Sashe 28
Shahaab Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abba yasa hannu yad'auki wayar hajja dake ajiye agefe, number Walida yadubo yakira Walida yasa ta a amsa kuwwa yanda kowa zaiji abinda take fada, Walida tana daukan waya Abba yace "Walida mamuda ne"
Cikin ladabi ta gaishe shi, Shima ya amsa mata, sannan yayi mata ta manya yace "meyasa bazaki yiwa qawar ki fada bane ta dinga zuwa gidanku da rana, Amma kullum saide tazo da daddare, mu kinga munyi mata fada, taqi jin maganar mu"
Walida bata gane shan cikinta Abba yake ba, tayi murmushi tace "Abba da daddare Kuma? Ai Aisha bata zuwa da daddare, sau daya tata6a zuwa wajena da daddare Kuma Shima narakota har gida, ka tambayi su Hajja zasu fadama ma nazo gidan"
Abba yace "eh anyi haka fa, na manta wallahi, toki gaida mutanan gidan" daga Nan yakashe waya.
Kukan Aisha ne yake tashi awajan, sosai take kuka harda Jan zuciya. Abba ya kalleta yace "muna jinki, wajan wa kike zuwa?"
Cikin kuka tace "SHAHAAB"
Hajja tanajin haka tafara tafa hannu,Nan da Nan hawaye yafara sauka akan kumatunta, cikin mamaki tace "mesunan qawa?,to kode shine yabaki ribbon din Dana Gani a kanki kikace Walida ce tabaki?"
Babu musu ta daga kanta alamun hakane,
Cikin 6acin rai Abba yatashi ya wanketa da Mari yace "waye SHAHAAB?"
Zafin Marin ne yasa tasaka hannu ta dafe kuncinta, muryarta na rawa cikin kuka tace "shi.... Shin.. Shine yake zuwa yake kirana awaya Sai naje, Abba Allah Ina sonsa nide"
Wani Marin Abba yasake mata, cikin 6acin rai da takaici yace "shine kike binsa har cikin mota yana hure miki kunne ko? Ai kinsan da maganar inusa, wato irin mayaudaran samarin Nan ne yake zuwa wajan ki yana hure miki kunne harni Zaki kalla kina cewa ke kina sonsa ko? Idan na qara ji kince kina sonsa saina kakkarya ki a gidannan, Kuma daga yau babu ke babu shi,inusan damuka Sani shi zamu baki"
Cikin kuka tace "Allah banason inusa, nide Shahaab nakeso"
Jin abinda tace yasa Abba yayo kanta zai rufe ta da duka, cikin sauri Hajja tajanyota jikinta,
Hawaye ne suka sulalo daga idanun Ummah,koma waye wannan Shahaab haqiqa yariga yagama hurewa yarsu kunne, tunda gashi har mahaifin ta yana fada itama tana fada.
Hajja tasaka salati tana sake rushewa da Kuka, cikin kukan tace "wannan masifa Dame tayi kama? Mesunan qawa Ina kika samo wani Shahaab Kuma? Yaushe Zaki bi saurayi har cikin mota? Kifadamin su waye iyayensa inje inji Dame suke taqama da dansu zaizo wajanki batareda ubanki yasani ba?"
Cikin kuka tace "Hajja ni bansan iyayensa ba, Kuma nide Allah Shahaab nakeso"
Hajja tace "to inajin de aljani ne, Danni banta6a jin irin wannan sunan ba, saide a jinsin aljannu, ninasan ba zakiyi haka da niyya ba mesunan qawa, Gamo kikai da aljan"
Abba yace "babu wani aljani Hajja, Sai iskanci dayake damunta, Kuma ni bazata 6atamin suna ba, bazata janyomin abun kunya agida ba...."
Jin furucin Abba yasa Hajja tasake rushewa da Kuka tace"mummunan bakinka ba'a kan mesunan qawa ba, inda zatayi ciki da tuni tayi, jinake can unguwar gabar Yara suna Nan sunkai su talatin kowacce cikin shege ne da'ita, ita kanta Malamar asbitin dasuke zuwa wajanta take zubar musu cikin itama cikin shegen ne da'ita, Bayan Wanda ta haife, Amma ninasan Mesunan qawa inde tabiyo halin takwararta to ba zatayi cikin shege ba"
Ummah ta kalli Hajja da sauri, yaushe akayi ciki agarin har mutum talatin? (😂🤔)
Tagama lura cewa soyaiyar Aisha tasa kwata kwata Hajja bata ganin laifin yarinyar,ko kadan bazata iya tsawatar mata ba,Abba yace "tunda kince kina sonsa, tona tabbatar kona miki katangar qarfe tsakanin keda shi watarana bazan San lokacin dazaki tsallake kije wajan sa ba, danhaka ki shirya, zanje in samu jummai infada mata ta shirya takaiki can kano, daga Nan kuwuce Abuja akai ki gidan Mahmud Wakili aiki, tunda da naji tausayin ki nace ba zakije ba Gara ki zauna agaban mu abaki inusa, to yanzu Gara kije, dade ki zauna agari kina satar fita kina shiga motar saurayi bansan meyake miki ba, Gara kije can kikama aiki"
Yana fadin haka yafice daga gidan, Bai Zame ko'inaba Sai gidan Jummai qawar Hajja.
Aisha kuwa kuka tasa harda burburwa a jikin Hajja, "Hajja ki masa magana, Allah ni bazanje ko'inaba,Ina ruwana da wani Mahmud Wakili da zanje gidansa aiki, Kuma arasa gidan Wanda zanje aiki Sai wani Mahmud Wakili?, aini ba baiwar sa bace...."
Hajja ta share Hawayen idonta ta kama hannunta zasu shige daki, Aisha ta qwace hannunta taci gaba da kuka, Ummah tatashi ta wuce daki, domin kuwa ita hukuncin da mamuda ya yanke yayi mata daidai,babu Wanda zai nuna mata son Aisha kaf duniyar, Amma hakan ba zaisa taqi Bawa mijinta goyon baya akan tarbiyar yarinyar ba.
Jabir ne ya matso wajan ta yad'ora hannunsa akan dogon gashinta daya barbaje saboda kukan datasha, kannata yake shafawa tareda bubbuga bayanta alamun tayi hakuri, Shima kukan yake bashida bakin dazai iya lallashin yayar tasa, tana jinsa tafada jikinsa sukaci gaba da kukan gaba daya.
Awannna rana wuni sukai gidan babu dadi, Aisha banda Jan zuciya babu abinda take, abinci ma taqi Ci, Sai sharar hawaye take, Hajja tabata haquri harta gaji, ta qanqame wayar Hajja tana ta gwada Kiran Shahaab Amma abun baqin ciki waya taqi shiga, har dare Aisha tana daki taqi futowa waje, tana jiyo Abba yana shaida musu gobe jummai zatazo ta dauketa su tafi, jin babu Wanda yayi masa magana akan hukuncin nasa yasa wani sabon hawaye ya silalo daga idonta, baqin ciki yataru yazame mata goma da Ashirin, har gara ace wani gidan zataje aiki akan de taje gidan Mahmud Wakili,mutumin da kullum burinsa shine kamawa talakawa kayansu da kudaden su shine abinda ya'iya? Banda gidan man malam Audu daya saki bata ta6ajin inda akace yasaki gidan man wani ba, wayar Hajja tasake d'auka tafara Kiran layin Shahaab, saida ta kirashi yakai Sau goma,saide amsar guda daya ce, shine wayarsa akashe take.
Haka kowa yayi bacci Amma idon Aisha biyu, mutumin da taqi jininsa, Wai itace zataje gidansa aiki, Shahaab ne kawai zai fiddata daga wannan qulli, shikuma baya Nan, shin yasan Biron Dama haka kudinsa yake? Shine yasiyo mata da Kansa? Ko wanine yabashi? Shida yake Yaron Mahmud Wakili yaushe har zai samu wannan uban kudin? Anya ma kuwa yasan wanne irin Biro yabata? Haka ta dinga tunani tana yiwa kanta tambaya Wanda babu me amsa mata su Sai Shahaab, shikuma yamata Nisa.
Tana cikin wannan hali batasan yaushe bacci ya dauketa ba, washe gari haka ta zauna adaki taqi futowa, abinci ma qinci tayi, tun hajja tana lallashinta harta gaji taqyaleta, wajan qarfe goma Sha daya Abba yashigo tareda jummai, yana zuwa yacewa Ummah "kira mata Wannan yarinyar zasu tafi yanzu"
Cikin sauri Hajja tace"innalillahi wa inna ilaihirraji'un.... Yanzu mamuda da gaske kake ashe,? Yanzu rabani zakayi da me sunan qawa,?to babu inda yarinyar Nan zataje "
Cikin nutsuwa yace" Hajja, tafiyar ta shine yafi alkhairi, zamanta anan bansan wacce irin magana zata Dauko min ba"
yana fadar haka yashige Dakin Hajja yakamo hannun Aisha suka futo, kuka take tana Kiran Hajja, Hajja ta kama hannunta ta riqe itama tana kuka, daqyar Abba ya fizgeta suka fita waje, wata yar qaramar mota ce a kofar gidan, cikin motar yasaka ta, sannan jummai tashiga, shikuma yarufe musu motar, yasunkuyo da Kansa ta window yace "idan kunje kano, Akira hajiyar a tambayeta aji koda tasamu yar aikin to asake tura mata Aishan ko bude get ne ta dinga yi musu, zamanta acan din Hankali na zaifi kwanciya, nasan babu ita babu haduwa da wannan Yaron dayake hure mata kunne"
Aisha tana jinsa saide ko d'ago kanta batayi ta kalleshi ba, kanta na cikin qafafunta tana kuka.
Jummai tace "karka damu mamuda, nasan ma za'a dace insha Allah, bazan dawo gida Bama Sai an tabbatar min sunje Abujan lafiya, kayi mata addu'ah"
Cikin sanyin jiki yayi murmushin qarfin Hali, tareda barin jikin motar yana juyawa gida, shi Kansa bazai so yarsa mace qwaya daya jal tayi nesa dashi ba, Sai dole, yana tare da'ita gida daya bai ta6a sanin akwai Wanda yake zuwa yana Kiran yarsa ba, zancen ma yawuce kofar gida agaban jama'ah saide a mota, Allah ne kadai yasan abinda zai faru inba Allah ne yakiyaye ba, juyawa yayi ya kalli motar yayinda suka fara tafiya, cikin ransa yana Binta da kyakkyawar addu'ah, Idonsa nakan motar har suka yi Nisa yadena hangosu.
Da alama Jummai ta shirya yin futo na futo tsakanin ta da Hajja😎😎
to, takwara tatafi wajan takwararta🙄, rashin kunya tatafi wajan masifa da iko🥹🥹
Wannan shi ake kira, angudu ba'a tsiraba 💁🏻♀️mahaifi yatura 'yarsa inda yake gudu 😇
Menene zai kasance Idan Shahaab ya dawo yaga Aisha acikin gidansa?🤔
Yaya makomar qaryaiyakin daya dinga shuka mata?🤔
(SHAHAAB littafin kudi ne, idan kika karanta min batareda kin biya ba, nabarki keda mahaliccinki,nera 300 Ne kacal bansaka kudi me yawa ba
0164549488
Amina muhammad
GTbank
My number
08033300034
Mutara zuwa gobe 🙏🏻
Amnah El Yaqoub✍🏻
Salam Alaikum,masu fitar min da littafi nagode, masu karanta wa batareda sisinsu ba nabarku kuda ALLAH,nide ban yafe muku ba, bazan yafe ba Kuma har abada, nabarku da futowar rana da faduwarta.
Masu cewa indinga yin posting biyu a rana kuyi haquri gaskiya bazan iyaba, Alokacin danace zan dinga yin posting biyu a rana, nayi tunanin yin VIP group 500, shine nace zan dinga yin posting biyu, to yanzu 300 dinma wasu suna cewa ta musu tsada,shiyasa nafasa yin VIP din, maganar posting biyu ta rushe, duk page guda daya, Ina bata awa hudu ne akansa, awa uku typing, awa daya editing, tayaya zan dinga bata awa takwas a rana inyi page guda biyu? Ayyukan gidan Ina zan kaisu? Masu min magana ta private inyi Yaya dasu? Masu kirana inyi Yaya dasu? Gaskiya kuyi haquri, kullum zamu dinga posting daya, idan Allah yasa nasamu lokaci zakuga posting biyu, idan bansamu ba zakuga daya, duk lokacin dakuka ga guda daya please 🙏🏻kuce Allah yayi masa Albarka Faqad👌🏻.
Page 22
Cikin ladabi ta gaishe shi, Shima ya amsa mata, sannan yayi mata ta manya yace "meyasa bazaki yiwa qawar ki fada bane ta dinga zuwa gidanku da rana, Amma kullum saide tazo da daddare, mu kinga munyi mata fada, taqi jin maganar mu"
Walida bata gane shan cikinta Abba yake ba, tayi murmushi tace "Abba da daddare Kuma? Ai Aisha bata zuwa da daddare, sau daya tata6a zuwa wajena da daddare Kuma Shima narakota har gida, ka tambayi su Hajja zasu fadama ma nazo gidan"
Abba yace "eh anyi haka fa, na manta wallahi, toki gaida mutanan gidan" daga Nan yakashe waya.
Kukan Aisha ne yake tashi awajan, sosai take kuka harda Jan zuciya. Abba ya kalleta yace "muna jinki, wajan wa kike zuwa?"
Cikin kuka tace "SHAHAAB"
Hajja tanajin haka tafara tafa hannu,Nan da Nan hawaye yafara sauka akan kumatunta, cikin mamaki tace "mesunan qawa?,to kode shine yabaki ribbon din Dana Gani a kanki kikace Walida ce tabaki?"
Babu musu ta daga kanta alamun hakane,
Cikin 6acin rai Abba yatashi ya wanketa da Mari yace "waye SHAHAAB?"
Zafin Marin ne yasa tasaka hannu ta dafe kuncinta, muryarta na rawa cikin kuka tace "shi.... Shin.. Shine yake zuwa yake kirana awaya Sai naje, Abba Allah Ina sonsa nide"
Wani Marin Abba yasake mata, cikin 6acin rai da takaici yace "shine kike binsa har cikin mota yana hure miki kunne ko? Ai kinsan da maganar inusa, wato irin mayaudaran samarin Nan ne yake zuwa wajan ki yana hure miki kunne harni Zaki kalla kina cewa ke kina sonsa ko? Idan na qara ji kince kina sonsa saina kakkarya ki a gidannan, Kuma daga yau babu ke babu shi,inusan damuka Sani shi zamu baki"
Cikin kuka tace "Allah banason inusa, nide Shahaab nakeso"
Jin abinda tace yasa Abba yayo kanta zai rufe ta da duka, cikin sauri Hajja tajanyota jikinta,
Hawaye ne suka sulalo daga idanun Ummah,koma waye wannan Shahaab haqiqa yariga yagama hurewa yarsu kunne, tunda gashi har mahaifin ta yana fada itama tana fada.
Hajja tasaka salati tana sake rushewa da Kuka, cikin kukan tace "wannan masifa Dame tayi kama? Mesunan qawa Ina kika samo wani Shahaab Kuma? Yaushe Zaki bi saurayi har cikin mota? Kifadamin su waye iyayensa inje inji Dame suke taqama da dansu zaizo wajanki batareda ubanki yasani ba?"
Cikin kuka tace "Hajja ni bansan iyayensa ba, Kuma nide Allah Shahaab nakeso"
Hajja tace "to inajin de aljani ne, Danni banta6a jin irin wannan sunan ba, saide a jinsin aljannu, ninasan ba zakiyi haka da niyya ba mesunan qawa, Gamo kikai da aljan"
Abba yace "babu wani aljani Hajja, Sai iskanci dayake damunta, Kuma ni bazata 6atamin suna ba, bazata janyomin abun kunya agida ba...."
Jin furucin Abba yasa Hajja tasake rushewa da Kuka tace"mummunan bakinka ba'a kan mesunan qawa ba, inda zatayi ciki da tuni tayi, jinake can unguwar gabar Yara suna Nan sunkai su talatin kowacce cikin shege ne da'ita, ita kanta Malamar asbitin dasuke zuwa wajanta take zubar musu cikin itama cikin shegen ne da'ita, Bayan Wanda ta haife, Amma ninasan Mesunan qawa inde tabiyo halin takwararta to ba zatayi cikin shege ba"
Ummah ta kalli Hajja da sauri, yaushe akayi ciki agarin har mutum talatin? (😂🤔)
Tagama lura cewa soyaiyar Aisha tasa kwata kwata Hajja bata ganin laifin yarinyar,ko kadan bazata iya tsawatar mata ba,Abba yace "tunda kince kina sonsa, tona tabbatar kona miki katangar qarfe tsakanin keda shi watarana bazan San lokacin dazaki tsallake kije wajan sa ba, danhaka ki shirya, zanje in samu jummai infada mata ta shirya takaiki can kano, daga Nan kuwuce Abuja akai ki gidan Mahmud Wakili aiki, tunda da naji tausayin ki nace ba zakije ba Gara ki zauna agaban mu abaki inusa, to yanzu Gara kije, dade ki zauna agari kina satar fita kina shiga motar saurayi bansan meyake miki ba, Gara kije can kikama aiki"
Yana fadin haka yafice daga gidan, Bai Zame ko'inaba Sai gidan Jummai qawar Hajja.
Aisha kuwa kuka tasa harda burburwa a jikin Hajja, "Hajja ki masa magana, Allah ni bazanje ko'inaba,Ina ruwana da wani Mahmud Wakili da zanje gidansa aiki, Kuma arasa gidan Wanda zanje aiki Sai wani Mahmud Wakili?, aini ba baiwar sa bace...."
Hajja ta share Hawayen idonta ta kama hannunta zasu shige daki, Aisha ta qwace hannunta taci gaba da kuka, Ummah tatashi ta wuce daki, domin kuwa ita hukuncin da mamuda ya yanke yayi mata daidai,babu Wanda zai nuna mata son Aisha kaf duniyar, Amma hakan ba zaisa taqi Bawa mijinta goyon baya akan tarbiyar yarinyar ba.
Jabir ne ya matso wajan ta yad'ora hannunsa akan dogon gashinta daya barbaje saboda kukan datasha, kannata yake shafawa tareda bubbuga bayanta alamun tayi hakuri, Shima kukan yake bashida bakin dazai iya lallashin yayar tasa, tana jinsa tafada jikinsa sukaci gaba da kukan gaba daya.
Awannna rana wuni sukai gidan babu dadi, Aisha banda Jan zuciya babu abinda take, abinci ma taqi Ci, Sai sharar hawaye take, Hajja tabata haquri harta gaji, ta qanqame wayar Hajja tana ta gwada Kiran Shahaab Amma abun baqin ciki waya taqi shiga, har dare Aisha tana daki taqi futowa waje, tana jiyo Abba yana shaida musu gobe jummai zatazo ta dauketa su tafi, jin babu Wanda yayi masa magana akan hukuncin nasa yasa wani sabon hawaye ya silalo daga idonta, baqin ciki yataru yazame mata goma da Ashirin, har gara ace wani gidan zataje aiki akan de taje gidan Mahmud Wakili,mutumin da kullum burinsa shine kamawa talakawa kayansu da kudaden su shine abinda ya'iya? Banda gidan man malam Audu daya saki bata ta6ajin inda akace yasaki gidan man wani ba, wayar Hajja tasake d'auka tafara Kiran layin Shahaab, saida ta kirashi yakai Sau goma,saide amsar guda daya ce, shine wayarsa akashe take.
Haka kowa yayi bacci Amma idon Aisha biyu, mutumin da taqi jininsa, Wai itace zataje gidansa aiki, Shahaab ne kawai zai fiddata daga wannan qulli, shikuma baya Nan, shin yasan Biron Dama haka kudinsa yake? Shine yasiyo mata da Kansa? Ko wanine yabashi? Shida yake Yaron Mahmud Wakili yaushe har zai samu wannan uban kudin? Anya ma kuwa yasan wanne irin Biro yabata? Haka ta dinga tunani tana yiwa kanta tambaya Wanda babu me amsa mata su Sai Shahaab, shikuma yamata Nisa.
Tana cikin wannan hali batasan yaushe bacci ya dauketa ba, washe gari haka ta zauna adaki taqi futowa, abinci ma qinci tayi, tun hajja tana lallashinta harta gaji taqyaleta, wajan qarfe goma Sha daya Abba yashigo tareda jummai, yana zuwa yacewa Ummah "kira mata Wannan yarinyar zasu tafi yanzu"
Cikin sauri Hajja tace"innalillahi wa inna ilaihirraji'un.... Yanzu mamuda da gaske kake ashe,? Yanzu rabani zakayi da me sunan qawa,?to babu inda yarinyar Nan zataje "
Cikin nutsuwa yace" Hajja, tafiyar ta shine yafi alkhairi, zamanta anan bansan wacce irin magana zata Dauko min ba"
yana fadar haka yashige Dakin Hajja yakamo hannun Aisha suka futo, kuka take tana Kiran Hajja, Hajja ta kama hannunta ta riqe itama tana kuka, daqyar Abba ya fizgeta suka fita waje, wata yar qaramar mota ce a kofar gidan, cikin motar yasaka ta, sannan jummai tashiga, shikuma yarufe musu motar, yasunkuyo da Kansa ta window yace "idan kunje kano, Akira hajiyar a tambayeta aji koda tasamu yar aikin to asake tura mata Aishan ko bude get ne ta dinga yi musu, zamanta acan din Hankali na zaifi kwanciya, nasan babu ita babu haduwa da wannan Yaron dayake hure mata kunne"
Aisha tana jinsa saide ko d'ago kanta batayi ta kalleshi ba, kanta na cikin qafafunta tana kuka.
Jummai tace "karka damu mamuda, nasan ma za'a dace insha Allah, bazan dawo gida Bama Sai an tabbatar min sunje Abujan lafiya, kayi mata addu'ah"
Cikin sanyin jiki yayi murmushin qarfin Hali, tareda barin jikin motar yana juyawa gida, shi Kansa bazai so yarsa mace qwaya daya jal tayi nesa dashi ba, Sai dole, yana tare da'ita gida daya bai ta6a sanin akwai Wanda yake zuwa yana Kiran yarsa ba, zancen ma yawuce kofar gida agaban jama'ah saide a mota, Allah ne kadai yasan abinda zai faru inba Allah ne yakiyaye ba, juyawa yayi ya kalli motar yayinda suka fara tafiya, cikin ransa yana Binta da kyakkyawar addu'ah, Idonsa nakan motar har suka yi Nisa yadena hangosu.
Da alama Jummai ta shirya yin futo na futo tsakanin ta da Hajja😎😎
to, takwara tatafi wajan takwararta🙄, rashin kunya tatafi wajan masifa da iko🥹🥹
Wannan shi ake kira, angudu ba'a tsiraba 💁🏻♀️mahaifi yatura 'yarsa inda yake gudu 😇
Menene zai kasance Idan Shahaab ya dawo yaga Aisha acikin gidansa?🤔
Yaya makomar qaryaiyakin daya dinga shuka mata?🤔
(SHAHAAB littafin kudi ne, idan kika karanta min batareda kin biya ba, nabarki keda mahaliccinki,nera 300 Ne kacal bansaka kudi me yawa ba
0164549488
Amina muhammad
GTbank
My number
08033300034
Mutara zuwa gobe 🙏🏻
Amnah El Yaqoub✍🏻
Salam Alaikum,masu fitar min da littafi nagode, masu karanta wa batareda sisinsu ba nabarku kuda ALLAH,nide ban yafe muku ba, bazan yafe ba Kuma har abada, nabarku da futowar rana da faduwarta.
Masu cewa indinga yin posting biyu a rana kuyi haquri gaskiya bazan iyaba, Alokacin danace zan dinga yin posting biyu a rana, nayi tunanin yin VIP group 500, shine nace zan dinga yin posting biyu, to yanzu 300 dinma wasu suna cewa ta musu tsada,shiyasa nafasa yin VIP din, maganar posting biyu ta rushe, duk page guda daya, Ina bata awa hudu ne akansa, awa uku typing, awa daya editing, tayaya zan dinga bata awa takwas a rana inyi page guda biyu? Ayyukan gidan Ina zan kaisu? Masu min magana ta private inyi Yaya dasu? Masu kirana inyi Yaya dasu? Gaskiya kuyi haquri, kullum zamu dinga posting daya, idan Allah yasa nasamu lokaci zakuga posting biyu, idan bansamu ba zakuga daya, duk lokacin dakuka ga guda daya please 🙏🏻kuce Allah yayi masa Albarka Faqad👌🏻.
Page 22