← Book details AmatulMaleek Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 58 OF 96

Sashe 58

AmatulMaleek Complete Hausa Novel · about 8 min read

Azaban dataji tana ratsata ne ya Sanyata rintse idanuwanta ahankali hawaye masu radadi suka gangaro mata Wanda take dangantawa da radadin ciwonta Amma Kuma daga zuciyarta radadin hawayen ke fitowa Dan nauyin kirjinta yakasa ko girgizuwa.

Qara Gudu hawayenta keyi tana kasa riqesu sai kawai ta saki kuka mara sauti tana rufe fuskanta da bakinta da tafin hannayenta ta can Kuma ruwan zafin na ratsata.

Ta jima a Hakan kafin ta share hawayenta ta Bude ruwan suka tsiyaye tana ciki batareda ta tashi ba
Suna gama tsiyayewa ta sake Tara wasu duk tana ciki zaune ruwan ya sake taruwa ta sake jimawa acikinsu kafin jikinta ya Dan samu karfi da kuzari tayi wankan daga zaune cikin bathtub din.

Tana gamawa brush ta sake yi ta sake goge fuskarta da towel me kyau kafin ta Bude kofa ta fito tana daurewa duk zafi tana tafiya daidai tinanin zata samu maamah a dakin amma maamah din Bata dakin.

Numfashi kawai ta sauke a boye kafin ta qaraso ahankali ta zauna gaban mirror tana Dan kallan kumburan idanuwanta da Jan su harma da fuskanta gaba Daya.

Bady oil ta daure sama sama ta shafa sbd anty Farha datake taimaka mata.

Turare ma kadan ta shafa anty Farha ce ta dauko mata kaya ta fara Saka undies kafin ta Saka doguwan Aleana katar gown mara nauyi Se kudi.

Tana gama shiryawa dawowa tayi kan shimfidan sallan da Akai mata ta zauna a zaune tayi sallan sbd bazata iya tsayuwa ba jiri take ji da rashin qarfin jiki.

Har ta idar da sallan maamah Bata shigo dakinba Dan haka ta miqe ahankali ta koma kan kujera ta zauna ahankali tareda hade qafafunta guri Daya qafarta sanye da safa me taushi.

Tea dinta aka sake qarowa zafi aka dawo mata dashi ta karba jikinta a sanyaye tace

"Thank you anty Farha"

Gyada mata Kai kawai anty Farha tayi tana nuna mata bowl na Naman da aka danderunsa tana cewa ta daure taci.

Dayake Bata iya magana bare gardamawa sbd zuci da gangar jikinta gaba Daya Babu me dadi.

Ahankali ta ringa cin Naman tana cusawa cikinta tana Shan tea din har ta Dan ci sosai ta shanye tea din gaba Daya Dan shine yafi mata dadi sosai a ciki.

Fitar da kayan Akai anty Farha ta Bata maganinta ta sha sai alokacin anty Farha ta zauna tana daukan wayarta tana Dan duba chats kafin ta turawa Mr Jameel txt na tambayar ASH TALBA zai tafi Greece dinne yanxu?

Mr Jameel dayake tareda ASH a lokacin Yana kammala Wani aikinsa ne da wasu baqinsa,
Satan kallansa yayi Yana sake karanta sakon Farha kafin ya Bata reply da cewan yau din zasu bi flight na dare zuwa lag,ya Dora da tambayar Yaya jikin Amatun.

Kasa basa amsar jikin Amatun Daya tambaya tayi ta ajiye wayarta tana Kai hannu ta dauko wayar Amatun Dan duba ko sakonsa idan ya shigo sai Taga wayar a flight mode Amatun ta Sakata.

Juyowa tayi ta Kalli Amatun Taga taqi kallo gefenta idanuwanta a rufe suke duk da ba bacci takeyiba.

******Maamah a Palo kuwa kusan da farko shock ta shiga na zancen farkawar Abeeda Daya shiga kunnuwanta,
Abeeda ta tashi?
Abeeda zata dawo garesu?
Abeeda ta rayu??
Hawayen farin ciki da tashin hankali da firgici ne lokaci Daya suka fara gangaro mata tana jikin duk jikinta na shiga rawa da sanyi.

Husnah ma hawaye takeyi cikin murna da farin cikin Dake Neman zautata,
Rungume maamah tayi tana murna tana maimaita mum dinta ta tashi.

Toshewa kan maamah yake Neman yi Dan kuwa Jin tayi kaman yau Abeedan zata dawo Dan haka ta shiga tsoro da tashin hankalin wannan data kasa rabasa Tin tini,
Wace kaddarar ce wannan?
Tayaya zata bari Abeeda taji wannan zancen auren?
Tayaya Abeeda zataji 'yarta ce take auren mijinta da itace tasani Kuma ta sheda yanda take tsananin son ASH da kishinsa.....

Kasa motsawa tayi daga inda take zaune tareda shiga tinani da firgici,
Ga dai labarin farin ciki me girma dasuketa Jira tsawon shekaru Amma gashi murnarsu na rauni sbd wannan auren daya zama auren kaddara.

Husnah kuwa wayoyi tafara cikin murna da farin cikin data rasa Ina zata Saka kanta ta miqe ta wuce dakinta tana cigaba da wayoyinta tabar maamah din zaune a palon kaman Wanda ta shiga coman itama.

Maamah gaba Daya mantawa tayi da Amatu batada lafiya sbd halinda ta shiga Dan haka ta manta da komawa dakin Amatun ta koma dakinta zuciyarta na nauyi da shiga tinani me zurfi da nauyi sedai bangare daya na zuciyarta farin ciki me girma da sanyi sosai takeji na tashin yar uwarta Dan kuwa a rayuwa babban burinta baifi farfadowan Abeeda ba,
Bayan yayanta da mijinta itace a duniya tafi kowa fata da adduar Abeeda ta Farka yau Kuma gashi Allah ya amsa adduarsu ya tayar musu da ita.

Amatu kuwa a kwance ta wuni jikinta gaba Daya yaqi dadi anty Farha ce ta ringa kulawa da ita cikeda kulawa da tattali tana kokarin hanata shiga damuwan ciwon.

Zuwa yamma zazzabi ya sake rufeta sedai anty Farha tayi kokarin ganin ya sauka ta hanyar Bata magani da goge mata jikinta ta rage Mata zafin.

Sai bayan sallan magrib gidan kusan kowa ya Tina da ciwon Amatun har maamah,
Bayan sallah magrib maamah ta shigo dakin tana kallan Amatun tana zaune tsakiyan gadonta Rabin jikinta rufe tana sanye da halfvest sbd zafin jikinta ya Ragu anty Farha na zaune sai a lokacin ta gama sallan magrib dinta.

Qarasowa maamah tayi tana kallan Amatun yanzu cikin tausayawa gaba Daya ta koma kaman wadda tayi sati tana jinya gashi ta tafi tanata murna da farin cikin farkawar Abeeda Batazo ta sake duba 'yarta ba.

Zaunawa tayi kan kujera tana kallan Amatun cikin tausayi da kulawa da kauna tace

"Amatu Yaya jikin naki?
Wai jikin har haka ne sosai Daman?
Kuka kikai ta yi ne fuskanki tayi Hakan Amatu?

Numfashi Amatun ta sauke ahankali tareda yin qasa da kanta kawai Dan batasan me zatace ba.

Anty Farha data miqe tsaye tana zare hijabin sallah tace

"Kuka taketa yi shiyasa duk ta sauyawa fuskanta kama Amma dai yanzu jikin nata yayi sauki,
Allah dai ya qaro afuwa ya Bata lafiya gaba Daya"

Amin" mamah tace tana dawo da kallanta kan Amatun tana cewa

"Meye abin kuka a ciwo Amatu,
Ai dauriya akeyi ba gashi yanzu kin samu saukinba..

Shigowan mum Aisha da Husnah ne a bayanta ya saka maamah da anty Farha kallan kofar banda Amatu da Bata Kalli kofan ba saima Dan lumshe idanuwanta tayi Dan batasan hayaniyar da zasu iya tadawa a dakin.
##MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

51
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI'IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

**************
Daga Husnah har mum Aisha idanuwansu akan Amatun suke fatar jikinta na daukan idanuwansu sbd Babu Wanda ya taba ganinta a Hakan acikinsu,Basu dauka kyau da lafiyayyar jiki har haka ne da ita ba,

Mum Aisha kallan qurullan datake mata Se yanzu ne take jin tausayin Naufal Ashe abinda yasashi nacewa Amatun kenan sbd ganin asalin kyanta da Kila shine kadai ya taba ganinsa gashinan an sabauta mata shi sbd wannan kyan Dan macijin,

Husnah ma kuwa kasa dauke idanuwanta tayi daga kan Amatun Babu abinda yake jikin Amatun da Bai tsole idanuwanta ba ya tokare kirjinta Dan kuwa da ace Amatun da gaske zata zama matan Dad dinta kishiyar mum dinta zata iya zaucewa Dan Taya mum dinta kishi sbd da ba ita din yarinya ce ga zama matar Dad dinta ba da tabbas Amatun zata iya zautar da Dad dinta idan ya ganta ahakan,

Anty Farha ce ganin duk sun rude sunma rasa me ya kawosu bare magana ta nufi wardrobe zata daukowa Amatun rigar da zata Saka aka Bude kofar bedroom din cikin nutsuwa tareda turowa
Kaman a mafarki dukkaninsu qamshinsa ya sakasu juyawa ga kofar gaba dayansu.

ASH TALBA ne da kansa ya Bude kofar bedroom din Yana sanye da kayan Daya fita dasu tin safe hakama qafafunsa ba slippers bane Da Yana dawowa gida yake zare takarminsa ya Saka slippers dinsa masu taushi da tsada dasu yake yawon cikin gidansa Dan sakewa.

Da alama dawowansa mansion din kenan Kokuma daga mota Kai tsaye Nan din ya fara zuwa.

Mamaki ne a kan fuskan kowannensu Banda Farha data ji sanyi da farin cikin ganinsa zuwa duba Amatun dasuka cire Rai da zuwan nasa,

Maamah Amatu ta juyo ahankali ta kalla da idanuwanta dasuka cika da mamaki Amma tana boyewa,

Amatun kaman yanda Bata dago ta Kalli su Husnah ba bayan shigowansu hakama yanzu din Bata Kalli kofarba duk da qamshinsa ya bata tabbacin waye din y shigo dakin.

Mum Aisha Baki take Neman saki zarginta na son sake tabbata sedai Kuma itama dole ta danne nata mamaki da tashin hankalin tana boyewa kaman yanda maamah tayi.

Husnah ce ta kasa boye mamaki da firgicinta harma da baqin cikin dayake neman mamayeta na ganin Dad dinta a dakin Amatun,duk da tasan bedroom dinta zai tafi kila ya zo Nan din.

Cikin kokarin daidaita kanta kada ta bayyanarda abinda takeji a gabansa tace

"Dad ba Nan ne bedroom dina ba,
Kuma naji sauki sosai kana fita na farfado na.....

Idanuwansa Dasukai ciki ciki da pressure datai masa yawa ya dauke daga Amatun Daya zubawa su tin shigowansa ya watsawa Husnah ahankali ya furta

"Husnah kuje idan na fito zamuyi maganan zan duba Abeeda I have a flight to catch"
Chapter 58 · 0% Book details