← Book details AmatulMaleek Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 89 OF 96

Sashe 89

AmatulMaleek Complete Hausa Novel · about 8 min read

Numfashi ya fara saukewa Yana fara zayyano mata abinda yake faruwa na auren maamah din da mum Aisha harma da Husnah dakuma auren Husnah din Daya dawo kansa ya Dora da tambayarta raayinta akan aurensa da Husnah Yana kallanta.

Shiru tayi cikin mamaki me girma da fargaban auren maamah din Dan kuwa abun yayi Wani iri Amma tana magana maamah zata ga laifinta musamman yanzu datake cike da fushi da ita akan cikin.

Maganar aurensa da Husnah kuwa rasa abin fada Tayi Dan kaman yanda Abdul din ya fada ko ita bazata taba So Husnah taje gidan nasu aure ba Dan kuwa mutuwa kwata kwata rayuwarta zatai Dan haka batajin zata Hana Abdul aurenta sbd kubutar da ita duk da abubuwan Dake tsakaninsu wannan Wani lamarin ne daban.

Ajiyan zuciya ya sauke da amincewan Amatun Dan kuwa bazaiso ya auri Husnah batareda yar uwar tasa na kaunar alaqar ba har cikin rantaba.

Shiru sukai kafin ta kallesa tana ajiye cup din hannunta ta tambayesa Haydar murya a sanyaye.

Bayaninsa yayi mata akan fushin da yayi Amma dai zai sauko sbd duk Basu kyauta masa ba zasuyita basa hakuri harya hakura din.

Maganar maamah ya fara yiwa Amatun itama Yana mata nata nasihar akan maamah uwa ce baa fushi da mahaifi komai zeyi maka Dan haka ta tabbatarda tayi magana da mamaah ta Bata hakuri duk da batada laifi.

Shiru tayi sbd Bata taba fushi da mahaifiyarta ba hasalima tsoro ne yake Sakata yin nesa da ita sbd kada ta shiga tashin hankali ta Saka maamah din cikin Bacin Rai.
##MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

78
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI'IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

*************
Karfe goma Abdulhameed yabar gidan ya koma bayan sun jima suna magana sosai tsakaninsa da Amatun.

Mum Aisha har guduwa daga mansion din taso yi Amma Sam securities sun Hana kowa fita Dan haka dole ta dawo da motarta tayi parking ta dawo cikin kaman mahaukaciya Dan kuwa tin kayan jiya ne a jikinta gashi Naufal Se kiransa takeyi wayarsa kashe sbd har lokacin gidan Yola din baa mayar da wuta ba daqyar yake zuwa ya samo caji a gun masu caji da kekensa ta qafa Daya.

ASH ko breakfast ya kasa yi a cikin gidan sbd rashin dawowan su little Abeeda har lokacin Dan haka ya fahimci gidan Farha ta wuce kenan Bata dawo Nan din ba.

Numfashi ya sake me dumi Yana Dan Jin sanyin jiki na shigarsa ya daure ya kame ya shirya ya fito qarfe goma da Rabi lokacin Kuma Abdulhameed ya dawo gidan yayi parking mota ya fito kenan Mr Jameel Shima ya shigo harabar gidan yayi parking tasa motar ya dauko tsadaddun shaddodi da yadikan manya masu tsada ready made kusan duka size din Abdulhameed din ya wuce dasu ya miqawa Abdul din ya wuce gurin ASH Dake jiransa.

Abdul su kawu ne suka kirasa da kansu suka isar masa da sakon ASH din na yau din duka zaa daura auren harda nasa Dan haka Saiya shirya zama magidanci Kuma wlh ya riqe yar mutane da kyau tinda Shima gashinan tasa yar uwar ta samu guri har uban yar masu gida akeci akanta.

Shiru kawai Abdul yayi sbd Bai dauka tinda ya amince ba zaace zaa daura auren yanzu ba.

Fitowa yayi yaje ya sanar da maamah wadda itama zataso Daman a daura auren Husnah ta samu me kulawa da ita yanda ya kamata tinda su dole yanzu zasu bar Nan din.

Albarka ta sakawa auren tana danne damuwarta da halin datake ciki ita tareda fada masa ya riqe yar mutane da kyau da kulawa.

Mum Aisha na ganin lokaci ya sake matsowa ta fito a rikice ta koma gurin ASH ta ringa kuka tana rokonsa Amma Sam baima Kalli inda takeba Saida su kawu suka shigo kallo daya tayiwa dukkaninsu batareda ma tasan waye nata angon a cikinsu ba ta fasa kukan baqin ciki sbd ganin su dukan kaman baqin aljanu kowannensu karnin shaddarsa kawai zai iya sumar da ita,ita datake shafa turaren da kudinsa zai ciyar da kaf gidan Sanda Fulde din na tsawon kwanaki koma satittika Amma ace aure zatai da wainnan fataken.
Ficewa tai tana Jin Hawan jininta na tashi da baqin cikin ganinsu kawai.

Tana ficewa kawu ashiru ya bita da Satan kallo Dan shi gaba Daya Sonta ma qara shigarsa yakeyi,
'dan nata ma da ake fada shi taje dashi agolanci zai amshesa ya hada da nasa manyan yayan ya riqe.

Husnah na daki ta rasa meyake mata dadi,ta rasa wa zata kira wa zata kama gashi Haydar yace tayi zamanta daki karya fito sai komai ya kammala sunga abinda ya faru tukuna.

Maamah ma tana dakinta zaune yanzu tinanin Amatu ne Kuma yake rufeta gashi dai ma zata koma kauye tabar Amatu anan karshe abinda taita tashin hankali Akai tana ji tana Gani Amatu zata cika gidan da yayan ASH batada ta cewa,
Amma Kuma har lokacin mamakin samun cikin Amatun Bai Dena jijjigata ba,
Tayaya ASH ya iya kebewa da Amatun har cikin ya samu?
Suna cikin gida Daya yarta tayi ciki harya bayyana Bata saniba,
Kunyar kanta da damuwa me nauyi ce ta sake danne zuciyarta gashi yanzu kiri Kiri tana kallo zata tafi tabarta zaman auren da Basu shirya ba.

Karfe goma sha Daya da mintina aka fara daura auren Abdulhameed Sanda Fulde da Husnah Ashraf Talba akan sadaki Naira dubu dari biyu Wanda Abdulhameed dinne ya biya abinsa da kansa mutane qalilan ne suka sheda a masallacin gidan nasa,
sai Kuma na maamah da kawu bello akan sadakinsa da Shima shine ya biya abinsa dubu Tara.
Na mum Aisha da kawu ashiru shine na qarshe da aka daura akan sadakinsa Shima Daya biya dubu Tara Dan dubu goma goma aka yanka musu sadakin.

Mum Aisha ko da aka gama daurin auren ciwonta ya tashi gaba Daya na hawan jini dole aka kwasheta zuwa asibiti,
Maamah kuwa kukan datasha kaman qaramar yarinya ita kadai cikin daki tana Jin baqin cikin su kawun Dan batasan ma inda zata fara zama da matansa ba da Babu hakuri ko hankali a cikinsu ba ko kadan,
Da anbarta ba aurenma zata iya komawa kauyen tayi zamanta Amma auren baida Wani amfani da girmanka.

Husnah na daki duk tayi zuru cikin matsanancin halin tsoro da fargaban Menene makomarta,
Yanda zuciyarta ke bugawa kaman zata fado da tsantsan tashin hankali ya Saka hannuwanta ma rawa sukeyi tana dai zaune cikin fita hayyacinta aka Bude kofar bedroom din nata aka shigo...

Haydar ne cikin cikin fararen manyan kaya da Dan adonsa Dan inganta auren yar uwarsa da nuna farin cikinsa Koda kuwa ana cikin damuwa ne.

Ganinsa ya Sakata juyo da jajayen idanuwanta ta zuba masa bugun zuciyarta na tsananta har yayi yawan da ba'a cika so ba.

Qarasowa yayi da sauri Dan ganin ta kusa rasa bugun zuciyarta yana isowa ya riqeta Yana cewa

"Andaura aurenki da Abd.....
Bai qarasa ba Idanuwanta suka juye tana sauke numfashi me qarfi ta sume a jikinsa Dan sanyin Daya ratsa kunnuwanta da zuciyarta haryafi karfin bugun zuciyarta a lokacin.

Tarota yayi jikinsa hankalinsa na tashi ya fara Ambatar sunanta da qarfi Yana Dan jijjigata.

Daukota yayi gaba Daya a ya Sauko zai fita da ita zuwa asibiti Abdulhameed Daya baro gurinsu kawu ya gansa da sauri ya qaraso Yana tambayar abinda ya sameta.

Kasa amsawa Haydar yayi Yana kallan fuskanta.

Hannuwa Abdulhameed din ya Saka ya karbeta daga jikin Haydar din Yana cewa

"Mu koma a kira likita yafi zuwan asibiti tinda kaman Suma ne"

Juyawa sukai suka koma saman tana jikin Abdul Daya daukota kaman Bai dauko budurwa ba kaman yarinya ya dauko.

Bedroom din nata suka koma ya kwantar da ita khaltume ta kawo ruwa da sauri tace a fara yayyara mata a Gani.

Abdul dinne ya Karba ya zuba mata a fuska Yana ambatar sunanta har lokacin tana jikinsa.

Ajiyan zuciya tafara saukewa tana jerowa kafin ta Bude idanuwanta ahankali tana sake sauke ajiyan zuciya Wani bayan Wani.

Khaltume na ganin Hakan ta sauke numfashi itama hakama Haydar shi kansa Abdul din ajiyan zuciya ya sauke.

Akan fuskar Abdul ta sauke idanuwanta ko kyaftawa Batayi jikinta gabaki daya ya matu Bata iya motsa ko hannunta ahankali ta Bude bakinta kuka na Neman kwace mata tace

"Thank you"

Kalman data furta ya Yanke zuciyar Haydar gaba Daya har hawaye suka ciko Idanuwansa ace tana yiwa namiji godiya Dan ya aureta.

Shi kansa Abdulhameed kalman yankan zuciyarsa tayi Dan haka ya dora hannunsa ahankali kan bakinta tareda girgiza mata Kai yana kallan cikin idanuwanta yace

"Dad dinki Bai Bani aurenki Dan kice thank you ba Ya bani ne sbd yasan kinada mahimmanci me girma a zuciyarsa da bazai iya Bada ki kauyen ba"

Kalamansa suka Saka hawayen cikin idanuwanta saukowa tana Jin zuciyarta na samun nutsuwan fara dawowa hayyacinta idan har da gaske tanada sauran mahimmanci a zuciyar Dad dinta.

Haydar juyawa yayi ya fita Dan amsa wayar iyayensu na porthcrt da yanzu ne suka gama magana da ASH ya sanar dasu auren Husnah din.
Chapter 89 · 0% Book details