← Book details Huriyya Part 1 And 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 133 OF 163

Sashe 133

Huriyya Part 1 And 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ya karasa a zuciyarsa domin bakinsa ya masa nauyi kirjinsa ya kau yaji, kansa yayi nauyi har ya rasa abun da zai fara tunani. Ya aje wayar a tebur ya zauna yayi shiru na wasu mintuna yana kallon wani gurin kamin ya soke kai kasa yana sauke ajiyar zuciyar da ta ki sauka a zuciyarsa. Tunanin yake ta ina ya gaza a matsayinsa na uba, ta ina ya kyautata ta ina ne be kyautata ba? Me ya kawo haka a cikin familynsa ga yaran da suka shi ya haife su? Ya kai hannu ya dauki wayarsa ya shiga contact dinsa ya nemo number da ya kwashe shekaru be ji daga gareta ya kira. Sai da jiran ya yanke ya sake yin wani shi ma ya yanke a uku aka daga.

“Assalamu Alaikum”

Appa baya iya amsa sallama a yanzu dan haka be amsa ba, maganar ma kamar wanda aka dannewa numfashi haka yake yinta.

“Zan aiko da mota yanzu, za a dauki Hurriya taje asibiti ta duba mijinta ba shi da lafiya”

“Wane irin magana ne wannan? Tun da ace mana an daura auren nan yau kwana biyu mutunen be zo ya ganta ba, fari ne ba ki ne mu ba mu san kamaninsa ba, sai kuma yanzu ka ce zata je ta duba shi?”

Ya daga yatsansa yana nunawa kamar ance masa tana gabansa a zaune.

“Dan Allah Iyami karki musa min, karki kara min bakinciki da bacin da nake ciki a yanzu, baki san halin da nake ciki ba matukar ba so kuke na fadi na mutu ku huta... ”

Jin wannan kalamin ya saka Amma bata sake cewa komai ba har Appa ya kashe wayar, Direbansa dake gida ya kira ya fada masa yaje ua dauki Hurriya ya kaita asibitin, sannan ya dayan direbansa ya fada masa ya kunna mota za su tafi gida yanzu nan. Yasir ne last mutumen da ya kira ya fada masa ya same shi gida yanzu nan, sannan ya mike tsaye cike da nauyin zuciya irin na uban da yake jin kamar ya gaza ta wani bangaren ya fice daga office din.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

47
Amma ta kalli Gwaggo mamakin bayyane a fuskarta.

“Alhaji ne, wai zai aiko da direba a dauki Hurriya ya kaita asibiti ta duba mijinta”

Gwaggo ma mamakin ne fal a ranta.

“Ba shi da lafiya ne?”

“Da alama kam, amman Gwaggo ta ya zata tafi duba shi mutunen da be taba zuwa gidan nan ba tun da aka daura musu aure ni ban san shi ba shi ma be san ni ba?”

“Ko dai shi ma baya son auren ne? Ko kuma marar lafiya ne aka aura mata?”

“Shi nake tunani Gwaggo, kar abun yayi ma Hurriya yawa, na ji mahaifinta ma kamar a cikin damuwa”

“Allah dai ya kyauta, wannan abun da daure kai yake”

“Kuma kin ga Kaltume da Nafisa ba za su so Hurriya da alheri ba, za su iya zugawa mahaifinta ya aura mata kowa saboda ta sha wahalar rayuwa”

“Amman a yanzu ina ganin kamar Alhaji ya fara dawowa hayyacinsa ai, Allah dai kadai ya san me yake nan”

Amma ta fada tana aje kofin maganin dake hannunta sannan ta yunkura ta tashi tsaye cikin rashin kuzari irin na wanda be gama warkewa daga ciwo ba ta taka ta fita daga dakinta. Dakin Rukkayya ta nufa domin a can Hurriya take rayuwa a yanzu, lalulen dakin Amma ta fara yayewa sannan ta shiga dakin, Hurriya na jin yanayin tafiyar ta Amma da bata gama kwarewa ba ta tashi zaune idanuwanta cike da duhu tana kallon saitin kofar. Amma ta zauna kusa da ita tana kallonta.

“Hurriya ina son ki ba ni aron hankalinki”

Hurriya ta juya ta gefen da take jin muryar Amma ta mika mata dukan natsuwarta.

“Ba dan kina yata ba, hakika ke yarinya ce mai hakuri da sanin ya kamata, kuma kin hadu da kalubalen rayuwa da kananan shekaru daman haka tsarin rayuwa yake, wani da dadi wani babu, eani kuma na sirka masa, dan haka ina son ki kara hakuri akan wanda kike da shi kuma ki karbi kaddara a duk yadda ta zo miki, a matsayi na uwa zan yi ina nawa kokarin na ga baki cutu ba a rayuwar gidan aurenki, sai dai kuma idan na hango wata matsala ko wahala da zaki sha zan tare ko da bani da karfi haka zan ta yaki har Allah ya mu nasara”

“Na gode Amma”

“Allah ya miki albarka, Hurriya kin san mutumen da mahaifinki ya aura miki? Kin taba ganinsa ko da sau daya?”

Ta yi shiru na wasu dakiku kamin ta daga kai.

“Na san shi”

“Marar lafiya ne? Ko yana da wata nakasa ko aibu?”

“Ba shi da shi ko daya Amma, a lokacin da nake gidan idan Momy ta hanani abinci shi yake kawo min wani abu na ci, ko lokacin da Namra ta shake ni shi ya mareta yana da kirki, amman yana da saurin fushi da zuciya kamar Hamad”

Amma ta ji sanyi a ranta jin kadan daga hallaya da siffar mijin da yarta ta aura. Zuciyarta kuma sai ta karkata akan furucin Hurriya cewar Namra ra makureta.

“Me kika yi ma Namra ta makureki?”

Hurriya ta bata labarin abun da ya faru, Amma ta girgiaza kai, ta sani daman jininta ba zai sha da dadin a gidan Momy ko Hajiya Kaltume ba. Ajiyar zuciya ta sauke

“Appanki ya kira yanzu, yace direba zai zo ya dauke ki ya kai ki asibiti ki duba mijinki wai ba shi da lafiya, ki shirya Rukkayya zata rakaki”

“Toh Amma”

Amma ta tashi ta fice daga dakin, Hurriya ta kai hannu tana tana awarwaron da Captain ya saka mata a hannu da sunan wani abokinsa ya bata, tana jin kamar babu dadin jin cewar ba shi da lafiya, ko dai baya son auren ne dole aka masa? Ko kuma wani abu ya faru? Kwantawa ta yi kan tana tunani kala kala a ranta, zuciyarta na raya mata taya mutum kamar Captain zai yarda ya aureta bayan duk abun da ake cewa ta yi? Kuma gashi bata gani a yanzu, wata kila dai dole aka yi masa, amman kuma yadda Momy take jinsa anya zata masa dole? Bayan Namra ta mata gargadi akansa Momy ma ta yi mata. Sai da direban ya shigo sannan Rukayya ta shigo dakin ta saka Hijab dinta ta sakawa Hurriya ta kama hannunta suka fita Amma na Allah ya tsare, Gwaggo kuma na fada mata idan ta shiga ta gaishe da kowa.

CAPTAIN POV.

Idanuwan da ya rufe ne ya sake budewa sakamakon bude kofar dakin da aka yi, Salim ya sake dawowa hannunsa rike da leda ya nufi gurin da aka tana da ya aje ledar sannan ya kalli Captain.

“Sannu Allah ya baka lafiya, ga apple nan na san kana son Apple na siyo a waje ne, anjima zan dawo Allah ya kara afuwa”

Sannan ya kalli Ammy dake zaune.

“Ammy zan tafi sai anjima zan dawo Allah ya ba shi lafiya”

“Amin Salim an gode”

Har ya fice Captain be ce masa komai ba.

“Abun da kake yi wani lokacin baka kyautawa Captain, na san kana da fushi amman danne zuciya ake, ko sai anjima baka cewa yaron nan ba, ba dan kana da aboki kamar Salim ba da yanzu ba ku shirya ba, amman yana mutunkata yana sonka, duk abun da kake masa baya dubawa yana nan tare da kai, duk da yana karkashinka yana baka girma da kulawa na abokantaka ba na aiki ba”

Nan ma be ce komai ba, Ammy zata sake wata maganar wayarta ta yi ringing sai ta mike tsaye ta fice daga dakin. Captain ya sauke ajiyar zuciya ya ya dan dago kadan, ya sake bude wayarsa ya kunna video ya sake kallo.

“Ina fatan hakan ya saka ki farinciki Hurriya, and Sister nan da ta aikata miki wannan abun i hope bakincikin da zata shiga zai ninka wanda ta saka ki”

Ya fita daga whatsapp din ya shiga contact dinsa ya kira Nafi'u. After sun gaisa ya gabatar masa da bukatarsa.

“Asiri na tuno na abun da ya faru da yarinyar nan so zan turo maka video yanzu ina son ka yadashi iya yadda zaka iya, ya karade ko'ina a kafofin sada zumunta Please”

“Za'ayi haka ranka ya dade ka aiko da video”

“Okay, ba zan baka komai ba a yanzu dai na ga yanayin aikinka, idan ka cancanci da yawa zan baka”

“Zaka gani Sir”
Chapter 133 · 0% Book details