← Book details Huriyya Part 1 And 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 57 OF 163

Sashe 57

Huriyya Part 1 And 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲

𝐏𝐚𝐠𝐞 1️⃣5️⃣

“Sam Sam Sam ni hukuncin da Alhaji yayi a gidan nan be yi min ba”

Cewar Hajiya Kaltume da shigowarta falonta kenan. Khairi ta yi karaf ta ce.

“Ba ke kadai ba Hajiya, ni Wallahi na dauka ma korar Hurriya zai yi, domin zata iya satar kudin nan”

Hajiya Kaltume ta zauna tana fadin.

“Ai ba nata ne ya ban mamaki ba, na Nafisa ne, yadda ta ci mutunci na ta dora min sata ban ji ba ban gani ba, amman ace Alhaji ya kyaleta ba tare da yi mata wani hukunci ba? Ni wane irin rashin godiyar Allah ne zai saka ni sata a bangarenta, ni ban ma san ta fita bangaren ba, amman da yake ta raina ni haka ta laka min sata, saboda bata da ta ido har da wani aiko masu aiki wai su zo duba mata bangarena, haka fa matar ta taba dora min laifin fasa tayar bakinta, ta maida ni kamar wata karamar yarinya”

“Wallahi Hajiya abun da Momy take yi a gidan yana wuce gona da iri, da zarar an taba ta sai tace ita mai kudi ce, mu gaba daya ganinmu take kamar wasu awaki ita kadai ce mutum”

Hajiya ta kara kashe ido domin laka mata sata da Momy ta yi da kuma kyalewar da Appa yayi be yi komai ba ya fi komai bakanta mata rai.

“To wai waye zan tura ya shiga ya dauki kudin a bangarenta, idan ma ba wanda yake bangaren ba waye zai san gurin da take aje kudinta, da sarka har a dauka, ko dai masu aikinta ko kuma ita wannan mai siffar macizan ce”

“Ni fa zuciyata ta fi yarda ma ita ce, amman kin ga yadda ta wani sha jinin jikinta sai kuka take ita munafuka, har Appa ya tausaya mata, wannan yarinyar da film take da ta kwashi kudi dominbta iya acting”

“Bar shi ai sai na masa magana akan haka, dan yau yaushe za a shaideshi ne, har da wani cewa wai duk abun da yake mata ba sonta ne ba shi ba, kin ji min wata maganar banza”

Sai da Khairi ta kalli kofa domin tabbatar da babu wanda zai shigo sannan ta kalli Hajiya Kaltume ta ce.

“Ya Yasir ma da wani ne sai yayi masa dukan mutuwa kamin ma a gane gaskiya, amman kin ga da yake Hurriya ce uffan be ce ba, balle har ta kai ga ya doketa, ai Wallahi Salma ta huta da tafi yin masters dinta a waje, Maama kuma ta yi aure babu mai shan wahakarsa sai ni, daman ni ya tsaneni a gidan nan”

Hajiya Kaltume ta daga mata hannu.

“Ni yanzu ba ta Yasir nake ba, maganar nan ba zan bari ta wuce ba, ba a dora min sata da kurciyata ba yanzu da yayana ba za a dora min sata na kyale ba, kuma Wallahi sai na bawa Nafisa mamaki sai na maidata abar tausayi”

Khairy ta dan kalli wayarta da sakwannin ke appearing saman screen din wayarta, ta dan bata fuska kadan da alamar damuwa sannan ta fara taba wayar tana reply kaminnta mike tsaye ta nufi dakinta. Hajiya Kaltume kamar tashinta take jira sai ta tashi ita ma ya nufi nata dakin ta dauki wayarta ta kira aminiyarta da bata iya boyewa komai, sai dai ga mamakinta sai da wayar ta yanke har sau biyu ana uku Hajiya Fatee ta amsa cikin wata murya dake bayyana damuwarta.

“Toh sawun giwa ya take na rakumi aka ce na kira na fada miki damuwata kuma na jiki a cikin wata damuwar lafiya Hajiya Fatee”

“Ina lafiya anje gyaran kai an kare wuya, Hajiya Kaltume ina nan cikin matsalar cikin nan, jiya da shekaranjiya ko bachi ban iya yi ba, na rasa madafa”

“Subhanallahi, baki sake kiran Malam ba? Ba na ce ki kira shi ba?”

“Na...”

Har zata yi subutar baki ta fada ma Hajiya Kaltume yadda suka yi da Malam sai kuma ta tuna gargadin da yayi mata.

“Toh zan kira shi, ni tsoron kiransa nake kar ya fada min wani abun da zai daga hankali na, domin na lura kamar akwai matsala”

“Aa ki kwantar da hankalinki Hajiya Fatee, kuma ki nuna masa damuwarki, kuma ki bi duk wani abu da zai fada miki, na san ba zai wuce kudi ba, ko kuma ya ce sai kin siya mishi wani abu, komai dai minene karki yarda cikin nan ya bayyana Hajiya Fatee domin bayyanar cikin nan matsala ce da ko mun mutu sai mun bar abun fada, duk tsanani karki yarda sirrinki ya bayyana”

Shiru Hajiya Fatee ta yi na dan lokaci kamin ta amsa.

“Toh Hajiya Kaltume, abun kunya ne kam sosai amman kuma idan ya fada min wani abun da ba zan iya yi ba fa?”

“Kamar ya? Haba ta wajena karki karyar da zuciyarki mana karki yarda ta fada miki akasin abin da na fada miki, yo Allah na tuna ko cewa yayi sai kin bashi kanki ko kin bashi jini ko rabin dukiyarki ai kya aikata saboda rufin asirinmu”

Hajiya Fatee ta yi murmushin takaici mai sauti.

“Hajiya Kaltume ni yanzu me nake da shi? Wannan bakar matar da Fadeel ya auro ai duk ta ga bayan komai nawa, duk wani boko ko malami da kika sani a garin nan babu wanda be ci kudina ba, saboda wannan bakar yarinyar kuma kudi ba kadan suke karba ba, amman babu biyan bukata ni na rasa gane wani irin abu ne wannan, shiyasa na fara yakin yanzu da bakina”

“Waya san da me ta mallake miki da, ai wasu yayan dangin maguzawa ne Hajiya Fatee, kuma su ma fa Malam nan sun iya tsibbo sosai, suka yi ma wasu ma balle yaransu, zata iya yiyu mahaifinta ne ya tsaya mata, kuma yayi mata wani abun da za a lalata duk wani shiri nake”

“Toh yanzu idan magani be yi ba, zan yi yaki da halshena, shiyasa na fada masa ya zaba ko dai kara aure ko sakinta ko kuma na yafe shi har abada kuma Wallahi zan iya saboda kura ta kai bango ba da ita da Iyami su suka ja mana shiga wahala, kara ma Iyami tana san tana amsar nata hukuncin amman ita wannan sai kara samun gurin zama take”

“Toh amman Hajiya wannan hukuncin be yi tsauri ba? Kina ganin zai iya aikata daya daga ciki? Matar nan fa ba karamar mallaka ta yi masa ba”

“Dole ya zama ba, kuma zan fada masa Khairi nake son ya aura domin ita kadai zata share min hawaye na”

Hajiya Kaltume ta yi murmushin jindadi.

“Da yardar Allah kuwa, daman duk cikin yayana babu mai halina irin Khairi ta fisu fahimtar duniya ta san ciwon kanta sosai”

“Na lura da haka ai, sai dai kuma ki ja mata kunne ta jajirce gurin jan hankalinsa sosai saboda ta dauke hankalinsa daga gurin wacan tun kamin ma ta shiga”

“Haka za'ayi, Allah dai ya hada kansu ya ba mu nasarar wannan aikin jihadi da zamu yi”

“Ameen”

Daga haka suka yi sallama kowacce ta sauke waya da tunani na dabam, musamman ma Hajiya Kaltume da take jin idan har Khairi ta auri Fadeel ta yi sa'a domin namiji ne mai kyau ga hankali ga kudi ga iya kula da gidansa, musamman ma idan aka kure matarsa yaransa kuma a maida su hannun uwarsu ko Hajiya Fatee gida ya zama na yarta ita kadai.

“Matukar kika auri Fadeel Khairi kin yi dace, amman na lura ke ma kamar kina son raba min hankali biyu toh ba zan dauka ba”

Magana take da kanta, ta sake daukar wayarta ta kira Malaminta ta fada masa abun da ya faru har tana zargin ko aikinsu ya fara karyewa ne, sai ya bukaci ta bashi minti goma zai sake kiranta, after ten minutes ya kira yana fada mata abun da ya faru.

“Daman na san ba zai karye ba, ai ba karamin aiki na yi ba, haba Hajiya duk bayan sakamakon da kika min ga kudi ga Makka da kika kai ni, sai kuma na bari ki ji kunya? Sam ai ba zan yarda ba, kawai dai abun yana dan fisgo masa ne, kin san fa ya fi son yarinyar nan fiye da sauran yayansa domin na duba na ga haka a zuciyarsa musamnan ma yanzu da abubuwan nan suke faruwa, kawai dai mun danne son ne a zuciyarsa ba zai iya nunawa, kuma muka kawo tsana muka saka a tsakaninsu”

Hajiya Kaltume ta ji dadi sosai.

“Haka nake son ji, amman Malam ta bangaren Nafisa fa Malam, matar nan ta zame min karfen kafa, na rasa ya zan yi da ita, amman maganar gaskiya tana jefani a damuwa sosai, ka duba ka gani kirikiri an mata sata amman sai ni ta dorawa, kai ba dan gidan nan ba ne ai sai na yi kararta”

“Karki damu, ita ma zamu maida hankali a gurinta, kuma zamu zafafa na Alhaji ta yadda ba zai iya yanke shawarar komai ba, sai dake, kuma zan saka masa tsananin tsoronki sannan mu cire Nafisar a zuciyarsa kamar yadda muka cire iyami”

“Haka nake so Malam, anjima kadan zaka ji sako mai nauyi”

Ya amsa da dariya.

“To Maa Shaa Allahu, sai dai kuma ina son na fada miki ki maida hankali gurin Hurriya, domin yanzu haka da na duba matsalalolin gidan na duba na duba na kasa ganin komai ta bangarenta”

“Kamar ya Malam?”
Chapter 57 · 0% Book details