← Book details AmatulMaleek Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 66 OF 96

Sashe 66

AmatulMaleek Complete Hausa Novel · about 8 min read

Gefen maamah dukkaninsu suka tada sallah
Suna gamawa Nan suka jiyo suna fuskantar maamah itama kallansu tayi da mamakin yanda suka iya zuwa sukai zamansu musamman Amatu datake da karatu a gabanta Dan haka kafin amsa gaisuwarsu fada Tayi sosai suna Bata hakuri hardai ta sauka suka sake gaisawa cikin nutsuwa tana amsawa tana tambayar Yan gidansu Farha din idanuwanta na kan Amatun data sauya gaba Daya ta koma kamar wata wadda taje Hutu da Jin dadi kawai sbd Hutu ne sosai ya bayyana a tattare da ita,
Ta ciko kadan,fatarta ta sauya,haskenta ya sake samun lafiyayyar kyau,hakama qamshinta ya sake zama na musamman..

Irin kallan da maamah kewa Amatun ya Sanya Amatun shiga firgici da bugawan zuciya ahankali sedai Bata bari ta iya hada ido da maamah din ba ta miqe tana nufar inda ta ajiye wayarta tana daukowa Taga tanada misscalls uku tana ganin numbers din ta tabbatarda waye me Kiran Dan haka text kawai ta iya turawa a lokacin tana Saka Kiran Abdul Dan kawar da kallan qurullan maamah a kanta ta miqa mata wayar suka fara magana daga Nan anty Farha itama ta sake shiga firar aka bar zancen kallo aka koma na fira duk da Amatun Bata cikin sakewa har lokacin zuciyarta a yanayi na yar fargaba take.

Su karima ne suka kawo musu abincinsu a Nan dakin aka Jere musu Daman suna buqatan abincin.

Ko fara ci Basu yiba husnah ta shigo dakin batareda tasan suna Nan ba da niyar magana da maamah akan dawowan Amatun sai Kuma ta gansu a tareda Maamah din.

Qarasowa tayi ahankali ta zauna sama sama ta gaisa dasu tareda zubawa Amatun idanuwanta dasuke jajir yanzu kullum sbd ciwon Rai dai yaqi qarewa kowa a gidan.

Yanda take kallan Amatun a qure hankalinta na Neman tashi cikin shakka da tsoro Dan kuwa ta kasa yarda da Nigeria su Amatun suka tsaya hakama hakanan taji takasa yarda da rashin dawowan Dad dinta Daya kamata y dawo a sati biyun da suka wuce gashi acan Greece ance yabaro.

Maamah ce ta lallabata tace taci abincin tareda su Dan haka ta zauna cin abincin tareda su Badan tanajin yunwa ba Dan kuwa Jin tayi cikinta ya cunkushe gaba Daya ya cika da baqin ciki har Babu gurin Shan iska.

Amatu kuwa abincinta takeci a natse cikin Kwanciyar hankali Dan yunwa takeji ba laifi, hakama anty Farha abincinta takeci babu abinda ya dameta da Husnah din bare maamah datake ta lallabata kaman yarinya qarama.

Sbd Husnah Dake gurin yasaka hirarsu batai Wani tsayiba bayan cin abincinsu tattarawa sukai suka nufi daki sbd suna buqatan wanka da Hutu Daman.

Saida safe sukai da maamah suka fice daga maamah din har Husnah suna bin Amatu da kallo kowa zuciyarsa na harbawa batareda yasan abinda yake zuciyar Dan uwansaba.

Su kuwa suna Isa daki Amatun ce tafara yin wanka Dan Koda suka shigo tini karima ta gyare dakin qamshi da sanyin AC ne kawai ke tashi.

Tana fitowa wanka Shirin bacci kawai tayi ta Haye gado Daman sun Riga sunyi ishai a gurin Maamah.

Wayarta ta kunna daga kwancen data ke ko minti uku baayiba kiransa ya shigo wayar ta dauka a hankali jikinta na mutuwa da Jin muryarsa cikin wata irin nutsuwa da kamewansa dakuma wahalalliyar so Dake dawainiya dashi.

Kaman yanda take amsawa a kasalance da sanyi kusan Shima ahakan yake mata magana Dan haka suka jima a shiririce suka gama wayar tayi bacci sbd bacci me nauyi ne yake cikeda idanuwanta.

Koda anty Farha ta fito har tayi shirunta ta gama tini ita tayi Nisa a bacci.
#MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

58
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI'IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

******************
Washe gari kusan latti kowa gidan yatashi sbd bacci da suka jima sunayi,
Mum Aisha da safen lokacinda ta Hadu da Amatun gurin cin abincin mamakinta kasa boyuwa yayi a gaban maamah data hawo saman duba Husnah data ringa mata kuka bayan tafiyarsu Amatun akan ta taimaketa tasa a raba auren Nan kada mum dinta taji zata iya rasa ranta,
Mum Aisha bakinta Kai tsaye batareda itama tayi Kai tsaye da yawa ba tace

"Amatu Biki kuwa kika tafi Lagos kokuwa Wani gurin kuka tafi Dan Sam bakiyi kama da wadda ranar Lagos ma ta sauka akanta ba"

Daga Amatun har maamah data shigo palon a lokacin har Husnah data dago kowannensu shiru yayi cikin rashin sanin abin yi ko fada.

Anty Farha ce tahau kame Kamen zancen tana cewa

"Bikin Hutu ne ai bana wahala ba,Kuma tinda mukaje Amatun Bata fita koina ba Dan bazan bar matar ASH TALBA guda ba tana yawo ta jigata"" qarasa maganar tayi cikin Maida zancen wasa duk da Babu Wanda zancen yake wasa a gurinsa cikinsu,

Abincin ma kusan kowa Jin yayi cikinsa ya cika Banda mum Aisha datai maganar ko a jikinta.

Maamah jiki ba qwari ta koma inda ta fito Husnah ma Shan dole tayiwa tea din Dake hannunta tana danne zuciyarta Dake Neman dawo da abinda taci.

Amatu ce kawai ta qarasa cin abincin cikin sanyi batareda tace komaiba.

Suna gamawa Shirin school tayi ta ficewarta tareda anty Farha da itama tana buqatan zuwa shagonta Taga halinda ma'aikatanta ke ciki.

Bayan fitarsu kallan Husnah mum Aisha tayi cikin takaici Kai tsaye tace

"Ke kin yafe karatun kenan sbd baqin cikin wata zata fiki matsayi gurin Wanda kike dukan gaban mahaifinki ne."

Kasa cewa komai Husnah tayi sbd Babu ranar da yanzu mum Aisha Bata tayar mata da ciwon depression dinta da maganganunta Wanda mum Aisha da gasken so take kafin ASH ya dawo ta jiyarwa da yar tasa qwaqwalwa kowa ya huta.

Amatu a school ta wuni sai yamma ta dawo gidan batareda anty Farha ba wadda Se dare zata dawo Dan haka dakin maamah tayi sallah tana idarwa taci abinci ta kwanta baccin yamma.

Sai magrib ta Farka ta shiga toilet tayi alwala sukai sallah tana idarwa waya ta fara da anty Farha dake Bata labarin abinda ya faru a shagonta yau din na wata yar matsala da itace ta Sanyatama dadewa Bata Dawo ba.

Maamah tanason yiwa Amatu magana akan auren ASH TALBA amma Kuma sai ta fasa sbd ganin kwata kwata Amatun rayuwarta takeyi a natse batareda ma tinawa da auren ASH dinba Dan haka sai takejin baima kamata tana maimaitawa Amatun maganar aurenba Koda da sunan gargadine Dan haka sai kawai ta hadiye maganarta koba komai yanzu ASH din tinda Abeeda ta farfado bawani zama zai ringa yi anan ba kafin a dawo da ita.

Cikin kwana biyu maamah ta sauyawa Amatun zuwa normal yanda suke hakama itama Amatun hankalinta ya kwanta ganin mahaifiyarta ta dawo mata daidai sai kawai take sake samun Kwanciyar hankali da nutsuwa ta bangare daya ma sosai take cikin nutsuwan zaman anty Farha tareda ita Dan tattalin datake nuna mata sai takejin kaman ASH din Yana tareda ita sbd komai na kulawan anty Farha datake mata bisa ga umarninsa ne da Kuma kaunar da anty Farha din ke Mata da zuciyarta Daya.

Mum Aisha ma da kusan abinda takeso ne yaketa Shirin faruwa a gidan na tarwatsewa Daya bayan Daya sai hankalinta yake Dan Kwanciya sbd tsaf ta hango kadan kadan Husnah Neman zaucewa takeyi a cikin gidan ubanta gashi ASH kaman Wanda baida niyar dawowa shiru Bai dawoba Dan haka Husnah ta sake shiga tashin hankali da damuwa ga barazanar da kullum mum Aisha da Naufal ke Mata akan fada masa abinda tayi idan har Bazata ringa abinda suka sakataba na son tarwatsa maamah da Amatu.

Damuwa da kadaici da barazanar mum Aisha ya Saka Husnah fara zarewa tana komawa ruwa na ciwonta Dan haka maamah hankalinta yafara tashi itakuma karshe ma kusan dakin Husnah din ta dawo da kwana Dan Husnah Bata iya bacci kowanne dare cikin kuka da buga kanta take gashi Sam duk wayar da ASH keyi da maamah din Dan Jin lafiyar kowa da Gidan Bata fada masa ba sbd kada ta raba masa hankali ga ciwon Abeeda da Kuma na yarsa,
Ita kanta Husnah din ta kasa barin ya gane halinda take ciki sbd Yana sani zai tabbatarda ya gano meya sameta anan zai San tasan ba shine ya haifetaba,kisan mummuke mum Aisha ke Mata tana Bata azabar boye Dan kuwa ko maamah Bata Saniba Dan ita kanta Husnah batason maamah ta sani tasan cewa itace ta tura Naufal yiwa Amatu fyade Dan kuwa tana sani zata iya juya Bata Baya bayan ita kadaice gatanta da bangon jinginarta a yanzu dakuma zamanta wadda kawai zata hurawa auren Amatu da Dad dinta wuta ya mutu batareda mum dinta ta dawoba.

Satinsu Amatu biyu da dawowa ASH TALBA ya sauka Abuja lokacin Bata gidan tana school Kuma Bata dawo ba Sai yamma Dan haka batama lura da motocinsa da aka fito dasu daga inda suke ba wainda suke nuna ya dawo a duk lokacinda zaka gansu a filin harabar gidan kusa kusa.

Ganin maamah a kitchen tareda su karima yasata tinanin me takeyi a kitchen ASH Baya gari tinda yawanci abincin dazai ci ne kawai take Saka hannu a ciki yanzu sbd sanin bayason abincin masu aiki.

Bata tsaya ba bayan maganarda tayi da maamah din sama sama ta wuce sama a Dan gajiye.

Tana shiga dakinta handbag dinta da wayarta ta jefar ta nufi toilet tana zare kayan jikinta.

Wanka tayi gajiyanta ya sake sosai ta fito ta zauna tana shafa Mai tana kallan time da aka fara Kiran magrib.
Chapter 66 · 0% Book details