← Book details AmatulMaleek Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 33 OF 96

Sashe 33

AmatulMaleek Complete Hausa Novel · about 8 min read

Abincin da Husnah ta zuba masa Shima ya kalla
Yanason tuwo Amma yanzu dare yayi masa da cinsa sosai Dan haka kadan Shima yaci ya buqaci tea.

Husnah Bata iya dafawa ba Dan haka Amatu ta kalla wadda ita Kuma Daman hanyar barin gurin take nema Dan haka ta miqe ahankali ta bar gurin zuwa kitchen.

Tana aikin tana Shan fruits dinta Daman shi tuwon taci kadan a dining,
Tana gamawa ta juye ta dauko ta fito
Koda takai tea din daga Husnah har Abdul sun tashi ba kowa saishi a gurin Dan haka a natse ta iso ta ajiye tareda zuba masa ta juya tabar gurin.

Dakinta Takoma brush kawai tayi ta kwanta Dan baccin takeji sosai a yau din.

ASH kuwa Daman yace Abdul ya samesa bayan sun gama cin abincin Dan haka Abdul Yana kwatanta gamawansa ya fito a natse ya nufi palonsa tareda knocking cikin girmamawa da sallama ya shiga bayan ya basa izinim shigowa.

Zaunawa yayi bayan ya sake gaida Dad din.

A natse ya qarasa wayarsa kafin ya kasheta gaba Daya ya ajiye gefensa ya Kalli Abdulhameed din cikin nutsuwa yafara fada masa yafara shirye shiryen tafiya makaranta zaibi Haydar can inda yake zuwa nxt month Dan angama komansa kadan ne abubuwan dasuka rage.

Godiya sosai Abdulhameed yayi cikin bayyanarda farin cikinsa tareda adduar Allah ya Saka da Khairan.

Koda ya fito yasan Yan matan sunyi bacci Dan haka dakinsa Kai tsaye ya wuce cikeda murna da farin ciki me tsananin gaske ya ringa nafila yana godewa Allah tareda yiwa ASH addua da iyayensa babah da maamah.

Washe gari lokacinda ya sanarwa da Amatu kasa riqe farin cikinta yayi ta rungumesa tana Jin dadi sosai tareda yiwa ASH din addua Dan kuwa zuwa yanzu ta tabbatarda ba Wani maganar aurenta dayake gabansa Dan haka itama zata dage tayi abinda yake gabanta kawai,

Maamah ma sosai tayi farin ciki Kuma dole Badan tanada yanda zatayi ba ta tafi har palonsa tayi masa Godia ta fito
Husnah ma tayiwa Abdul din murna sbd Haydar ze samu na gida a tareda shi Koda maganar auren Amatu da Dad dinsu ta Isa kunnensa aqalla tasan Abdulhameed zai tsaya ya kula dashi batareda ya shiga Wani halin ba duk da dai su haryanxu soyayyar kuruciya ce yakewa Amatun.

Cikin farin ciki yau sukai breakfast dinsu a dakin maamah tareda ita suna gamawa Farha tazo tini Dan haka Amatu fitowa tayi ta Takoma bedroom dinta ta shiga wanka,

Kafin ta fito duk kayan da aka siyo jiyan Farha ta jera komai a inda ya kamata dakin ya sake sauyawa zuwa na budurwar da Bata rasa komaiba na duk Wata luxury rayuwa.

Dayake tayi latti ba Bata lokaci ta shirya kaman dai yanda kusan kayan duk dogayen riguna ne masu kudi
Acikinsu ta shirya suka fito Kai tsaye mota suka shige zuwa school.

Abinda yake bata mamaki da kawo mata Farha da Akai shine me zatai mata?
Haka kawai zata ringa rakata makaranta su dawo?

Bata tambayarba sbd batama ga Wanda zata tambaya ba hakama ita kanta Farha din yanda take kula da ita tana nuna mata wasu abubuwan da Bata saniba yasa take ganin ba takura sosai a yawonta da ita.

Kwana biyu duk suka fita sai anyi siyayyar abubuwan buqatanta harma da Wanda Bata buqatan,
Farha kaman designer ce kaman Kuma beauty designer,hakama abinda ta lura dashi shine kodai qanwar Mr Jameel ce Kokuma yar uwarsa sbd akwai kusanci a tsakaninsu hakama kusan komai shi Farha din ke kira Yana Bada kudin da kamar baisan zafinsu ba dayake kusan shine bankin ASH TALBA.

A cikin kwanakin dasukaita zuwa suna wucewa Farha ta Saka Amatu Dan fara sakin jiki da ita sosai duk kamun kan Amatun da rashin son mutanenta Saida ta sake da Farha duk da ta girmeta Amma Sam ba wanna tsakaninsu hakama a aynzu data fara sabawa da amfani da kayan da aketa siyowan taji tafi sakewa a cikin dogayen rigunan dasuka zama suturarta a yanzu,

Ta bangaren cikin gidan kuwa sosai kowa ya zama busy shiyasa kusan kowa a gajiye kowanne dare ake kwantawa,

Abdulhameed shirye shiryen tafiyarsa kawai yakeyi sosai hakama maamah duk Jin takeyi ta shiga sanyi sbd tinda ta haifesu Bata taba nesa dasu ba Koda na kwana biyu ne koyaushe tana tareda yayanta duk inda zasu Dan haka yanzu dazai tafi wata qasa duniyar Jin takeyi kaman bazai iyaba sedai tinowa da Haydar na can Kuma zasu kula da juna sosai yake sata Jin hankalinta ya kwanta,

Husnah Kuma exams ne a gabanta shiyasa ta kasa gane kanta sosai ta dage sbd kusan Amatu sosai take kawo wuta a nata karatun Dan haka yanzu da Bata kaunar abinda ma zaisa Dad dinta ya duba cigaban Amatu akan nata Sam Bata kaunarsa.

*****Ta bangaren ASH TALBA kuwa kusan kullum da Amatu ta gane Yana shan tea da dare koyaushe kafin ta shige saita dafa ta Kai dining a flask ta ajiye ta shigewarta,
Shima Daya fahimci yanzu kullum ana aje masa sai ya rage fitowa cin abinci tareda su Sai ya gama komai zai fito yasha ya koma ya kwanta.

Mum Aisha tayi tafiyar dole wadda take Jin idan batai ba zata iya fashewa a cikin gidan sedai a Tararda gawarta Dan haka tayi tafiya kanta ya fara warwarewa kafin ta dawo tasan yanda zatayi da yar cin Amana maamah wadda taci amanar aminta da zumunci.

Tafiyar Abdul tazo daidai da tafiyar Husnah porthcrt mahaifiyar Faisal ta rasu Dan haka sosai hankalinta ya tashi haka itama Maamah sosai ta shiga damuwa ga exams sunayi a lokacin,

Ranar da Abdulhameed ya wuce AmatulMaleek Tasha kuka a jikinsa kaman shine yayan itace kanwar
haka ya ringa rarrashinta Yana Bata qwarin gwiwan fuskantar rayuwarta batareda tsayawa kebe kanta ko takura kanta akan aurenda ASH Kila ya manta dashi.

Maamah ma taji dadin shawarar Daya bawa Amatun sbd so take Amatun itama ta manta da Wani maganar auren harsu samu Abeeda ta tashi Dan Tana tashi tasan ASH TALBA bazai qara ko kwana da auren Amatun ba zai sallameta asiri rufe batareda Abeeda ma tasan anyi auren an warwareba.

Abdulhameed ya tafi yabarsu da kewansa Dan haka maamah dole cikin kwanakin ta Maida kulawanta da tattalinta ga Amatu wadda ta shiga damuwa sosai na tafiyan Abdul sbd shine abokinta Kuma abokin shawararta.

Farha da maamah ne suka dage harta sake batareda ta Dade cikin damuwarba sbd exams dinta.

ASH TALBA tin washe garin rasuwar umman Faisal yaje yayi gaisuwa ya dawo,
Husnah ma itace ta riga Amatu gama exams dinta Dan haka babu Bata lokaci tayi Shirin tafiya porthcrt Kuma tareda maamah zasu itama tayi gaisuwa.,
A bangaren husnah da gangan ta da tafiyar maamah din sbd idan suka tafi gidan ze Kona ba kowa sai Amatu da masu aiki wainda suke bangarensu daban,cikin mansion dai ze kasance Amatu ce kawai Dan haka tsoro da firgici bazai taba barinta yin karatun da zatai exam me kyau ba sbd itama Bata karatun exam din ya lalace ne kwata kwata daga ranar da umman Faisal ta rasu.

Ita kanta Amatun da zasu tafi hankalinta tashi yayi sosai da barinta da zaayi ita kadai a gidan sosai ta shiga damuwa Amma batai magana ba sbd tasan ma ba lallai atafi da ita ba Kuma ko taje Yan uwan Faisal din da yawa basa Sonta ganin itace ta Hana ya auri Husnah ko gaisuwar rasuwar txt tai masa har so uku duk bayan awanni saita masa ta tura masa sbd bazata iya kiransa ba tin ranarda aka daura aurenta masu sake magana ba baice mata komaiba ko a waya haka itama batasan me zata ce masa ba,
A makarantar ma sosai suke wasan boyo da juna kaucewa juna sosai sukeyi basa son su Hadu.
##MAMUH#

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

31
Su Husnah na hanyar zuwa airport ta Ciro wayarta daga handbag dinta shedan na ingizata ta Dan shakka Amma Kuma zuciyarta na sake turata ta Nemo numbern Naufal ta tura masa txt din idan Yana son Neman gafarar AmatulMaleek ita kadaice a Mansion ko Babu kowa Se masu aiki hakama Dad dinta baya gari.

Tana tura sakon ta mayar da wayarta handbag dinta ta rufe tareda kallan maamah da itama itan ta kalla cikin kulawa ta saki murmushi tana Dan kwantawa jikin Maamah ahankali tace

"Maamah Allah yasa mum dina ta samu lafiya ta dawo cikinmu Ina kewanta sosai."

Numfashi me dumi maamah ta sake tana amsawa da "Amin ya Allah" zuciyarta na Dan nauyi sbd duk lokacinda ta Tina da Abeeda da auren mijin Abeedan Dake kan tata 'yar Jin takeyi hankalinta da duniyarta na jijjiga sosai cikin tashin hankali da damuwa.

Suna Isa airport Basu Wani jimaba suka hau jirginsu ya tashi Husnah na sauke ajiyar zuciya me sanyi.

Ranar da suka tafi din a school Amatu ta wuni Se magrib ta dawo gida cikin sanyin jiki tayi wanka ta fito taci abinci Takoma daki ta kwanta zazzabi na Neman rufeta sbd kadaici da rashin nutsuwar zuciya.

Bacci Rabi da Rabi tayi har tasamu asuba tayi ta tashi tayi sallah sai alokacin ta koma baccin kirki.

Bacci tayi cikin nutsuwa da Kwanciyar hankali har qarfe Tara kafin ta tashi tayi wanka ta fito daure da towel ta zauna gaban mirror ta shirya ta Saka undies kafin ta Saka doguwar rigar army green ta fito qamshinta na tashi ahankali cikin sanyi ta nufi kitchen Bata nufi dining ba Dan batajin zaa jera abinci tinda ita kadaice sedai ga mamakinta tini aka jera abincin breakfast dinta komai da komai Yana kan dining din dole can ta koma taci abincin tana gamawa ta miqe Takoma daki ta sake Dan gyarawa ta fito.

Dayake ko Farha kwana biyu Bata Nan ita kadai ta shiga mota driver ya jata zuwa school.

Acan ta wuni yauma sai yamma ta dawo tana gama komai ta shige ta rufe daki ta kwanta.

Kwana hudu da tafiyarsu maamah ta gama exams dinta ita Dan haka yau din data gama da wuri ta dawo tana shigowa mansion din ana Kiran laasar.

Wanka tafara yi Tayi sallah tana Jin nauyin dayake kanta kaman ya sauka tinda ta gama jarabawanta.
Chapter 33 · 0% Book details