← Book details Shahaab Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 43 OF 71

Sashe 43

Shahaab Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Cikin farinciki mama tace"ikon Allah, ashe tana Jigawan, ninama Rasa Yaya akai kayi dabarar saka mata agogo me d'aukeda na'ura Shahaab,kodan kasaba yin dabara kana kama 6arayin gwamnati shiyasa yanzu ma kayi dabara kakamo 6arauniyar zuciyar ka?"

Cikin sauri ya sunkuyar da Kansa qasa saboda wata irin kunya data kamashi, saida yadan Sosa kansa, sannan ya kalleta yaga ita zuciyarta daya tayi maganar ko ajikinta, ahankali yace"a a mama, ainasan batada waya a hannun ta, nasaka na'urar a jikin agogon ne saboda idan inason ganin ta, zan duba Inga halin datake ciki, banyi hakan da wata manufa ba, Amma Kuma gashi cikin ikon Allah hakan yayi amfani, Bari inkira kakarta inji Yaya ta sauka, dafatan ta'isa lafiya, dazu nakira ta tanata fada, mama bakiji yanda ta rufeni da fada ba, halin ta sak irin na mamanah"(😂)

Cikin dariya mama takai masa duka tace"d'an mutum wasa ne Shahaab? Ai tanada gaskiya, karabu da'ita karka kirata, kabari gobe mushirya mubi jirgi, Sai muje a basu haquri, daga Nan Kuma Sai ayi maganar aurenku, kaga hakan zaifi, suma zasuji dadi Susan cewa sun turo yarsu gidan karamci"

Cikin jin dadi yace"to mama Allah yakaimu, saimu tafi sassafe ko?"

Mama ta kallashi,Shima kallon ta yayi, Sai a lokacin yaga kallon Fassara take masa, cikin sauri yatashi yabar falon Nata cikeda kunya, Sai aikin shafa lallausar sumar Kansa yake.

Mama data bishi da kallo tana ganin fitarsa tasaki murmushi, ta daga hannunta sama tana yiwa Allah godia daya karkato mata hankalin danta yake son aure yanzu, tana fatan ace anayin wannan aure Aisha tasamu ciki ko Allah zaisa itama taga jikokin ta kafin tarasu.

******

Gaba dayansu su ukun atsakiya suka saka Aisha sunajin yanda take basu labari, Abba ya kalleta yace"amma qawar Hajja banda Shirman ki Dan kun samu Sa6ani da uwar Dakin naki saiki niqo irin wannan hanyar kitaho ke kadai? Bakya tsoron asaceki a hanya?"

Ummah tace"hanya Kam babu kyau, yanda ake diban mutane kamar wasu dabbobi,qasar nan anmaida rai ba'a bakin komai ba"

Murmushi tayi tace"wallahi Ummah Ina mata komai,Bana mata rashin kunya saboda tsohuwa ce, yanda kikaga Hajja itama haka take, Amma idan ta rikice saiki Rasa gane kanta, shiyasa Nima nataho gida, dama nagaji,ga sauran kudina ma kuyi amfani dashi Ummah"
Ta qarasa maganar tana bude handbag dinta, duk sauran kudin dake ciki ta fitar dashi ta basu, Hajja ta kalli kudin tace"me sunan qawa wannan kudin ai yayi yawa,duk na menene haka? Ko kudin aikin naki ne?"

Kanta ta Girgiza Tace"A a Hajja,me gidan ne yabani kudin da Kansa, ban roqeshi ba"
Abba ya Jinjina Kansa, Hajja tace"yawwa nikin tuna min ma, dazu wannan saurayin naki ya kirani, Wai sunansa Shahaab, ke yake nema in baki waya idan kina kusa, na qare masa tatas nace idan yasake kirana sainaci masa mutunci, shida yayi silar barinki gida?"
Murmushi tayi tace" Hajja Aida baki masa haka ba"

Kafin Hajja tayi magana Abba yace"har yanzu de baki rabu dashi ba kenan, bamu Isa mu fada miki magana ki saurari maganar mu ba, ai shikkenan Allah yabada sa'a"

Jikin Ummah yayi Sanyi jin furucin Abba, ta kalli Aisha taga yarinyar tanata Fara'ah, Sai can Aishan ta d'ago kanta ta kalli Abba Tace"Abba Bahaka bane, Amma kayi haquri, duk bayanin dazan Maka ba lalle ka ganeba"
Daga Nan bata sake cewa komai ba tafada duniyar tunani
batason taga yanda Abban ta zaiji kunya, Amma data fada masa cewa Shahaab din de dayake qi shine Mahmud Wakili, Shahaab din dayake qi gidansa yasake tura ta aiki, tasan Hajja zata masa wankin Babban Bargo, ahankali tasake cewa "Abba jabir bai fada muku Mahmud Wakili ne ya turashi qasar waje karatu ba? Bai fada Maka shine yatura ka umara ba?"

Cikin tsananin mamaki Abba yace"mahmud Wakili Kuma?"

Hajja tace"jabir bai fada mana koma ba, Amma menene dalilin yimana wannan abun? Keda kike gidansa bai fada miki saboda me yayi mana haka ba?"

Murmushi tayi ta Girgiza, sannan tace" tunda nafada muku yanzu saiku shirya kuje kuyi masa godia, saiya fada muku da dalilin da Kansa"

Hajja tace"tokode daga zuwa yaganki ya qyasa? Fadamin gaskiya"

Hararar Hajja tayi, tatashi tashige Dakin Hajjan tafara shirin wanka, Hajja tatashi tabiyo bayanta taga harta daura zani da alama wanka zata shiga, kallon ta tayi tace"mesunan qawa Habujan Nan ta kar6eki, jikinki yayi wani mulmul kamar matar kansila, kode kaji kikeci ne kullum?"

Cikin dariya tace"kullum sunake ci, abinci Kala Kala Hajja Sai Wanda naza6a, nama kuwa kamar abun banza"

Hajja tace"ikon Allah, kice naman kaji yana Nan kayan qarfi..."

Aisha tayi dariya tace" karfin ne kawai bakida shi Hajja da kinje kema kinci"

Murmushi Hajja tayi ta qaraso Dakin, ita Kuma ta juya tashige wanka.

******

Yau yariga mama futowa falo,tun sassafe yafuto su kansu ma'aikatan sunyi mamakin ganinsa afalo, yad'ora kafa daya Kan daya yana kallo, yayi mutuqar kyau cikin suit, Sai qamshi yake zubawa, Sai wajan karfe takwas mama tafuto, ta shirya cikin less Mai ruwan golden, hannunta da wuyan ta sunsha sarqa da zoben gold, kana ganin ta kasan daula ta zauna, cikin mamaki ta kalleshi Tace"A a, yana ganka anan Kai kadai?"

Cikin sauri ya sunkuyar da Kansa qasa, yadan shafa sumar Kansa yace"mama ai nagama shirya wane"

Murmushi tasaki, ta nemi waje ta zauna tace"tokoma kacire wannan kayan kasako manyan Kaya, haba Mahmud, wajan surukanka zakaje fa ba wajan Aisha ba"

Kansa yadan shafa, sannan yatashi yakoma part dinsu, itama dinning ta nufa tafara cin abinci,don bazata iya wannan azalzalar ta Shahaab ba, Dan idan tabiye masa taga alama abincin ma bazasuci ba.

Tare suka dawo shida Munirat, shadda yasaka fara tareda babbar riga, kayan sunyi Masa kyau sosai fiyeda qananun kayan, Wanda bai saniba tsaf zaiyi tunanin wani sabon angon ne, agogon hannunsa ya daura sannan yaja kujera ya zauna, munirat ma ta zauna tareda gaida mama, cikin kulawa mama tace "Barka munirat"

Abincin suke ci Hankali kwance, mama data gama tana shirin tashi ta kalleshi tace"jirgin karfe nawa zamubi?"

Cikin sauri ya Kalle ta, saida ya ajiye spoon din dayake shan tea sannan yace mata"jirgi bazai tashi ba yau, saboda yanayin hazo, saide mutafi a mota"

Kanta ta Jinjina tace"to ai saimu wuce ko?"

Tissue yadauka ya goge bakinsa, dama kawai yana tura abincin ne, Amma ya matsu sutafi, cikin sauri yace"toshikkenan muje"

Munirat tayi mamakin sa, tafiya zaiyi Amma ko fada mata baiyi ba, batasan meyasa tsakanin jiya zuwa yau, yake share taba, har zata tambayesu Ina zasuje, Sai taga mama ta kalleta tace"to Munirat zamuje jigawa, kinsan yanayin tafiya bamusan Yaya zata Kaya ba, saboda haka kimana addu'ah,idan daga Nan Kuma kinji anyi masa mata acan saiki shirya kar6ar abokiyar zama"

Cikin sauri Shahaab ya kalli mama, baiso ta fadawa munirat zancen auren ba, yasan tanada kishi dole zata daga hankalin ta, shiyasa yaso saiya dawo saiya sanar da'ita ta cikin ruwan Sanyi.

Dam! dam!! dam!!! Gaban munirat yayi wata irin faduwa, hannunta datake cin wainar qwai yad'auki karkarwa har batasan lokacin da fork din yafadi daga hannun taba,ta zubawa mama ido tana kallon ta, mama dataga yanayin munirat ya sauya tace"ikon Allah, menene abun rawar jiki daga maganar kishiya munirat? Dama yamiki alqawari zai zauna dake kadai ne? Banda abinki munirat yanda Shahaab yakeda kyau irin wannan ai kema kinsan dole yanmata zasu so shi,ballantana ma wannan yarinyar kin Riga kinsanta, Aisha ce, idan ya auro tama itade ba baquwa bace awajanki, dama gida daya kuke zaune shikkenan saiku dora daga inda kuka tsaya, may be Rabon muga qananun Yara agidan ne shiyasa Allah yakawo maganar auren, kema ai zakiso ganin yaran Shahaab suna kuka, suna fada, suna Rikici akan sweet..."

Jikin Shahaab yayi Sanyi, yasaki ajiyar zuciya, yaga alama idan bai katse maganar ta mama ba, Tofa bazata dainaba,Wai ahakan ma Dan batasan da case din filayenta da munirat din ta dauke taje ta siyar ba, dama suna yar tsama to idan tasan da batun filayen Allah ne kadai yasan inda rigimar tasu zata qare, ahankali yace"muje mama"
Yajuya ya kalli munirat, fuskarsa babu yabo babu fallasa yace"saimun dawo"

Munirat dai batasan cewa Shahaab yayi mata magana ba, tadaisan yayi magana Amma kwata kwata bata cikin nutsuwar dazata gane meyake fada, wani irin tashin Hankali ne ya wanzu a Saman fuskarta, baqin ciki ya tokare mata maqoshi, suna fita takifa kanta akan dinning table tasaki wani irin kuka maicin rai, dama ashe Aisha baquwar mama zai aura? Kenan ita ya mallakawa company? Ita Mahmud zaiyi wa haka? Dama tasan hakan zai iya faruwa, tunda har uwarsa ta riqe masa yarinyar ya matsa yaji ba'irin na matarsa bane ai dole ya rikice yabibiyi yarinyar. (🙈)
Kuka take me mutuqar cin rai, kwata kwata tunanin ta ya tsaya cak, tarasa Ina zata samu mafita, Amma abinda takeji acikin ranta Gani take dazata samu wuqa Toda tsaf zata Iya da6awa wannan tsohuwar(🙆🏻‍♀️)

Mota biyu sukayi, daya suna ciki ita dashi a zaune abaya, Sai driver dayake jansu, dayar Kuma securities ne aciki saboda tsaro.

Suna hanya yake turawa Ramadan text cewa suntafi jigawa shida mama, Sai tsiya Ramadan yake masa shikuma yana murmushi.

(nabarki da Allah keda kika karanta batareda kin biyaba)
******

Aisha ta kalli Hajja tace"Hajja meyake damunki ne Naga kinyi shiru, ko bakya jin dadi?"

Ajiyar zuciya tayi tace"inafa jin dadi mesunan qawa, gaba daya yau Jina nake jikina Sanyi kalau, tun asuba gabana yake faduwa, bansani ba ko mutuwa zanyi"

Cikin tashin hankali Ummah tace"Hajja Dan Allah Kidena wannan maganar, idan bakida lafiya tashi muje nakai ki chemist din Mubarak dogo"

Cikin sauri Aisha ta kalli Hajja tace" Ko wani abu kike so kici saina siyo miki?"

Ganin yanda duk suka daga hankalin su yasa tad'an kwantar da Hankalinta tace"lafiya ta kalau wallahi, kawai gaba nane yake faduwa"

Ummah tace"to kidinga addu'ah Hajja, insha Allah Sai alkhairi"

Kallan Aisha Hajjan tayi tace"mesunan qawa, dauki kudi aqasan fillo na kije bakin kasuwa ki siyo mana kaji, da nasan da zuwanki jiya Aida tun safe zanje insiyo miki, Amma tunda bansani ba kije yanzu ki siyo mana"

Cikin sauri Ummah tace"Hajja aiga kudin datazo dashi jiya, kusan dubu talatin dawani abu, ta d'auka aciki taje tasiyo"
Chapter 43 · 0% Book details