← Book details AmatulMaleek Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 70 OF 96

Sashe 70

AmatulMaleek Complete Hausa Novel · about 8 min read

Qin daukan wayarsa tayi harya Dena Kiran,
Mr Jameel kawai yacewa bayan sun tafi driver ya kawo masa Husnah din office zasu fita.

Tsit gidan yayi kowa cikin damuwa da nauyin zuciya yake musamman Husnah da Maamah Dan Amatu yunwarta kasa riquwa tayi jiki ba qwari ta fito ta sauko qasa ta samu abinci a kitchen taci ta qoshi ta koma sama kenan zata shige bedroom dinta Husnah ta fito dakinta suka Hadu a tsakiyar palon
Kasa riqe zuciyarta Husnah tayi ta tsaya gaban Amatu tareda tarewa cikin daci da tsananin baqin ciki tace

"Menene sunan da zaa kiraki dashi?
Kafin ki jefawa mijin Aminiyar mahaifiyarki kanki ya kamata kiyi tinanin alaqan maamah da mum,
Menene su.....cikin Bacin Rai da baqin cikin maganar idanuwanta suka rufe bata tsaya komaiba ta kama hannun Husnah din da karfi ta fizgeta zuwa hanyar palon Dad din nata Dan Bata amsar maganarta a gabansa sedai ko taku biyu bataiba taji an riqo nata hannun tana juyowa Taga maamah tana mata Wani irin kallo idanuwanta jajir.

Magana zatai sbd idanuwanta da suka cika da bacin Rai da baqin cikin abinda Husnah din ta fada mata maamah ta katseta Kai tsaye da cewa

"Ina Zaki?
Ina Zaki jata kuje??

Sakin hannun Husnah din tayi tareda kallan maamah din bacin ranta Baya boyuwa tace

"Maamah kinji kalaman data jefeni dasu?
Kin....

Daga mata hannu maamah tayi cikin Bacin Rai da baqin ciki tana cewa

"Komai aka fada Amatu kece kikaja,
Meyene alaqarki da abinda suke fada din?
Shin kin menene ma ya hadaki guri Daya da ASH din harma wanna abin duka yake neman lalacewa?

Katseta Husnah tayi hawayen baqin cikinta na qaruwa tace

"Maamah wlh a dakin dad ta kwana....

Shiru maamah tayi jikinta na rawa tana kallan Amatun da dukkanin bacin Rai hakama Amatun sai alokacin hawayen baqin ciki me tsananin gaske ke ciko idanuwanta
maamah tace

"Me Husnah ke fada?

Saukowa hawayenta sukai tana kasa cewa komai saima nauyi da zuciyarta tayi kafin tayi magana baqin ciki ya Saka idanuwanta Neman juyewa ta dafa Bango da sauri sbd jirin Daya debeta zai zubar Dan Bata dauka maamah zata jefeta da wannan tambayar ba.

Kuka Husnah ta sake fashewa dashi tana ihun mum dinta mutuwa zatai idan taji wannan mummunan labarin,
Hakama Amatu taci Amanar mum dinsu da Haydar.

Gaba Daya hargitsa gurin tayi da kukanta da maganganunta da suka Saka Amatu barin gurin zuciyarta na nauyi da tsananin damuwa da bacin Rai da fushin da batama San tanada shi ba.

Maamah kasa cewa komai tayi sai kawai ta bar palon ta kira ASH da kanta akan tanason magana dashi idan Yana gida.

Baya gida ya sanar mata Amma zai dawo da wuri a ranar.

Mr Jameel kuwa drivern da aka Saka ya kawo Husnah office din Dad dinta ya sake kira Amma driver ya sanar masa Husnah Bata fito ba.

Amatu bayan shigewarta daki kuka ta saki me ciwo da dacin Rai sbd lamarin yafara yimata yawa,
Ta rasa tayaya ta rasa so da kauna tareda yardar mahaifiyarta..

Kuka takeyi sosai Wanda ma batasan Yaya takejin Yana zuwaba Yana sake tayar da zuciyarta zuwa wuya.

Wayarta anty Farha keta kira Amma takasa dauka Dan haka ta kira khaltume wadda sukai tsit sbd ihun kukan da Husnah keyi tana fasa kayan palon saman ko zuciyarta Dake balbala da wuta zata sauka Amma Sam Babu abinda takeji a zuciyarta da jikinta bayan zafin baqin ciki.

Maamah Dake dakinta tana Jin ihun Husnah din da tashin hankalin datakeyi tana ambatar sunayen Amatu Dana mum dinta Amma Bata motsaba daga dakinta sbd yau lamarin ya isheta Babu abinda take buqata bayan barin gidan itada Amatun Dan ita yanzu bama zata iya bari Abeeda ta dawo ta tadda Amatun a gidan ba bare tasan meya faru.

Khaltume ce ta sanar da anty Farha abinda yake faruwa cikin damuwa gashi mum Aisha ta tattara ta fita batama gidan bare dakatar da Husnah wadda gaba Daya t zare Babu abinda take gani bayan Dad dinta da Amatu suna cin Amanar mum dinta.

Ita kanta Amatu datake dakin tana Jin duk abinda Husnah din keyi hakama kuka takeyi sosai Dan kuwa tasa bacin Rai da tsananin kukan da Maamah Tasha Koda Bata fada ba,
Ita komai ya isheta itama batason zaman kaman yanda Husnah take fadan bazata iya zama inda Amatu take ba itama Hakan takeji sbd abubuwan sun mata yawa.

Anty Farha Kam tashi hankalinta yayi Dan haka ta kira wayar mr Jameel ta sanar masa anata tashin hankali a Mansion din.

Satar kallan ASH yayi Wanda yake amsa waya ahankali yaga yanda yake wayar hankali kwance da nutsuwa.

Yanda Mr Jameel yake satar kallansa ya tabbatar masa da magana me mahimmanci Dan haka ya Dan takaita wayar ya kashe Yana kallansa yace

"Uhumm Ina ji"

Cikin damuwa da Dan sauke Kai mr Jameel din yace

"Ana rigima ne a mansion tsakanin Husnah da L.A"

Shiru yayi tareda dagowa ya zubawa Mr Jameel din idanuwansa Yana nazarin zancen sbd baijin akwai abinda zaisa ma ko hayaniya Husnah tayi da Amatu Bare rigima,
Wayar da maamah tai masa ce ya dawo masa.

Wayarsa ya dauka Kai tsaye maamah din ya kira.

Tana daf da katsewa ta dauka a natse sedai muryarta Sam Babu dadi da alamu kuka tai ko makamancinsa.

Baima yi mata magana ba sai kawai ya kashe wayar Yana nazarin abinda zai zama rigimar,
Idan har Husnah zatai hayaniya da little Abeeda akan maganar aurensa dayake kanta ne dakuma mum dinta hakama Asmau yasan Daman tanada damuwa da auren.

Idan maamah tana cikin wannan halin to little Abeeda na cikin Wanda ya fisa,
Dagowa yayi ya Kalli mr Jameel Kai tsaye yace

"Ayiwa Maamahn little Abeeda komai su wuce tareda Husnah Greece"

Kaman Mr Jameel na Jira ya gyada Kai da sauri Dan kuwa yau ba sai gobe ba zai tura su Lagos suna can zai qarasa musu komai su wuce.

Fitowa sukai Kai tsaye mota ya nufa da sauri aka Bude masa ya shige suka nufi gida Yana kashe wayoyinsa tin a hanya.

Koda suka iso Husnah tafara gabalaita da kukan datakeyi da tashin hankalin hakama maamah dole tazo ta riqeta tana kokarin dawo da ita hankalinta cikin kulawa da damuwa me tsananin gaske.

Anty Farha ta riga su ASH isowa Dan haka ta ringa buga dakin Amatu wadda ta rufe kanta data cikin tayi kuka harta galabaita sbd maganganun da maamah ta shigo ta fada mata masu kama da tafiyarsu zasuyi subar gidan hakama batajin zata sake barinta ko fitowa daga dakin nata har su samu barin gidan.

Tashi hankalin anty Farha yayi musamman ganin palon kaman anyi damben balai a cikinsa sai tsoron ko Wani abin ya faru kafin su zo ya shigeta ta ringa buga kofar tana Kiran sunan Amatun,
Gasu maamah da Husnah a palon hakama su karima suna palon qasa a tsaye jiki duk yayi sanyi sbd Basu taba ganin wannan tashin hankalin a gidan ba bayan na gobarar da Akai.

Babu tsammani sukaga ASH a cikin palon kallo daya yayiwa gurin gaba Daya ya Kalli Husnah Dake jikin maamah tana kuka har lokacin ya nufi kofar dakin Amatun Kai tsaye daidai ta budewa anty Farha kofan dakin Dan haka anty Farha janyewa tayi ta basa kofa ya shiga Kai tsaye Yana kallan idanuwanta dasukai jajir ko tsayuwar arziki Bata iyayi.
##MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

62
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI'IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

*************
Duk tashin hankalinda Husnah take ciki Bude jajayen idanuwanta tayi ta zubawa kofan dakin Amatun Daya shige.

Maamah ma kusan mutuwar zaune take Neman yi sedai kafin suyi Wani motsi mr Jameel dayake siqe dasu Kiran Farha yayi Yace tace su fito ga motar zuwa airport na jiransu ya fasa bari gobe su tafi yau ze ingizasu Lagos suje su Jira visa daga can su wuce hankalinsu suka ya kwanta Dan idan ba zuwa sukai suka dubo madame Abeeda sukaga halinda take ciki bazasu bari a zauna lafiya ba tinda yanajin komai dayake faruwa a cikin gidan a bakin anty Farha gameda auren.

Mum Aisha ma da isowanta gidan kenan Mr Jameel yace Maza Maza su fito jiransu akeyi jirgi ze tafi ya barsu.

Mamaki me tsananin gaske dukkaninsu suka shiga musamman maamah da mum Aisha da basusan da tasu tafiyar ba tsoro ma ne yake Neman kama mum Aisha Amma Kuma tinda mr Jameel yace tafiyar zasuyi to tabbas ASH ne ya Bada wannan umarnin gashi babu me ikon tambayar dalili sedai Babu Wanda yakeda raayi na tafiyar a cikinsu a dai wannan halin da ake ciki har gwara maamah tanason ganin Abeeda Kam Amma ba yanzu da ake cikin wannan tashin hankalinba sedai Babu gurin musawa ko fasawa.

AmatulMaleek dinma Basu samu Gani ba anty Farha itace ta hado kayan maamah tana sake tausarta da maganganun nasiha da Sam Babu me shigar maamah din tayaya zata bar Amatun a gidan bayan ASH Yana gari.

Kaman wasa sai gasu a mota an wuce dasu airport zuciya fal tashin hankali da mamakin Daya kasa barinsu tantancewa Saida suka daga zuwa Lagos suka tabbatarda dai kuwa tafiyar zasuyi ba Shiri ba sanarwa.

Basu dawo hayyacinsuba Saida suka samu kansu a Lagos tareda anty Farha wadda zata jagoranci tafiyar duk da itama ba shiri Amma ta yarda ta biyosu su tafi din Dan masifar kowannensu yawa ne da ita gwara akaisu gurin Abeedan idan qarasa ta zasuyi da masifarsu su qarasata acan din.
Chapter 70 · 0% Book details