuwa stairs din haka ya ji. Ba kwalliya ta yi ba amman green atamfar dake jikinta ta karbe ta sosai ta yi mata kyau, Brown hullar dake kanta ma ta fito da ita, ga dan gilashinta dake kara mata kyau a kullum. Ba tarbiyar ta bace yi ma wanda ya girmeta magana a tsaye ba, musamman ma ace mutumen a zaune yake dan haka ta risina a gabansa.

“Gani”

“Me yasa baki yi sallah da wuri ba sai yanzu? Baki san babu kyau sallah a makare ba?”

“Mun fita ne tare da Yaya Khairy kuma na yi bachi a can ban san an yi sallah ba”

“Da kika dawo kuma kika tsaya wasa da ruwa, wuce ki dafa min taliya”
Chapter 81 · 0% Book details