Sashe 3
Shahaab Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai yamma yayi shirin tafiya gida, yana futowa kuwa mutanan nasa suka take masa baya har zuwa mota, mutum dayane yabude masa mota yashiga, Alokacin har anfara yayyafi kasancewar kudancin qasar sunfi arewacin Nigeria saurin samun ruwan sama, yana shiga motar ya Lumshe Idonsa, ga qamshin ruwan sama me dadi yana busowa cikin motar, yagaji sosai, zaiso ace yasamu anyi masa massage Ayanzu (🤭)
Tafiya Mai Nisa sukayi, kafin su qarasa gida, Alokacin har ruwan yafara qarfi, sojoji ne awajan gidan, dakuma daidai kun Yan sanda, get man nabude musu get, driver ya danna hancin motar zuwa cikin gidan, gida ne babba gari guda, ba zakayi tunanin ma acikin qasar Nan gidan yake ba, acikin harabar gidan ma sojoji ne suke shawagi, motarsa tana tsayawa daga me gadi har sojojin wajansa suka nufa kowa yanayi masa sannu da zuwa, hannunsa yadaga musu kawai,kasancewar Ana Dan ruwa yasa yayi sauri Kai tsaye yawuce part din MAMA.
Yana shigowa falon yafara cire jacket dinsa, tareda necktie din wuyansa, duk da girman falon Nata, wani kafet ne Mai masifar laushi yake malale a falon, ga wata katuwar plasma tana aiki, daga fentin falon har kujerun da labulaye duka milk colour ne, wata tsohuwa ce mai kimanin shekaru sittin da shida a zaune, saikuma wata yarinya a tsugunne a gabanta, tana matsa mata qafafu
Cikin fad'a-fad'a tadubi yarinyar "ke! Kidena matsa min qafa da qarfi mana kamar kinsamu wani dutsi, nagaji dayin complain a kanki, Nan gaba kad'an zan'iya sallamar ki idan baki gyara halinki ba"
Cikin ladabi tace "kiyi hakuri Hajiya"
Cikin muryarsa Mai cikeda miskilanci yace "mama"
Kallan sa tayi tace "SHAHAAB kadawo?"
Bai bata amsa ba saida ya zauna yana fadin "wash! Allah na mama nagaji"
Yarinyar datake matsawa wadda aka kira da mama qafafu, cikin tsantsar ladabi kanta asunkuye, batare data hada ido dashi ba tace "yalla6ai barka da dawowa"
Bece da'ita uffan ba, Sai mama ce data watsa mata wani irin kallo tace "saiki tashi kije, zan gana da Dana"
Cikin sauri yarinyar tatashi tabar wajan har qafafunta na hardewa
Kallan sa tayi tace "Shahaab ya aikin? Kadawo lafiya?"
Kafin yabata amsa agogon hannunsa ya nuna alamun Ana kiransa, ta6a agogon yayi ya amsa Kiran dake shigowa, daga dayan bangaren muryar wani mutum ne yake tashi "ranka yadade kanada baqi daga bayelsa"
Dafe Kansa yayi, kwata kwata ya manta da Zuwansu, ahankali ya kalli mama, shide yasan be'isa yasake fita yanzu ba, cikin muryarsa Mai dadi yace "kafada musu muhadu dasu gobe misalin karfe goma nasafe" daga Nan yakashe wayar, ya maida dubansa zuwaga mama
Hankalin tane taji ya kwanta Bayan taji bazai sake fitaba, taqi jinin ta ganshi nesa da'ita
Tafison kullum ta kasance tareda dannata qwaya daya tal a duniya, batason yawan rashin zamansa agida ko kad'an, cikin kulawa yace "waye yata6aki mama? Keda waye?"
Ajiyar zuciya ta sauke tace "ai kasan damuwa ta, rashin dawowarka ne gida dawuri, saikuma batun qawata Aysha Sulaiman bompai, dakamin alqwari zaka nemomin ita"
Kansa ya sunkuyar qasa, wannan qawa ta mama! Wannan qawa ta mama!! Da yanada halin dazai mantar da'ita wannan qawar Tata datuni yayi, saboda babu Wanda yasani tana Raye har yanzu kokuma ta mutu, ahankali ya d'ago Kansa ya kalleta, yakama hannayenta yariqe yace "za'a duba agani"
Shiru mama tayi tana Kallan sa, tarasa meyasa Shahab baison maganar qawarta, tun lokacin data fada masa inde taga qawarta Aysha to zata hadashi aure da 'yarta idan mace ta Haifa, tun daga lokacin yaqi jinin tayi masa maganar qawar Tata, saboda bashida ra'ayin yin wani aure yanzu, idan ba bayason Nemo mata qawar Tata ba yaushe zata yi masa maganar amma yace Wai za'a duba, hakan yana nufin Bama shine zai dubaba kenan, ko meyasa yake gudun yin wani auren? Kokuma baida cikakkiyar lafiya irinta maza oho masa, rashin haihuwar sa yana damunta, ga Kuma rashin qawarta wadda take Fata, take Kuma burin tahadu da'ita kafin Takoma ga mahaliccinta, wadannan burikan Nata guda biyu su take Fata su kasance, yau ace taga jinin Shahaab, sannan Kuma taga qawarta Aysha Sulaiman
Ajiyar zuciya ta sauke tace "Yaya labarin Munirat? Har yanzu haihuwa shiru babu ciki bare ayi tunanin labarin haihuwa ko?"
"Ana Addu'ah de"
Shine abinda yafada mata
Kallan sa tayi dakyau Kai tsaye tace "inaso kafin namutu, Inga qawata Aysha, sannan Kuma Inga yayanka, Qawata Aysha de Ina Nan Ina nemanta, Kuma nasan insha Allah watarana zan ganta, Amma Kai haihuwa bakada tabbas,matarka ba haihuwa zatayi ba, yakamata kayiwa kanka fada, saboda haka yaushe zaka sake aure? "
Gabansa ne yafadi,cikin sauri ya d'ago Kansa ya kalleta, Dan qaramin bakinsa ya bude kamar Mai shirin cewa wani abu, Amma Kuma yakasa magana, ganin yazuba mata ido yana Kallan ta yasa taci gaba da fadin "yakamata kabi shawara ta, ka 6oye kanka kanemi aure, kafuto a matsayin SHAHAAB kanemi aure da soyaiyar tsakani da Allah bata kudi ba, muddin kace zakaje wajan yanmata a matsayin MAHMUD WAKILI,to bazaka ta6a samun soyaiyar gaskiya ba"
Tamkar Wanda zai Fashe da Kuka yace "mama itama Munirat din tana sona, nida ita ai sai Allah mama"
Batace dashi komai ba saboda taqaici kawai wayarta ta d'auka dake Gefe, tawuce dakinta tabarshi anan, hakan yana nufin shiru ma amsa ce game Hankali.
Yana ganin shigewarta daki yaji kamar ya kurma ihu kozaiji dadi, tayaya mama zatace yayi aure Bayan irin dunbin soyaiyar Da Munirat take nuna masa?
Jikinsa a sanyaye yamiqe yanufi part dinsu, duk ruwan dayake sauka akansa ko kad'an baya jinsa, yasan cewa idan yabi Bayan mama ma to bazata saurare Shiba, yana zuwa falon ya hangota gaban TV da remote a hannunta, Riga da siket ne ajikinta dinkin ya zauna Das ajikinta,munirat chocolate beauty ce, Amma hutu, dakuma jin dadin datake samu, da shafa mayuka masu mutuqar tsada yasa gaba daya bazaka ce mata chocolate ba, fatarta tayi wani irin luwai luwai kamar ka latsa jini yafuto, mace ce har mace, Mai aji dakuma wadatar ilmin boko,Daurin ture kaga tsiya tayi, hakan yabawa gashin dokin data saka damar futowa sosai Kai kace halalinta ne, falon bashida wani tarkace, kujerun falon Kala biyu ne, akwai yellow, dakuma ash colour, Sai aka hadasu akayiwa falon qawanya dasu
Tsayawa yayi yana qare mata kallo, haqiqa yana qaunar munirat, Kuma itama ya tabbatar tana mutuqar sonsa, babu abinda ta rageshi dashi, sannan tana mutuqar qoqarinta wajan ganin ta kyautata wa mama, Amma mama bata Gani
Jin alamun kamar Ana kallon ta ne yasa tajuya, tana ganinsa tatafi dawani irin taku me daukar hankali, ta qarasa wajan sa
"barka da zuwa my Dear"
Cikin damuwa ya Lumshe Idonsa ya bude, alamun amsawa, murdaddan dantsan hannunsa ta kama tace "muje kayi wanka, meyake damunka ne Naga kamar kana cikin damuwa, gashi katsaya ruwa ya ta6amin kai"
Ta qarasa maganar tana janshi ciki, ahankali ya janye jikinsa yace "kije kiyi kallonki, yaude na hutar dake, idan nagama zan futo"
Murmushi tasaki, ta rungume shi tasakar masa kiss a kumatu, sannan tasake shi tajuya, saqon Nata yashige shi sosai, har saida hakan yasa shi Lumshe Idonsa, batare daya shirya ba
Washegari da safe bai tashi dawuri ba, sakamakon gajiyar da yayi cikin dare,tun kafin yatashi daga baccin munirat ta silale tatafi part din mama,yau tana so tayi wa mijin ta girki Wanda zaisa yaji dadi sosai kamar yanda yajiyar da'ita dadi adaren yau, ma'aikatan part din ta had'a gaba d'ayansu tasakasu su girka mata irin abunda takeso, cikin qanqanin lokaci suka kammala komai suka jereshi a Babban dinning din na mama, Wanda aqalla zai dauki mutane samada mutum takwas
Har zuwa lokacin Hajiya Mama Ana daki bata futo ba, munirat kuwa zama tayi akan kujera ta sallami masu aikin, wayarta ta d'auka tana chatting da qawayenta, dayawansu tallar magungunan mata suke mata, Wanda ita kanta batasan Dame aka hadasu ba
"menake Gani haka?!!!"
Mama data futo daga daki tafada, Bayan taga abinda aka ajiye a dinning, ta qarasa maganar idonta nakan munirat, fuskarta kuwa shimfide take da 6acin rai
Cikin sauri munirat ta kalleta, gabanta yafadi, da sauri ta sakko daga kan kujerarar ta tsugunna har wayar hannunta na faduwa, cikin ladabi da rawar murya tace "Barka da futowa mama, Ina kwana?"
"daban kwana ba kya ganni? Munirat yaushe Ina cikin gidannan har Zaki shigo min part dina kina bada umarni? Kinyi hauka ne?"
Adede lokacin yashigo part din, yashirya cikin suit kamar kowacce rana
Munirat da idonta yakawo ruwa, qwalla tataru tacika idon, ta girgiza kanta batare da tayi magana ba
Nunata mama tayi da d'an yatsa, tace"maza maza tashi kije tas ki cinye abinda kikasa aka girka, tun kafin ranki Dana iyayenki ya6aci.... "
Cikin sauri ya qaraso falon, cikin ladabi yace"mama kiyi hakuri Dan Allah"
Kallan sa tayi tace "Alhamdulillah... Gara da Allah yakawo ka"
Ta nuna masa munirat da hawaye ya wanke mata fuska tace "tun kafin namutu matarka ce mebada umarni...., to gatanan kasaketa"
Jiyayi kamar mama ta doka masa guduma a qirjinsa, munirat kuwa tanajin wannan furucin, tafice daga falon da gudu tana kuka.
LABARINSU:
Hajiya Mama, sunanta Aysha Yakubu Sagagi, tun Bayan rabuwar su da qawarta Aysha Sulaiman bompai Sai iyayenta suka rasu, daga Nan mijinta ya dauke ta suka tafi Nijar wajan dangin sa, sun dade acan yana kasuwancin sa, daga Nan suka sake dawowa Nigeria, ahankali ahankali har Allah yasa Arziqinsa yasake ha6aka, Bai Barta tayi maraicin iyayenta ba, janta yayi ajiki, ya dinga Koya mata harkokin kasuwancin sa, ahankali harta gane komai, lokaci zuwa lokaci yana tura ta wasu qasashen sarin kayaiyaki, har Allah yasa Shima yabude kamfanoni dadama, anan Nigeria da Kuma Nijar inda danginsa suke
Lokaci daya, sunansa yafuto acikin jerin sunayen masu kudin qasar Dama Africa baki daya, akwai wata Rana daya shirya zaije yataho da danginsa na Nijar, su dawo Abuja da zama gaba daya, yaje yataho dasu a hanyar su ta dawowa jirginsu yayi hatsari suka mutu gaba dayansu.
Tafiya Mai Nisa sukayi, kafin su qarasa gida, Alokacin har ruwan yafara qarfi, sojoji ne awajan gidan, dakuma daidai kun Yan sanda, get man nabude musu get, driver ya danna hancin motar zuwa cikin gidan, gida ne babba gari guda, ba zakayi tunanin ma acikin qasar Nan gidan yake ba, acikin harabar gidan ma sojoji ne suke shawagi, motarsa tana tsayawa daga me gadi har sojojin wajansa suka nufa kowa yanayi masa sannu da zuwa, hannunsa yadaga musu kawai,kasancewar Ana Dan ruwa yasa yayi sauri Kai tsaye yawuce part din MAMA.
Yana shigowa falon yafara cire jacket dinsa, tareda necktie din wuyansa, duk da girman falon Nata, wani kafet ne Mai masifar laushi yake malale a falon, ga wata katuwar plasma tana aiki, daga fentin falon har kujerun da labulaye duka milk colour ne, wata tsohuwa ce mai kimanin shekaru sittin da shida a zaune, saikuma wata yarinya a tsugunne a gabanta, tana matsa mata qafafu
Cikin fad'a-fad'a tadubi yarinyar "ke! Kidena matsa min qafa da qarfi mana kamar kinsamu wani dutsi, nagaji dayin complain a kanki, Nan gaba kad'an zan'iya sallamar ki idan baki gyara halinki ba"
Cikin ladabi tace "kiyi hakuri Hajiya"
Cikin muryarsa Mai cikeda miskilanci yace "mama"
Kallan sa tayi tace "SHAHAAB kadawo?"
Bai bata amsa ba saida ya zauna yana fadin "wash! Allah na mama nagaji"
Yarinyar datake matsawa wadda aka kira da mama qafafu, cikin tsantsar ladabi kanta asunkuye, batare data hada ido dashi ba tace "yalla6ai barka da dawowa"
Bece da'ita uffan ba, Sai mama ce data watsa mata wani irin kallo tace "saiki tashi kije, zan gana da Dana"
Cikin sauri yarinyar tatashi tabar wajan har qafafunta na hardewa
Kallan sa tayi tace "Shahaab ya aikin? Kadawo lafiya?"
Kafin yabata amsa agogon hannunsa ya nuna alamun Ana kiransa, ta6a agogon yayi ya amsa Kiran dake shigowa, daga dayan bangaren muryar wani mutum ne yake tashi "ranka yadade kanada baqi daga bayelsa"
Dafe Kansa yayi, kwata kwata ya manta da Zuwansu, ahankali ya kalli mama, shide yasan be'isa yasake fita yanzu ba, cikin muryarsa Mai dadi yace "kafada musu muhadu dasu gobe misalin karfe goma nasafe" daga Nan yakashe wayar, ya maida dubansa zuwaga mama
Hankalin tane taji ya kwanta Bayan taji bazai sake fitaba, taqi jinin ta ganshi nesa da'ita
Tafison kullum ta kasance tareda dannata qwaya daya tal a duniya, batason yawan rashin zamansa agida ko kad'an, cikin kulawa yace "waye yata6aki mama? Keda waye?"
Ajiyar zuciya ta sauke tace "ai kasan damuwa ta, rashin dawowarka ne gida dawuri, saikuma batun qawata Aysha Sulaiman bompai, dakamin alqwari zaka nemomin ita"
Kansa ya sunkuyar qasa, wannan qawa ta mama! Wannan qawa ta mama!! Da yanada halin dazai mantar da'ita wannan qawar Tata datuni yayi, saboda babu Wanda yasani tana Raye har yanzu kokuma ta mutu, ahankali ya d'ago Kansa ya kalleta, yakama hannayenta yariqe yace "za'a duba agani"
Shiru mama tayi tana Kallan sa, tarasa meyasa Shahab baison maganar qawarta, tun lokacin data fada masa inde taga qawarta Aysha to zata hadashi aure da 'yarta idan mace ta Haifa, tun daga lokacin yaqi jinin tayi masa maganar qawar Tata, saboda bashida ra'ayin yin wani aure yanzu, idan ba bayason Nemo mata qawar Tata ba yaushe zata yi masa maganar amma yace Wai za'a duba, hakan yana nufin Bama shine zai dubaba kenan, ko meyasa yake gudun yin wani auren? Kokuma baida cikakkiyar lafiya irinta maza oho masa, rashin haihuwar sa yana damunta, ga Kuma rashin qawarta wadda take Fata, take Kuma burin tahadu da'ita kafin Takoma ga mahaliccinta, wadannan burikan Nata guda biyu su take Fata su kasance, yau ace taga jinin Shahaab, sannan Kuma taga qawarta Aysha Sulaiman
Ajiyar zuciya ta sauke tace "Yaya labarin Munirat? Har yanzu haihuwa shiru babu ciki bare ayi tunanin labarin haihuwa ko?"
"Ana Addu'ah de"
Shine abinda yafada mata
Kallan sa tayi dakyau Kai tsaye tace "inaso kafin namutu, Inga qawata Aysha, sannan Kuma Inga yayanka, Qawata Aysha de Ina Nan Ina nemanta, Kuma nasan insha Allah watarana zan ganta, Amma Kai haihuwa bakada tabbas,matarka ba haihuwa zatayi ba, yakamata kayiwa kanka fada, saboda haka yaushe zaka sake aure? "
Gabansa ne yafadi,cikin sauri ya d'ago Kansa ya kalleta, Dan qaramin bakinsa ya bude kamar Mai shirin cewa wani abu, Amma Kuma yakasa magana, ganin yazuba mata ido yana Kallan ta yasa taci gaba da fadin "yakamata kabi shawara ta, ka 6oye kanka kanemi aure, kafuto a matsayin SHAHAAB kanemi aure da soyaiyar tsakani da Allah bata kudi ba, muddin kace zakaje wajan yanmata a matsayin MAHMUD WAKILI,to bazaka ta6a samun soyaiyar gaskiya ba"
Tamkar Wanda zai Fashe da Kuka yace "mama itama Munirat din tana sona, nida ita ai sai Allah mama"
Batace dashi komai ba saboda taqaici kawai wayarta ta d'auka dake Gefe, tawuce dakinta tabarshi anan, hakan yana nufin shiru ma amsa ce game Hankali.
Yana ganin shigewarta daki yaji kamar ya kurma ihu kozaiji dadi, tayaya mama zatace yayi aure Bayan irin dunbin soyaiyar Da Munirat take nuna masa?
Jikinsa a sanyaye yamiqe yanufi part dinsu, duk ruwan dayake sauka akansa ko kad'an baya jinsa, yasan cewa idan yabi Bayan mama ma to bazata saurare Shiba, yana zuwa falon ya hangota gaban TV da remote a hannunta, Riga da siket ne ajikinta dinkin ya zauna Das ajikinta,munirat chocolate beauty ce, Amma hutu, dakuma jin dadin datake samu, da shafa mayuka masu mutuqar tsada yasa gaba daya bazaka ce mata chocolate ba, fatarta tayi wani irin luwai luwai kamar ka latsa jini yafuto, mace ce har mace, Mai aji dakuma wadatar ilmin boko,Daurin ture kaga tsiya tayi, hakan yabawa gashin dokin data saka damar futowa sosai Kai kace halalinta ne, falon bashida wani tarkace, kujerun falon Kala biyu ne, akwai yellow, dakuma ash colour, Sai aka hadasu akayiwa falon qawanya dasu
Tsayawa yayi yana qare mata kallo, haqiqa yana qaunar munirat, Kuma itama ya tabbatar tana mutuqar sonsa, babu abinda ta rageshi dashi, sannan tana mutuqar qoqarinta wajan ganin ta kyautata wa mama, Amma mama bata Gani
Jin alamun kamar Ana kallon ta ne yasa tajuya, tana ganinsa tatafi dawani irin taku me daukar hankali, ta qarasa wajan sa
"barka da zuwa my Dear"
Cikin damuwa ya Lumshe Idonsa ya bude, alamun amsawa, murdaddan dantsan hannunsa ta kama tace "muje kayi wanka, meyake damunka ne Naga kamar kana cikin damuwa, gashi katsaya ruwa ya ta6amin kai"
Ta qarasa maganar tana janshi ciki, ahankali ya janye jikinsa yace "kije kiyi kallonki, yaude na hutar dake, idan nagama zan futo"
Murmushi tasaki, ta rungume shi tasakar masa kiss a kumatu, sannan tasake shi tajuya, saqon Nata yashige shi sosai, har saida hakan yasa shi Lumshe Idonsa, batare daya shirya ba
Washegari da safe bai tashi dawuri ba, sakamakon gajiyar da yayi cikin dare,tun kafin yatashi daga baccin munirat ta silale tatafi part din mama,yau tana so tayi wa mijin ta girki Wanda zaisa yaji dadi sosai kamar yanda yajiyar da'ita dadi adaren yau, ma'aikatan part din ta had'a gaba d'ayansu tasakasu su girka mata irin abunda takeso, cikin qanqanin lokaci suka kammala komai suka jereshi a Babban dinning din na mama, Wanda aqalla zai dauki mutane samada mutum takwas
Har zuwa lokacin Hajiya Mama Ana daki bata futo ba, munirat kuwa zama tayi akan kujera ta sallami masu aikin, wayarta ta d'auka tana chatting da qawayenta, dayawansu tallar magungunan mata suke mata, Wanda ita kanta batasan Dame aka hadasu ba
"menake Gani haka?!!!"
Mama data futo daga daki tafada, Bayan taga abinda aka ajiye a dinning, ta qarasa maganar idonta nakan munirat, fuskarta kuwa shimfide take da 6acin rai
Cikin sauri munirat ta kalleta, gabanta yafadi, da sauri ta sakko daga kan kujerarar ta tsugunna har wayar hannunta na faduwa, cikin ladabi da rawar murya tace "Barka da futowa mama, Ina kwana?"
"daban kwana ba kya ganni? Munirat yaushe Ina cikin gidannan har Zaki shigo min part dina kina bada umarni? Kinyi hauka ne?"
Adede lokacin yashigo part din, yashirya cikin suit kamar kowacce rana
Munirat da idonta yakawo ruwa, qwalla tataru tacika idon, ta girgiza kanta batare da tayi magana ba
Nunata mama tayi da d'an yatsa, tace"maza maza tashi kije tas ki cinye abinda kikasa aka girka, tun kafin ranki Dana iyayenki ya6aci.... "
Cikin sauri ya qaraso falon, cikin ladabi yace"mama kiyi hakuri Dan Allah"
Kallan sa tayi tace "Alhamdulillah... Gara da Allah yakawo ka"
Ta nuna masa munirat da hawaye ya wanke mata fuska tace "tun kafin namutu matarka ce mebada umarni...., to gatanan kasaketa"
Jiyayi kamar mama ta doka masa guduma a qirjinsa, munirat kuwa tanajin wannan furucin, tafice daga falon da gudu tana kuka.
LABARINSU:
Hajiya Mama, sunanta Aysha Yakubu Sagagi, tun Bayan rabuwar su da qawarta Aysha Sulaiman bompai Sai iyayenta suka rasu, daga Nan mijinta ya dauke ta suka tafi Nijar wajan dangin sa, sun dade acan yana kasuwancin sa, daga Nan suka sake dawowa Nigeria, ahankali ahankali har Allah yasa Arziqinsa yasake ha6aka, Bai Barta tayi maraicin iyayenta ba, janta yayi ajiki, ya dinga Koya mata harkokin kasuwancin sa, ahankali harta gane komai, lokaci zuwa lokaci yana tura ta wasu qasashen sarin kayaiyaki, har Allah yasa Shima yabude kamfanoni dadama, anan Nigeria da Kuma Nijar inda danginsa suke
Lokaci daya, sunansa yafuto acikin jerin sunayen masu kudin qasar Dama Africa baki daya, akwai wata Rana daya shirya zaije yataho da danginsa na Nijar, su dawo Abuja da zama gaba daya, yaje yataho dasu a hanyar su ta dawowa jirginsu yayi hatsari suka mutu gaba dayansu.