Sashe 33
Huriyya Part 1 And 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨
𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲
Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660
𝐏𝐚𝐠𝐞 3️⃣
Tun a ranar Bappa ya so ya samu Appa su tattauna kan lamarin amman hakan be samu ba sakamakon dare da yayi, daman daf da magariba Maama taje gidan. The following the day Bappa yayi ta kiran Appa a waya amman yaki dagawa, cikin yanayin damuwa Bappa ya kalli Iyami dake rike da carbi ya ce.
“Haka nake da bawan Allah nan, babu ranar da zan kira shi ya amsa min, tun da lamarin nan ya faru idan na kira shi baya daga wayata”
“Wata kila har yanzu yana jin kunyarka ne, ina ganin abun da zai fi ka shirya ka same shi gida da safen nan da wuri sai ka yi magana da shi”
“Ko kuma ita Iyamin ta kira shi a wayarta ba, ta yi magana da shi ko kuma ta ba ni wayar mu yi magana”
Ya karasa yana kallon Amma. Amma ta dauki wayarta ta lalabo number Appa da rabon ta yi waya da shi tun tana gidan, kamin ta danna masa kira ma sai da ta yi da gaske ta danne zuciyarta, sanin cewar saboda matsalar Hamad zata kira shi ya karfafa mata guiwar kiran, sai ita ma ta yi rashin sa'a kamar Bappa, be daga kiran ba, tun kiran na ringing har ta kai an fara rejecting.
“To wai lafiya ko kuma dai yana tsoron kar a fada miki ne, wata kila be san Maama ta zo gidan nan ba, ina tunanin a boye ta zo ta fada miki, domin irin wannan magana mai nauyi shi ya kamata ya taho da kansa ya fada miki, anya ba Hajiya Kaltume ta taro ta ba?”
A take Bappa ya gwatsale Gwaggo daman shi be cika yarda da irin abubuwan nan na zafin kishi ba, ko wani abun da za ace kishiya ta aikata ganin yake duk karya ne, ko wane bangaren daman ba zai so dayan bangaren ba dan haka kazafi da kage babu kalar wanda ba zai yi ma abokin adawarsa ba.
“Ku dai kullum baku da wata magana sai ta Hajiya Kaltume, ina ce saboda Hajiya Kaltume nan Iyami ta hadu da Alhaji, ni fa a gurina bani da kamar Hajiya Kaltume domin sanadinta Iyami ta auri Alhaji Haruna Mai Yadi, idan na fita har nuna ni ake ga surukin Alhaji, da can ba a kwano muke zaune ba? Amman ya zo ya siya mana babban gida ga kuma lalurar komai ya dauke mana, duk sanadin waye ba Hajiya Kaltume me? Dan Allah ku daina kawo min maganarta ma”
Gwaggo ta rausayar da kai.
“Toh Malam ai daman ba zaka yarda ba, baka san makircin mata ba”
“Ban sani ba, kuma bana son sani, yanzu ki tashi ki shirya mu tafi tare can mu same shi mu yi magana da shi”
“Toh bari na dafawa Hurriya Indome ta fi son karyawa da ita”
Amma dai bata ce komai ba, har suka ci suka shude, ita dai tunaninta na halin da danta yake ciki ne. Sai da Gwaggo ta dafawa jikarta Indomie ta zuba mata a karamar cooler sannan ta yi wanka Bappa ma yayi wanka suka shirya sannan suka bar gidan.
MAI YADI'S HOUSE.
Hajiya Kaltume ta dan leki wayar da Appa ya aje a gefe daya ta kalleshi.
“Iyami ce fa Alhaji?”
Appa kamar wanda aka rikita sai ya fara fada ta inda yake shiga ba nan yake fita ba.
“To me zan mata? Ba za a bar mutum da damuwarsa ba? Ta san halin da nake ciki ne? Mahaifinta yanzu ya gama kirana ita kuma ta dora da nata”
A kaikace Hajiya Kaltume ta ce.
“Ka sani ko zancen dawowarta za su maka ko kuma na Hamad?”
“Dawowarta? Ta zo ta yi me? Hamad kuma ai ni ma dana ne ba ita kadai ta haife shi ba balle ta nuna min sonsa”
“Gaskiya kam, ni ma da aka dauke min Ruma ai dole na zuba ido sai abun da ka yi, amman duk da haka dai Alhaji da dai ka bada kudin”
Appa yayi shiru kamar mai tsoron musa mata, ya kasa cewa komai.
“Kuma ba ka san shakkuwarta ba, da ka karba wayar ka ji abun da za su fada”
“Bana son na ji wani abun da da ya shafi Iyami ko gidansu a yanzu, damuwa ta min yawa kaina ma kamar ya fashe nake ji, na san kuma damu za su yi da maganar Hamad”
“Ikon Allah yau Alhaji Iyamin ce baka son jin wani abun da ya shafe ta? Toh Allah ya kyauta bari na kwashe kayan”
Ta fara kwashe kayan da ya ci abinci zuciyarta na wani irin zillo kamar zata fado tsabar farinciki. Jikinta har rawa yake kamin ta bar part din, tana shiga bangarenta ta aje tray a falo ta shige dakinta ta dauki wayarta sai kira ta aikawa Hajiya Fatee.
“Toh Allah dai ya sa lafiya wannan kira haka tun da safe?”
“Lafiya kalau sai alheri, Hajiya Fatee yau bana da inda zan saka ki, bani da wanda ya fi min ke a duniyar nan, Hajiya Fatee kin biyani Allah dai ya bar zumuncinmu”
Cikin mamaki da farinciki kawar tata ta amsa.
“Toh Ameen, amman ba ni an sha me ya samu?”
“Komai ma ya samu Hajiya Fatee yanzu zan fara samun kan mijina, abun da na kwashe shekaru ina nema ban samu ba, Hajiya Fatee yau Alhaji da kansa yake ta fada saboda Iyami da mahaifinta sun kira shi a waya, har yake fadar shi yanzu baya son wani abun da ya shafi iyami ya hada shi da ita”
Hajiya Fatee ta saka dariya irin mai ruguzawar nan.
“Hajiya Kaltume ni kaina na gasgata aikin Malamin nan, kuma na yarda ba da wasa yake aikinsa ba, domin ni na fi kowa shaidar hakan tun da ga ciki ya kwanta lafiya kamar babu shi, wata kila ma cireshi yayi gaba daya, amman har asibiti na tafi an auna babu ciki babu labarinsa”
“Ni Wallahi da farko nan na dauka ko aikin be yi ma, kwana nawa aka dauka amman shiru sai yau na fara ganin ikon Allah”
“Ai daman wani abun haka yake, kin manta yadda muka yi na auren Iyami? Shi ma ai sai da kika fara korafin be yi be yi ba, har ya ce kin yi gajin hakuri, yanzu ba gashi ta tafi ta bar miki idan ba”
“Na yarda, tabbas ni kuwa zan saka masa da sakamako mai kyau, sai yayi alfahari da ni”
“Ni ma ai na fada masa idan yayi abun da zai raba auren Fadeel da Afrah sai na masa kyauta mai tsoka da sai ya kasa mantawa da ni, kuma ya ce zai yi, sai dai ta inda lamarin ya sanyaya min guiwa cewar da yayi idan yayi mata aika dawo masa ake da ita”
Hajiya Kaltume ta rike baki. “Ai kin san bata tsawaya kanta ba, ita ma shigen shigen take”
“Ai na sani, shiyasa ta mallake min da komai sai Afrah gaba daya baya jin maganar kowa sai nata, kuma bana da ikon zaginta a gabansa sai ya fara masifa, ni daman tun farko bana son aurenta da yaron nan Wallahi, Allah dai ya riga da kaddara ne kawai”
“Ki sa ido ki yi kallo kamar yadda Iyami ta bar gidana, Afrah ma sai ta bar gidan danki da yardar Allah”
“Haka nake fata Hajiya Allah ya amsa”
“Ameen”
Hajiya Kaltume ta aje wayar tana murmushi kamar wadda aka yi ma bushara.
“Hmmmm Iyami.... Lallai kin zama labari a gidan nan, yaranki ma da yardar Allah sai sun zama su da babu duk daya a gidan nan”
Ta nufi bakin gadonta ta zauna tana kokarin sake yin wani kiran Khairi ta shigo dakin ta zauna kusa da ita ta kwanta jikinta.
“Hajiya yaushe Ruma zata dawo ne?”
Hajiya ta yi saurin saka wayar key tare da gefenta.
“Babu jimawa Khairi, mahaifinki ne yace a bashi lokaci zai nemi ragi, kuma kin ga ai ana neman ragi a komai”
“Toh Hajiya da zai yarda da sai ya bada kudin ya karbo Ruma, albashi Hamad din a barsa sai an shirya daman ya fitini kowa a gidan nan”
“Ai kin san ba zai yarda ba, kuma mutane ma sai su saka mana ido, ace saboda uwarsa bata gidan ne, kara dai a karbo su tare gaba daya”
“Allah sarki Ruma, Allah dai ya tsare ta”
“Ya ma tsare In Shaa Allah ba za su mata komai ba, ai yarinya ce kuma kin ga ba ita kadai suka dauka ba ko dan ganin idon Hamad za su raga mata tun da dan'uwanta ne”
“Allah yasa”
“Ameen tashi kuje ku karya, ni wanka zan yi yanzu”
“Na karya ai”
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨
𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲
Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660
𝐏𝐚𝐠𝐞 3️⃣
Tun a ranar Bappa ya so ya samu Appa su tattauna kan lamarin amman hakan be samu ba sakamakon dare da yayi, daman daf da magariba Maama taje gidan. The following the day Bappa yayi ta kiran Appa a waya amman yaki dagawa, cikin yanayin damuwa Bappa ya kalli Iyami dake rike da carbi ya ce.
“Haka nake da bawan Allah nan, babu ranar da zan kira shi ya amsa min, tun da lamarin nan ya faru idan na kira shi baya daga wayata”
“Wata kila har yanzu yana jin kunyarka ne, ina ganin abun da zai fi ka shirya ka same shi gida da safen nan da wuri sai ka yi magana da shi”
“Ko kuma ita Iyamin ta kira shi a wayarta ba, ta yi magana da shi ko kuma ta ba ni wayar mu yi magana”
Ya karasa yana kallon Amma. Amma ta dauki wayarta ta lalabo number Appa da rabon ta yi waya da shi tun tana gidan, kamin ta danna masa kira ma sai da ta yi da gaske ta danne zuciyarta, sanin cewar saboda matsalar Hamad zata kira shi ya karfafa mata guiwar kiran, sai ita ma ta yi rashin sa'a kamar Bappa, be daga kiran ba, tun kiran na ringing har ta kai an fara rejecting.
“To wai lafiya ko kuma dai yana tsoron kar a fada miki ne, wata kila be san Maama ta zo gidan nan ba, ina tunanin a boye ta zo ta fada miki, domin irin wannan magana mai nauyi shi ya kamata ya taho da kansa ya fada miki, anya ba Hajiya Kaltume ta taro ta ba?”
A take Bappa ya gwatsale Gwaggo daman shi be cika yarda da irin abubuwan nan na zafin kishi ba, ko wani abun da za ace kishiya ta aikata ganin yake duk karya ne, ko wane bangaren daman ba zai so dayan bangaren ba dan haka kazafi da kage babu kalar wanda ba zai yi ma abokin adawarsa ba.
“Ku dai kullum baku da wata magana sai ta Hajiya Kaltume, ina ce saboda Hajiya Kaltume nan Iyami ta hadu da Alhaji, ni fa a gurina bani da kamar Hajiya Kaltume domin sanadinta Iyami ta auri Alhaji Haruna Mai Yadi, idan na fita har nuna ni ake ga surukin Alhaji, da can ba a kwano muke zaune ba? Amman ya zo ya siya mana babban gida ga kuma lalurar komai ya dauke mana, duk sanadin waye ba Hajiya Kaltume me? Dan Allah ku daina kawo min maganarta ma”
Gwaggo ta rausayar da kai.
“Toh Malam ai daman ba zaka yarda ba, baka san makircin mata ba”
“Ban sani ba, kuma bana son sani, yanzu ki tashi ki shirya mu tafi tare can mu same shi mu yi magana da shi”
“Toh bari na dafawa Hurriya Indome ta fi son karyawa da ita”
Amma dai bata ce komai ba, har suka ci suka shude, ita dai tunaninta na halin da danta yake ciki ne. Sai da Gwaggo ta dafawa jikarta Indomie ta zuba mata a karamar cooler sannan ta yi wanka Bappa ma yayi wanka suka shirya sannan suka bar gidan.
MAI YADI'S HOUSE.
Hajiya Kaltume ta dan leki wayar da Appa ya aje a gefe daya ta kalleshi.
“Iyami ce fa Alhaji?”
Appa kamar wanda aka rikita sai ya fara fada ta inda yake shiga ba nan yake fita ba.
“To me zan mata? Ba za a bar mutum da damuwarsa ba? Ta san halin da nake ciki ne? Mahaifinta yanzu ya gama kirana ita kuma ta dora da nata”
A kaikace Hajiya Kaltume ta ce.
“Ka sani ko zancen dawowarta za su maka ko kuma na Hamad?”
“Dawowarta? Ta zo ta yi me? Hamad kuma ai ni ma dana ne ba ita kadai ta haife shi ba balle ta nuna min sonsa”
“Gaskiya kam, ni ma da aka dauke min Ruma ai dole na zuba ido sai abun da ka yi, amman duk da haka dai Alhaji da dai ka bada kudin”
Appa yayi shiru kamar mai tsoron musa mata, ya kasa cewa komai.
“Kuma ba ka san shakkuwarta ba, da ka karba wayar ka ji abun da za su fada”
“Bana son na ji wani abun da da ya shafi Iyami ko gidansu a yanzu, damuwa ta min yawa kaina ma kamar ya fashe nake ji, na san kuma damu za su yi da maganar Hamad”
“Ikon Allah yau Alhaji Iyamin ce baka son jin wani abun da ya shafe ta? Toh Allah ya kyauta bari na kwashe kayan”
Ta fara kwashe kayan da ya ci abinci zuciyarta na wani irin zillo kamar zata fado tsabar farinciki. Jikinta har rawa yake kamin ta bar part din, tana shiga bangarenta ta aje tray a falo ta shige dakinta ta dauki wayarta sai kira ta aikawa Hajiya Fatee.
“Toh Allah dai ya sa lafiya wannan kira haka tun da safe?”
“Lafiya kalau sai alheri, Hajiya Fatee yau bana da inda zan saka ki, bani da wanda ya fi min ke a duniyar nan, Hajiya Fatee kin biyani Allah dai ya bar zumuncinmu”
Cikin mamaki da farinciki kawar tata ta amsa.
“Toh Ameen, amman ba ni an sha me ya samu?”
“Komai ma ya samu Hajiya Fatee yanzu zan fara samun kan mijina, abun da na kwashe shekaru ina nema ban samu ba, Hajiya Fatee yau Alhaji da kansa yake ta fada saboda Iyami da mahaifinta sun kira shi a waya, har yake fadar shi yanzu baya son wani abun da ya shafi iyami ya hada shi da ita”
Hajiya Fatee ta saka dariya irin mai ruguzawar nan.
“Hajiya Kaltume ni kaina na gasgata aikin Malamin nan, kuma na yarda ba da wasa yake aikinsa ba, domin ni na fi kowa shaidar hakan tun da ga ciki ya kwanta lafiya kamar babu shi, wata kila ma cireshi yayi gaba daya, amman har asibiti na tafi an auna babu ciki babu labarinsa”
“Ni Wallahi da farko nan na dauka ko aikin be yi ma, kwana nawa aka dauka amman shiru sai yau na fara ganin ikon Allah”
“Ai daman wani abun haka yake, kin manta yadda muka yi na auren Iyami? Shi ma ai sai da kika fara korafin be yi be yi ba, har ya ce kin yi gajin hakuri, yanzu ba gashi ta tafi ta bar miki idan ba”
“Na yarda, tabbas ni kuwa zan saka masa da sakamako mai kyau, sai yayi alfahari da ni”
“Ni ma ai na fada masa idan yayi abun da zai raba auren Fadeel da Afrah sai na masa kyauta mai tsoka da sai ya kasa mantawa da ni, kuma ya ce zai yi, sai dai ta inda lamarin ya sanyaya min guiwa cewar da yayi idan yayi mata aika dawo masa ake da ita”
Hajiya Kaltume ta rike baki. “Ai kin san bata tsawaya kanta ba, ita ma shigen shigen take”
“Ai na sani, shiyasa ta mallake min da komai sai Afrah gaba daya baya jin maganar kowa sai nata, kuma bana da ikon zaginta a gabansa sai ya fara masifa, ni daman tun farko bana son aurenta da yaron nan Wallahi, Allah dai ya riga da kaddara ne kawai”
“Ki sa ido ki yi kallo kamar yadda Iyami ta bar gidana, Afrah ma sai ta bar gidan danki da yardar Allah”
“Haka nake fata Hajiya Allah ya amsa”
“Ameen”
Hajiya Kaltume ta aje wayar tana murmushi kamar wadda aka yi ma bushara.
“Hmmmm Iyami.... Lallai kin zama labari a gidan nan, yaranki ma da yardar Allah sai sun zama su da babu duk daya a gidan nan”
Ta nufi bakin gadonta ta zauna tana kokarin sake yin wani kiran Khairi ta shigo dakin ta zauna kusa da ita ta kwanta jikinta.
“Hajiya yaushe Ruma zata dawo ne?”
Hajiya ta yi saurin saka wayar key tare da gefenta.
“Babu jimawa Khairi, mahaifinki ne yace a bashi lokaci zai nemi ragi, kuma kin ga ai ana neman ragi a komai”
“Toh Hajiya da zai yarda da sai ya bada kudin ya karbo Ruma, albashi Hamad din a barsa sai an shirya daman ya fitini kowa a gidan nan”
“Ai kin san ba zai yarda ba, kuma mutane ma sai su saka mana ido, ace saboda uwarsa bata gidan ne, kara dai a karbo su tare gaba daya”
“Allah sarki Ruma, Allah dai ya tsare ta”
“Ya ma tsare In Shaa Allah ba za su mata komai ba, ai yarinya ce kuma kin ga ba ita kadai suka dauka ba ko dan ganin idon Hamad za su raga mata tun da dan'uwanta ne”
“Allah yasa”
“Ameen tashi kuje ku karya, ni wanka zan yi yanzu”
“Na karya ai”