Sashe 17
Huriyya Part 1 And 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A haka sai da Hajiya ta kara sati daya a hannun mutanen nan ita da Hajiya Fatee domin police aka saka a lamarin su kuma suka hana a aika da kudin, suka ce za a gano inda take, sai da Appa ya ga abun na su ba mai yi ba, ga hankalin yaransa da yan'uwan Hajiya Kaltume ya tashi ya nemi sassauci suka rage kadan ga miliyan dari, a sake neman sauki, daker da addu'a da sudin goshi aka samu suka sauko a miliyan goma, bangare Hajiya Fatee ma haka suka karba, Appa ya hada kudinaka rasa wanda zai kai, sai da wani kanen Hajiya Kaltume yayi jihadi yace shi zai tafi kai musu kudin, ranar da zai tafi suka fadi inda zai tsaya a dajin su zo su tafi da shi, haka kuwa aka yi Fadeel ya kawo nasa kudin aka hada da na Appa suka shiga mota aka kaishi har inda suka bukata suka fito suna masa addu'a, su kawo wajen gari suka tsaya. Ba zan wani jima ba suka kira suka ce aje a dauke ta a wata gona dake nan dogon dutse a nan za su aje su. Abun ka da mai nema Yasir da Fadeel da Uncle din Fadeel din suka nufi gurin da moto suna gudu kamar ba za su je su same su a gurin ba. Kamin su isa kowannensu hankalinsa ya tashi kuma zuciyarsa ta cika da zullumi, domin suna tsoron kar su je su tararda gawarta domin sun saba haka wani lokacin sai su ce aje a dauka sai an tafi a tararda mutum a mace.
A bakin titi suka faka motar suka fita suka shiga cikin gonar domin dubawa, Yasir da waya a kunne yana fadawa Appa sun isa gurin Appa kuwa sai gargadi yake masa.
“Yasir ku kula da kyau, zai iya yiyuwa dabara suka muku saboda idan kun shiga gurin su sace ku”
“Aka yi mana Addu'a Appa In Shaa Allah babu abun da zai faru, fatanmu dai a samu Hajiya da rai”
Yana rufe baki ya ji muryar Fadeel yana fadin ya karaso nan gasu a nan, da sauri Yasir ya katse wayar ya nufi gurin, Hajiya Fatee ce da Hajiya Kaltume daure jikin itace, kansu babu ko dankwali sai wani zane atamfa kala daya da suka yafa kamar wasu yan kauye sun yi yaushi kai kace allayahun da yayi sati ne a daure, fuska ta yi burun-burun kana ganin kasan an dade ba a sadu da ruwa ba, baki ya bushe idanuwa sun kode kamar wadanda suka kusa kusantar rame. Hajiya na ganin Yasir ta fashe da kuka, Hajiya Fatee kuma ta fara zubar da hawaye.
“Alhamdulillah Alhamdulillah”
Shi ne abun da sukr ta fada bayan sun kwance su.
“Ku yi sauri muje kar su biyo sawunmu, Sannu Hajiya”
Fadeel ya fada yana kallon mahaifiyarsa cike da tausayawa.
“Bana iya tafiya Fadeel bana iya komai”
Tana maganar tana nishi hawaye na mata zuba, Hajiya Kaltume kam kuka take riri domin da yanzu da aka sako su da kuma lokacin da aka kama su duk yayi mata kamar mafarki, ita kadai ta an bakar azabar da suka sha. Duk yadda Yasir ya so su yi sauri hakan be samu ba saboda Hajiyoyin duk basa iya sauri tafiyar ma sai daker gashi jikin ba kadan ba balle yayansu su ce za su taimaka musu, a haka dai suka isa gurin motar, Hajiya Fatee ita ce mai tafiya kamar mai tatata, Hajiya Kaltume ce mai dan kuzari shi ma ba wani da yawa ba sai na karfin hali. Hankalin kowa be kwanta ba sai da suka isa gida, domin kin amincewa suka yi da maganar Appa da kuma na yaransu cewar a tafi da su asibiti a duba lafiyarsu, Hajiya fatee ce ta fara nuna karfiya sannan Hajiya Kaltume ta rufa mata baya. Daga gidansu Yasir Fadeel ya dauki mahaifiyarsa ya fice da ita zuwa family house dinsu bayan ta yi wanka, sai dai ta kasa saka komai a baki duk kuwa da irin lallabata da Fadeel yake. Be isa gida ba Yasir ya kira wayarsa yana fada masa wai sun kira sun ce shi ma wanda aka aika yana da mai da alama za a samu wani abu dan haka sun rike shi sai an bada miliyan 20.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, mutanen nan ba su da imani ko kadan, kai yaushe aka gama wannan kuma ace sun kama wani? Wai anya ana son mu cigaba da rayuwa a kasar nan kuwa? Wannan wane irin bala'i ne?”
Haka yayi ta fada, Hajiya fatee tsabar tsoro ji take kamar ta rufe masa baki, domin ta ga tashin hankali da bata taba mafarki ba.
“Ka rufawa kanka asiri da zagin mutanen nan, ba au da imani ko kadan, su hanyar da imani ya bi ma ba su santa ba”
Fadeel ya juyo ya kalleta a daidai lokacin da ya faka motarsa a harabar gidan, yan'uwa da abokan arziki suka fito da gudu suka yo gurin motar domin taron Hajiya Fatee ciki har da Afrah da Hajiya Fatee take zagi wato matar Fadeel da kuma yaranta masu aure.
“Wallahi Hajiya Kaltume ce taja min, ita na raka a kauyen”
“Toh me kuka je yi kauyen?”
Bata samu amsa masa ba sakamakon bude gambun motar da aka yi ana murna da zuwanta, daman kuma tana neman dalili da zai hanata yi masa wani bayani dan bata shirya tonawa kawarta asiri ba. Ta bangaren Hajiya Kaltume after ta samu ganawa da mutane ta huta zuwa dare danta Yasir ya dauketa zuwa asibiti kamar yadda mijinta ya umarta. Sun dubata suka mata duk wani gwaje gwajen da ya dace sannan suka bata maganin zafi domin kafarta na ciwo sosai saboda tafiya, sai kuma na ciwon jiki da ciwon kai da na ido saboda kukan da suka sha har kammaninta sun sauya.
BAYAN KWANA BIYU....
Hajiya Kaltume ce zaune kan kujera Maama na matsa mata kafafuwan da har yanzu ba su daina mata zafi ba, domin bata taba gwada yin tafiyar da ta yi daga inda yan fashin dajin suka kamata ba zuwa sansaninsu, ko a lokacin da take da kurciya balle yanzu da girma ya fara kamata. Momy ce ta yi sallama ta shigo falon tana sanye da wada tsadadiyar shadda yar mali sai sheki take kamar an watsa mata ruwa, kana kallon shaddar ka san ranar ta fara sakata, wuyanta na cike da sarkar zinarin da ba ko wace matar mai kudi ce zata iya sakawa ba, gamshin da take ma na dabam ne domin Momy bata yarda ta siye turaren irin wanda Hajiya Kaltume ko Iyami za su iya siye ba ko da kuwa kudin da take da shi zai kare. Idan kana neman dake ji da kansu asalin ji da kai da nuna isa idan ka yi arba da Momy ka kai karshen aya. Maama ce ta amsa mata sallamar tana hada baki da Khairi dake fitowa daga kitchen rike da bowl din kankana. Hajiya Kaltume tun da ta kalli kofar falon ta ga Momy ce bata sake sha'awar kallon gurin ba. Tsaye Momy ta yi kusa da kujerar da Hajiya Kaltume take zaune abun ka da matan da tsibbo ya waya kuma suka wayance shi sai Hajiya Kaltume ta zame kafafuwanta daga hannun Maama ta matsa daga inda Momy take tsaye, jiki be bata banza ta kawo Momy bangaren ba, tunani take wani abun ta zo yi mata.
“Kaltume ashe an dawo”
Momy ta fada cikin izza tana Kiranta da Kaltume kai tsaye kamar yadda ta saba, tun zuwanta gidan taba taba kiranta da Hajiya ba balle kuma Yaya kamar yadda wasu matan suke yi idan za su kira uwargida ko da kuwa da sunan yaranta ne.
“Eh Allah ya nufa Nafisa”
Hajiya Kaltume ta amsa kamar an mata dole tana wani kashe ido. Momy ta tabe baki kamar wadda ta manta a falon Hajiya Kaltume take idan ma Hajiya bata ganinta kuma yaranta suna kallonta, amman tsabar raina uwarsu da ta yi da kuma rashin tsoron anyi an ce ya saka ta yin haka.
“Toh Allah kyauta gaba”
Maama da Khairi ne suka sam da Ameen, sukan tsoronta ya dade da cika musu ciki ba kamar mahaifiyarsu da take jin zata iya karawa da ita ba. Momy ta juya ta fara takawa kamar wanda bata son tafiya, haka yanayin ya ke tun tashi, sai dai lamarin ya samu promotion ne a lokacin da ta auri Alhaji Haruna Mai Yadi, saboda ta nunawa Hajiya Kaltume da Iyami ita yar sarauta ce kuma yar masu kudi ba Kamarsu.
“Mtsssss”
Hajiya Kaltume taja guntun tsaki tana bin bayanta da harara.
“Wallahi matar nan ta raina min hankali, wato na fahimci so ta yi na mutu gaba daya idan ba haka ba ace ma samu na kubuto hannun azzaluman mutanen nan da ba su san Allah ba, amman bata shigo ta min barka da dawowa sai yau da aka kwana biyu?”
Khairi ta mika mata bowl din watermelon din tare da fadar
“Hmmm Hajiya ai da baki dawi ba sai matar nan ta zuba ruwa kasa ta sha”
“Ai ni bayan Iyami bana da makiyiya irin Nafisa, kuma ita ma sai ta bar gidan nan da yardar Allah, komai sai ya dawo karkashin ikona sai na bata mamaki, ai Wallahi da ban dawo ba da sai Iyami ta ci ubanta dan sai ta gane kuskurenta, duk saboda ita na sha wannan bakar wahalar, duk dalilinta ne da bata aurar min miji ba da yanzu ban san wadannan yanta'adda da ba su da imani ba, yanzu na fito ga kanen can a daure”
“Hajiya ba su da Imani ko?”
Maama ta tambaya.
A bakin titi suka faka motar suka fita suka shiga cikin gonar domin dubawa, Yasir da waya a kunne yana fadawa Appa sun isa gurin Appa kuwa sai gargadi yake masa.
“Yasir ku kula da kyau, zai iya yiyuwa dabara suka muku saboda idan kun shiga gurin su sace ku”
“Aka yi mana Addu'a Appa In Shaa Allah babu abun da zai faru, fatanmu dai a samu Hajiya da rai”
Yana rufe baki ya ji muryar Fadeel yana fadin ya karaso nan gasu a nan, da sauri Yasir ya katse wayar ya nufi gurin, Hajiya Fatee ce da Hajiya Kaltume daure jikin itace, kansu babu ko dankwali sai wani zane atamfa kala daya da suka yafa kamar wasu yan kauye sun yi yaushi kai kace allayahun da yayi sati ne a daure, fuska ta yi burun-burun kana ganin kasan an dade ba a sadu da ruwa ba, baki ya bushe idanuwa sun kode kamar wadanda suka kusa kusantar rame. Hajiya na ganin Yasir ta fashe da kuka, Hajiya Fatee kuma ta fara zubar da hawaye.
“Alhamdulillah Alhamdulillah”
Shi ne abun da sukr ta fada bayan sun kwance su.
“Ku yi sauri muje kar su biyo sawunmu, Sannu Hajiya”
Fadeel ya fada yana kallon mahaifiyarsa cike da tausayawa.
“Bana iya tafiya Fadeel bana iya komai”
Tana maganar tana nishi hawaye na mata zuba, Hajiya Kaltume kam kuka take riri domin da yanzu da aka sako su da kuma lokacin da aka kama su duk yayi mata kamar mafarki, ita kadai ta an bakar azabar da suka sha. Duk yadda Yasir ya so su yi sauri hakan be samu ba saboda Hajiyoyin duk basa iya sauri tafiyar ma sai daker gashi jikin ba kadan ba balle yayansu su ce za su taimaka musu, a haka dai suka isa gurin motar, Hajiya Fatee ita ce mai tafiya kamar mai tatata, Hajiya Kaltume ce mai dan kuzari shi ma ba wani da yawa ba sai na karfin hali. Hankalin kowa be kwanta ba sai da suka isa gida, domin kin amincewa suka yi da maganar Appa da kuma na yaransu cewar a tafi da su asibiti a duba lafiyarsu, Hajiya fatee ce ta fara nuna karfiya sannan Hajiya Kaltume ta rufa mata baya. Daga gidansu Yasir Fadeel ya dauki mahaifiyarsa ya fice da ita zuwa family house dinsu bayan ta yi wanka, sai dai ta kasa saka komai a baki duk kuwa da irin lallabata da Fadeel yake. Be isa gida ba Yasir ya kira wayarsa yana fada masa wai sun kira sun ce shi ma wanda aka aika yana da mai da alama za a samu wani abu dan haka sun rike shi sai an bada miliyan 20.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, mutanen nan ba su da imani ko kadan, kai yaushe aka gama wannan kuma ace sun kama wani? Wai anya ana son mu cigaba da rayuwa a kasar nan kuwa? Wannan wane irin bala'i ne?”
Haka yayi ta fada, Hajiya fatee tsabar tsoro ji take kamar ta rufe masa baki, domin ta ga tashin hankali da bata taba mafarki ba.
“Ka rufawa kanka asiri da zagin mutanen nan, ba au da imani ko kadan, su hanyar da imani ya bi ma ba su santa ba”
Fadeel ya juyo ya kalleta a daidai lokacin da ya faka motarsa a harabar gidan, yan'uwa da abokan arziki suka fito da gudu suka yo gurin motar domin taron Hajiya Fatee ciki har da Afrah da Hajiya Fatee take zagi wato matar Fadeel da kuma yaranta masu aure.
“Wallahi Hajiya Kaltume ce taja min, ita na raka a kauyen”
“Toh me kuka je yi kauyen?”
Bata samu amsa masa ba sakamakon bude gambun motar da aka yi ana murna da zuwanta, daman kuma tana neman dalili da zai hanata yi masa wani bayani dan bata shirya tonawa kawarta asiri ba. Ta bangaren Hajiya Kaltume after ta samu ganawa da mutane ta huta zuwa dare danta Yasir ya dauketa zuwa asibiti kamar yadda mijinta ya umarta. Sun dubata suka mata duk wani gwaje gwajen da ya dace sannan suka bata maganin zafi domin kafarta na ciwo sosai saboda tafiya, sai kuma na ciwon jiki da ciwon kai da na ido saboda kukan da suka sha har kammaninta sun sauya.
BAYAN KWANA BIYU....
Hajiya Kaltume ce zaune kan kujera Maama na matsa mata kafafuwan da har yanzu ba su daina mata zafi ba, domin bata taba gwada yin tafiyar da ta yi daga inda yan fashin dajin suka kamata ba zuwa sansaninsu, ko a lokacin da take da kurciya balle yanzu da girma ya fara kamata. Momy ce ta yi sallama ta shigo falon tana sanye da wada tsadadiyar shadda yar mali sai sheki take kamar an watsa mata ruwa, kana kallon shaddar ka san ranar ta fara sakata, wuyanta na cike da sarkar zinarin da ba ko wace matar mai kudi ce zata iya sakawa ba, gamshin da take ma na dabam ne domin Momy bata yarda ta siye turaren irin wanda Hajiya Kaltume ko Iyami za su iya siye ba ko da kuwa kudin da take da shi zai kare. Idan kana neman dake ji da kansu asalin ji da kai da nuna isa idan ka yi arba da Momy ka kai karshen aya. Maama ce ta amsa mata sallamar tana hada baki da Khairi dake fitowa daga kitchen rike da bowl din kankana. Hajiya Kaltume tun da ta kalli kofar falon ta ga Momy ce bata sake sha'awar kallon gurin ba. Tsaye Momy ta yi kusa da kujerar da Hajiya Kaltume take zaune abun ka da matan da tsibbo ya waya kuma suka wayance shi sai Hajiya Kaltume ta zame kafafuwanta daga hannun Maama ta matsa daga inda Momy take tsaye, jiki be bata banza ta kawo Momy bangaren ba, tunani take wani abun ta zo yi mata.
“Kaltume ashe an dawo”
Momy ta fada cikin izza tana Kiranta da Kaltume kai tsaye kamar yadda ta saba, tun zuwanta gidan taba taba kiranta da Hajiya ba balle kuma Yaya kamar yadda wasu matan suke yi idan za su kira uwargida ko da kuwa da sunan yaranta ne.
“Eh Allah ya nufa Nafisa”
Hajiya Kaltume ta amsa kamar an mata dole tana wani kashe ido. Momy ta tabe baki kamar wadda ta manta a falon Hajiya Kaltume take idan ma Hajiya bata ganinta kuma yaranta suna kallonta, amman tsabar raina uwarsu da ta yi da kuma rashin tsoron anyi an ce ya saka ta yin haka.
“Toh Allah kyauta gaba”
Maama da Khairi ne suka sam da Ameen, sukan tsoronta ya dade da cika musu ciki ba kamar mahaifiyarsu da take jin zata iya karawa da ita ba. Momy ta juya ta fara takawa kamar wanda bata son tafiya, haka yanayin ya ke tun tashi, sai dai lamarin ya samu promotion ne a lokacin da ta auri Alhaji Haruna Mai Yadi, saboda ta nunawa Hajiya Kaltume da Iyami ita yar sarauta ce kuma yar masu kudi ba Kamarsu.
“Mtsssss”
Hajiya Kaltume taja guntun tsaki tana bin bayanta da harara.
“Wallahi matar nan ta raina min hankali, wato na fahimci so ta yi na mutu gaba daya idan ba haka ba ace ma samu na kubuto hannun azzaluman mutanen nan da ba su san Allah ba, amman bata shigo ta min barka da dawowa sai yau da aka kwana biyu?”
Khairi ta mika mata bowl din watermelon din tare da fadar
“Hmmm Hajiya ai da baki dawi ba sai matar nan ta zuba ruwa kasa ta sha”
“Ai ni bayan Iyami bana da makiyiya irin Nafisa, kuma ita ma sai ta bar gidan nan da yardar Allah, komai sai ya dawo karkashin ikona sai na bata mamaki, ai Wallahi da ban dawo ba da sai Iyami ta ci ubanta dan sai ta gane kuskurenta, duk saboda ita na sha wannan bakar wahalar, duk dalilinta ne da bata aurar min miji ba da yanzu ban san wadannan yanta'adda da ba su da imani ba, yanzu na fito ga kanen can a daure”
“Hajiya ba su da Imani ko?”
Maama ta tambaya.