Sashe 25
Shahaab Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Su Aisha basu San menene yafaru ba Sai Gani tayi wannan securities din duk sun sunkuyar da kansu qasa suna fuskantar ta, har rige-rigen bata haquri suke, haushi da Kuma mamakin su ya kamata, yanzu yanzu suka gama cewa zasu kaisu folice station Amma Kuma suna bata haquri yanzu, kamar wasu masu Fama da aljannu, taqaici da 6acin ran da aka bata ne yasa tayi jifa da turaren data dauka, tajuya tafice cikin fishi, ice-cream dinma tafasa Sha,har suka fice daga mall din Ramadan bai daina kallonta ba, yarinyar tahadu ta ko'ina, babu wani namiji me lafiya dazai ganta yakasa yabawa.
Shahaab kuwa yana ganin yanda tafice cikin fishi yace"to 'Yan masifar sunzo"
Ramadan yajuyo yasake Kallan Shahaab daya 6uya abayansa Sai magana yake shi kadai, Kallan rashin fahimta yayi masa sannan yace "meyake faruwa ne?"
Wata irin ajiyar zuciya yasauke tareda Lumshe ido yabude, sannan yace "MAAMA"
Ramadan daya dauki haske cikin sauri ya zaro Idonsa yace "what...?"
Shahaab bai iya bashi amsa ba Sai Kansa daya daga masa kawai
Suna shiga mota Auwal yafara lallashin fati saboda kukan datake yi, saida tayi shiru sannan yaqara Bawa Aishan ma haquri, Bai qyalesu ba saida ya tabbatar sun Dan saki ransu, sannan sukai sallama suka shiga gida, Bayan sunyi shirin kwanciya Aisha banda tsinewa masu mall dinnan babu abinda take yi,ta nayi itama fati tana tayata, daqyar suka samu bacci ya dauke su
(Shahaab littafin kudine, idan kika karanta batareda kin biya ba, nabarki keda mahaliccinki, nide ban yafe a)
******
Tunda suka dawo masaukinsu Shahaab yayi shiru yana tunani shi kadai, Babban abinda yafi 6ata masa rai shine yanda ya ganta dawani yaro.
Ramadan ya kalleshi yace "Wai Dama haka yarinyar Nan take?, Shahaab Anya kuwa bahaushiya ce?"
Kansa ya jijjiga masa alamun hakane, ajiyar zuciya ya sauke yace "gaskiya tanada kyau sosai, amma Kuma yarinya ce sosai ya'akai Takeda kyan diri haka?"
Cikin masifa Shahaab yace "bansaniba, meya Hana kabita ka tambayeta?"
Murmushi Ramadan yayi, Bayan yagano kishi ne yake cin abokin nasa, ajiyar zuciya yasauke sannan yace "menene abun 6acin rai Kuma a magana ta?"
Cikin fishi yace "to kazo gabana Sai wani yabon ta kake, kaiba matarka ba, ba komai ba, ni abinda yafi 6atamin rai ma shine Yaron Dana gansu tare, bansan Yaya zanyi in tambayeta Shiba, zatace min Yaya akai nasan taje mall, idan nace Ina tareda ogana tace Amma nakasa yimata magana Ina Gani security suka ka masu, Ramadan duk kaine kajamin wannan abun, inda kabarni naje mata a Mahmud Wakili na, daduk haka bata faru ba, daga Kai har mama kira kuke idan zanyi mu'amula da mace tona 6oye mata kaina, na6oye mata koni waye, ta hakane zansan mesona tsakani da Allah, Ramadan ni banga amfani 6oyewa MAAMA kaina ba, saboda yarinya ce qarama, batada wani ilmi akan Zaman takewar rayuwa, yanda yarinyar ta yarda Dani idan saceta zanyi da tuni na saceta, na lura batasan komai ba akan soyaiya Sai abinda aka Koya mata,nafada mata banda aure, ta yarda, nafada mata nidan maiduguri ne, tayarda, nafada mata ni Yaron Mahmud Wakili ne, tayarda, duk wani abu Dana fada mata yarda take saboda tasan bazanyi mata qarya ba,nafada mata inason haihuwa idan nayi aure da bakinta tace zata fara azumin sitta shawwal tayi min addu'ah ko Allah zai ban haihuwa, yanzu Mena aikata haka? Inda nafada mata gaskiya tunda farko dazan iya futowa a ko'ina ne in kare ta amatsayina na Mahmud Wakili"
Jikin Ramadan ne yayi Sanyi,kafadarsa yadan bubbuga yace "kayi hakuri Shahaab...,Amma shawarar damuka baka nida mama itace mafita,inda bakayi hakan ba, zaka San halaiyar yarinyar ne kamar haka? Ni banga laifin taba dakake cewa baka sonta, wannan yarinyar babu inda bazaka shiga da'ita ba, asalima yarinya ce qarama Sai abinda ka dorata akai zatayi, Amma tunda baka sonta, kadena zuwa inda take, kanisanceta, idan Kai kasan zuciyar ka, ita bakasan Tata ba, zata Iya sonka, qarshe karabu da'ita, hakan bai kamata ba, karabu da yarinyar mutane kawai "
Cikin tsananin kishi Shahaab yace"Nina Rasa gane inda kanufa Ramadan, saika dinga nunamin kamar so kake narabu da yarinyar kaikuma kaje ka aure ta"
Dariya ce ta kama Ramadan, Amma saiya danne, yace "Aure kuwa da gudu"
Shahaab yayi masa wani irin kallo, cikin zuciyar sa yace zan dauki mataki, dole zan kawo qarshan komai, haka suka kwana babu wanda yasake magana, kowa da abunda yake saqawa acikin ransa, shikam Ramadan ransa fes yayi bacci, ko banza yasan ya tunzura Shahaab, dama da niyya yafadi hakan danya ga gudun ruwan abokin nasa.
******
Washe gari tunda safe, Aisha tatafi gida, tana zuwa Hajja ta tareta cikin murna, tsarabar Lemo da bread din data kawo musu suka rarraba har jummai saida aka kaiwa, cikin sauri ta shige dakin Hajja ta dauki wayarta tafara duddubawa ko Shahaab Yakirata, saide bataga komai ba, tunani tafara me zata siyo masa idan yazo tabashi Shima a matsayin tsarabar kano? Wani tunani tayi, cikin sauri Takoma Dakin Umman ta, asusunta dayake Qasan gado tafasa,dubu biyar biyar din daya bata sau biyu, dakuma dubu biyunta na albashin ta, tahada dubu goma Sha biyu, tasaka hijab dinta ta cewa Ummah da Hajja "natafi gidansu Walida yanzu zan dawo"
Hajja tace "dole kije Kam kwana biyu Baku hadu ba, itama rannan tazo nace mata ai kin tafi kano"
Aisha batace komai ba tafice, tana fita kofar gida bata nufi gidansu Walida ba Kai tsaye wata hanya ta d'auka, saida taci tafiya sosai, sannan taje wani Babban shago, tabawa me shagon kudin tace "gashi abani agogo da links"
Cikin sauri ya d'ago ya kalleta yace "to wanne Kala kikeso?"
Tace "Nima bansaniba ba, kawai kabani me kyau"
Murmushi yayi yace "to Wanda zai saka fari ne ko baqi?"
Tace "fari ne"
Cikin farinciki yabata agogon da links din tuwan toka yace "to wannan zaifi kyau"
Kar6a tayi sannan tafice, acikin hijabinta ta 6oye su, sannan Takoma gida tasaka su acikin kayanta
******
Da yamma yaga Shahaab sai shiri yake, manyan Kaya ne ajikinsa na wani yadi Mai mutuqar kyau, cikin mamaki ya sake Kallan sa yace "fita zamuyi ne? Naga Kanata shiri"
Cikin sauri yajuyo ya kalli Ramadan din sannan yace "fita zanyi de"
Daria ce ta kama Ramadan, yayi murmushi yace "to naji, Ina zakaje?"
Kai tsaye yace "jigawa"
"Amma Shahaab kasan fa jirgin safiya zamubi mutafi Abuja, yanzu karfe hudu, idan katafi yaushe zakaje harka dawo?"
Kallan sa yayi yace "akwai tafiyar dazanyi zuwa Australia goben da yamma idan mun koma Abuja Dasafe, tafiyar zata daukeni wasu Yan kwanaki masu yawa, dole zanje inyi sallama da Maama, ko zan tafi ne batare data Sani ba?"
Ramadan yayi murmushi yace "a a, Amma Dan Allah katafi Dani danna sake ganin ta" (😂)
Cikin daure fuska yace "zanyi sallama da yarinya kana cewa zakaje, idan kaje a'ina zaka zauna? Ka zauna anan kawai, zan saka face mask inje dakaina indawo"
Yana gama fadar haka yafice daga d'akin, Ramadan yasaki murmushi cikin ransa yace "Allah yakai damo ga harawa...."
Idar da sallar magrib dinta kenan, tafada duniyar tunaninsa, sotake ta kirashi, Amma Kuma tasan idan ta ta6awa Hajja katin waya to zata gane, Kuma ta dinga yimata mita kenan,kamar almara taji wayar tana qara,tana dubawa taga number shice, cikin sauri ta d'auka sannan tashige Dakin Hajja, cikin wata irin murya wadda zaka tabbatar yayi kewarta yace "Maaaamah"
Wani irin yarrrr taji ajikinta, ahankali tace "na'am"
Kai tsaye yace "Ina kofar gida"
Cikin murna tace "da gaske?"
Yace "sosai, kifuto yanzu"
Tace "to" sannan takashe wayar
Daki ta wuce tadauko abunda ta siyo masa dazu, sannan tafuto tana Sanye da hijabi dogo, Ummah ta kalla tace "Ummah zanje wajan Walida"
Kafin Ummah tayi magana Hajja tace "keni narasa gane wannan zarya da kike a gidansu Walida, kusan kullum Sai kinje inji de lafiya?"
Dan qaramin bakinta ta turo gaba tace "littafi zan kar6o fa"
Ummah tace "kuma kullum bakida aiki Sai zuwa da daddare? Kishiga hankalin kifa"
Hajja tace "Allah ya kyauta, toki tabbatar kina kar6owa Zaki dawo"
Cikin murna tace "to Hajja"
Sannan tafice daga gidan cikin murna, wannan motar bada ita yake zuwaba, Amma kasancewar tasan anan yake ajiye motarsa, saita nufi wajan, tana zuwa bata jira yafuto yabude mata ba, tazagaya ta bude tashiga, sannan tarufe, Kallan sa tayi cikin farinciki tace "Dama wallahi sonake naganka, na Dade inason muyi waya inbaka labari"
Cikin mamakin farincikinta yace "meyasa baki kirani ba to?"
Cikin shagwa6a tace "to ai idan na kiraka Hajja zata gane, Kuma zata San nata6a mata katin waya"
Cikin ransa yace Kati Kuma? A fili saiyace "Dama ba wayarki bace?"
Girgiza kanta tayi tace "wayar Hajja ce"
"wace Hajja?" ya tambayeta
Tace "kaka tace, Amma Kuma wayar a hannu na take wuni, inayin game da'ita, yanzu Kuma Dana dawo Naga duk ta gogesu daga wayarta" ta qarasa maganar idonta na cikowa da qwalla
Cikin sigar rad'a yace mata "menene na kukan Kuma? Kincika shagwa6a Maama, Kidena yin game, kici gaba da karatu yafi"
Murmushi tayi tace "kasan me? Inaso inyi karatu inzama likita, indinga aiki a Asbiti, inkai babana Saudia, nikuma saina tafi tareda Ummah na da Hajja"
Wani irin daci yaji acikin ransa, saboda idan akwai abinda yatsana to shine matarsa tayi aiki, baya fatan ma ace yarage ta tawani Fannin bare har tayi tunanin yin aiki domin samun kudi, matsayin matarsa yawuce tayi aiki abata kudi, saide ta dauki kudin tabawa ma'aikata, wata zuciyar tace dashi to ita matarka ce? Acan Qasan maqoshinsa yace "yes"
saboda kada ta gane yanayin dayake ciki na rashin son karatu,Sai yayi Murmushi yace "nikuma fa? Bazaki kaini ba?"
Dariya tayi, tace"kaima saimu tafi dakai to,kabani wayarka nayi game kaji"
Cikin ransa yace"kodan yarinya ce? Yanzu inashi Ina wani game a wayarsa? Kallan ta yayi a fili yace "banda game"
Cikin sauri tace "to cartoon"
Murmushi yayi yace "Shima babu"
Bakinta ta turo gaba tace "to photuna"
Daukan wayar yayi batareda tunanin komai ba yabata, saboda yasan shide babu pictures dinsa aciki, haka babu wata shaida dazata Gani ta tabbatar mata cewa shine Mahmud Wakili.
Shahaab kuwa yana ganin yanda tafice cikin fishi yace"to 'Yan masifar sunzo"
Ramadan yajuyo yasake Kallan Shahaab daya 6uya abayansa Sai magana yake shi kadai, Kallan rashin fahimta yayi masa sannan yace "meyake faruwa ne?"
Wata irin ajiyar zuciya yasauke tareda Lumshe ido yabude, sannan yace "MAAMA"
Ramadan daya dauki haske cikin sauri ya zaro Idonsa yace "what...?"
Shahaab bai iya bashi amsa ba Sai Kansa daya daga masa kawai
Suna shiga mota Auwal yafara lallashin fati saboda kukan datake yi, saida tayi shiru sannan yaqara Bawa Aishan ma haquri, Bai qyalesu ba saida ya tabbatar sun Dan saki ransu, sannan sukai sallama suka shiga gida, Bayan sunyi shirin kwanciya Aisha banda tsinewa masu mall dinnan babu abinda take yi,ta nayi itama fati tana tayata, daqyar suka samu bacci ya dauke su
(Shahaab littafin kudine, idan kika karanta batareda kin biya ba, nabarki keda mahaliccinki, nide ban yafe a)
******
Tunda suka dawo masaukinsu Shahaab yayi shiru yana tunani shi kadai, Babban abinda yafi 6ata masa rai shine yanda ya ganta dawani yaro.
Ramadan ya kalleshi yace "Wai Dama haka yarinyar Nan take?, Shahaab Anya kuwa bahaushiya ce?"
Kansa ya jijjiga masa alamun hakane, ajiyar zuciya ya sauke yace "gaskiya tanada kyau sosai, amma Kuma yarinya ce sosai ya'akai Takeda kyan diri haka?"
Cikin masifa Shahaab yace "bansaniba, meya Hana kabita ka tambayeta?"
Murmushi Ramadan yayi, Bayan yagano kishi ne yake cin abokin nasa, ajiyar zuciya yasauke sannan yace "menene abun 6acin rai Kuma a magana ta?"
Cikin fishi yace "to kazo gabana Sai wani yabon ta kake, kaiba matarka ba, ba komai ba, ni abinda yafi 6atamin rai ma shine Yaron Dana gansu tare, bansan Yaya zanyi in tambayeta Shiba, zatace min Yaya akai nasan taje mall, idan nace Ina tareda ogana tace Amma nakasa yimata magana Ina Gani security suka ka masu, Ramadan duk kaine kajamin wannan abun, inda kabarni naje mata a Mahmud Wakili na, daduk haka bata faru ba, daga Kai har mama kira kuke idan zanyi mu'amula da mace tona 6oye mata kaina, na6oye mata koni waye, ta hakane zansan mesona tsakani da Allah, Ramadan ni banga amfani 6oyewa MAAMA kaina ba, saboda yarinya ce qarama, batada wani ilmi akan Zaman takewar rayuwa, yanda yarinyar ta yarda Dani idan saceta zanyi da tuni na saceta, na lura batasan komai ba akan soyaiya Sai abinda aka Koya mata,nafada mata banda aure, ta yarda, nafada mata nidan maiduguri ne, tayarda, nafada mata ni Yaron Mahmud Wakili ne, tayarda, duk wani abu Dana fada mata yarda take saboda tasan bazanyi mata qarya ba,nafada mata inason haihuwa idan nayi aure da bakinta tace zata fara azumin sitta shawwal tayi min addu'ah ko Allah zai ban haihuwa, yanzu Mena aikata haka? Inda nafada mata gaskiya tunda farko dazan iya futowa a ko'ina ne in kare ta amatsayina na Mahmud Wakili"
Jikin Ramadan ne yayi Sanyi,kafadarsa yadan bubbuga yace "kayi hakuri Shahaab...,Amma shawarar damuka baka nida mama itace mafita,inda bakayi hakan ba, zaka San halaiyar yarinyar ne kamar haka? Ni banga laifin taba dakake cewa baka sonta, wannan yarinyar babu inda bazaka shiga da'ita ba, asalima yarinya ce qarama Sai abinda ka dorata akai zatayi, Amma tunda baka sonta, kadena zuwa inda take, kanisanceta, idan Kai kasan zuciyar ka, ita bakasan Tata ba, zata Iya sonka, qarshe karabu da'ita, hakan bai kamata ba, karabu da yarinyar mutane kawai "
Cikin tsananin kishi Shahaab yace"Nina Rasa gane inda kanufa Ramadan, saika dinga nunamin kamar so kake narabu da yarinyar kaikuma kaje ka aure ta"
Dariya ce ta kama Ramadan, Amma saiya danne, yace "Aure kuwa da gudu"
Shahaab yayi masa wani irin kallo, cikin zuciyar sa yace zan dauki mataki, dole zan kawo qarshan komai, haka suka kwana babu wanda yasake magana, kowa da abunda yake saqawa acikin ransa, shikam Ramadan ransa fes yayi bacci, ko banza yasan ya tunzura Shahaab, dama da niyya yafadi hakan danya ga gudun ruwan abokin nasa.
******
Washe gari tunda safe, Aisha tatafi gida, tana zuwa Hajja ta tareta cikin murna, tsarabar Lemo da bread din data kawo musu suka rarraba har jummai saida aka kaiwa, cikin sauri ta shige dakin Hajja ta dauki wayarta tafara duddubawa ko Shahaab Yakirata, saide bataga komai ba, tunani tafara me zata siyo masa idan yazo tabashi Shima a matsayin tsarabar kano? Wani tunani tayi, cikin sauri Takoma Dakin Umman ta, asusunta dayake Qasan gado tafasa,dubu biyar biyar din daya bata sau biyu, dakuma dubu biyunta na albashin ta, tahada dubu goma Sha biyu, tasaka hijab dinta ta cewa Ummah da Hajja "natafi gidansu Walida yanzu zan dawo"
Hajja tace "dole kije Kam kwana biyu Baku hadu ba, itama rannan tazo nace mata ai kin tafi kano"
Aisha batace komai ba tafice, tana fita kofar gida bata nufi gidansu Walida ba Kai tsaye wata hanya ta d'auka, saida taci tafiya sosai, sannan taje wani Babban shago, tabawa me shagon kudin tace "gashi abani agogo da links"
Cikin sauri ya d'ago ya kalleta yace "to wanne Kala kikeso?"
Tace "Nima bansaniba ba, kawai kabani me kyau"
Murmushi yayi yace "to Wanda zai saka fari ne ko baqi?"
Tace "fari ne"
Cikin farinciki yabata agogon da links din tuwan toka yace "to wannan zaifi kyau"
Kar6a tayi sannan tafice, acikin hijabinta ta 6oye su, sannan Takoma gida tasaka su acikin kayanta
******
Da yamma yaga Shahaab sai shiri yake, manyan Kaya ne ajikinsa na wani yadi Mai mutuqar kyau, cikin mamaki ya sake Kallan sa yace "fita zamuyi ne? Naga Kanata shiri"
Cikin sauri yajuyo ya kalli Ramadan din sannan yace "fita zanyi de"
Daria ce ta kama Ramadan, yayi murmushi yace "to naji, Ina zakaje?"
Kai tsaye yace "jigawa"
"Amma Shahaab kasan fa jirgin safiya zamubi mutafi Abuja, yanzu karfe hudu, idan katafi yaushe zakaje harka dawo?"
Kallan sa yayi yace "akwai tafiyar dazanyi zuwa Australia goben da yamma idan mun koma Abuja Dasafe, tafiyar zata daukeni wasu Yan kwanaki masu yawa, dole zanje inyi sallama da Maama, ko zan tafi ne batare data Sani ba?"
Ramadan yayi murmushi yace "a a, Amma Dan Allah katafi Dani danna sake ganin ta" (😂)
Cikin daure fuska yace "zanyi sallama da yarinya kana cewa zakaje, idan kaje a'ina zaka zauna? Ka zauna anan kawai, zan saka face mask inje dakaina indawo"
Yana gama fadar haka yafice daga d'akin, Ramadan yasaki murmushi cikin ransa yace "Allah yakai damo ga harawa...."
Idar da sallar magrib dinta kenan, tafada duniyar tunaninsa, sotake ta kirashi, Amma Kuma tasan idan ta ta6awa Hajja katin waya to zata gane, Kuma ta dinga yimata mita kenan,kamar almara taji wayar tana qara,tana dubawa taga number shice, cikin sauri ta d'auka sannan tashige Dakin Hajja, cikin wata irin murya wadda zaka tabbatar yayi kewarta yace "Maaaamah"
Wani irin yarrrr taji ajikinta, ahankali tace "na'am"
Kai tsaye yace "Ina kofar gida"
Cikin murna tace "da gaske?"
Yace "sosai, kifuto yanzu"
Tace "to" sannan takashe wayar
Daki ta wuce tadauko abunda ta siyo masa dazu, sannan tafuto tana Sanye da hijabi dogo, Ummah ta kalla tace "Ummah zanje wajan Walida"
Kafin Ummah tayi magana Hajja tace "keni narasa gane wannan zarya da kike a gidansu Walida, kusan kullum Sai kinje inji de lafiya?"
Dan qaramin bakinta ta turo gaba tace "littafi zan kar6o fa"
Ummah tace "kuma kullum bakida aiki Sai zuwa da daddare? Kishiga hankalin kifa"
Hajja tace "Allah ya kyauta, toki tabbatar kina kar6owa Zaki dawo"
Cikin murna tace "to Hajja"
Sannan tafice daga gidan cikin murna, wannan motar bada ita yake zuwaba, Amma kasancewar tasan anan yake ajiye motarsa, saita nufi wajan, tana zuwa bata jira yafuto yabude mata ba, tazagaya ta bude tashiga, sannan tarufe, Kallan sa tayi cikin farinciki tace "Dama wallahi sonake naganka, na Dade inason muyi waya inbaka labari"
Cikin mamakin farincikinta yace "meyasa baki kirani ba to?"
Cikin shagwa6a tace "to ai idan na kiraka Hajja zata gane, Kuma zata San nata6a mata katin waya"
Cikin ransa yace Kati Kuma? A fili saiyace "Dama ba wayarki bace?"
Girgiza kanta tayi tace "wayar Hajja ce"
"wace Hajja?" ya tambayeta
Tace "kaka tace, Amma Kuma wayar a hannu na take wuni, inayin game da'ita, yanzu Kuma Dana dawo Naga duk ta gogesu daga wayarta" ta qarasa maganar idonta na cikowa da qwalla
Cikin sigar rad'a yace mata "menene na kukan Kuma? Kincika shagwa6a Maama, Kidena yin game, kici gaba da karatu yafi"
Murmushi tayi tace "kasan me? Inaso inyi karatu inzama likita, indinga aiki a Asbiti, inkai babana Saudia, nikuma saina tafi tareda Ummah na da Hajja"
Wani irin daci yaji acikin ransa, saboda idan akwai abinda yatsana to shine matarsa tayi aiki, baya fatan ma ace yarage ta tawani Fannin bare har tayi tunanin yin aiki domin samun kudi, matsayin matarsa yawuce tayi aiki abata kudi, saide ta dauki kudin tabawa ma'aikata, wata zuciyar tace dashi to ita matarka ce? Acan Qasan maqoshinsa yace "yes"
saboda kada ta gane yanayin dayake ciki na rashin son karatu,Sai yayi Murmushi yace "nikuma fa? Bazaki kaini ba?"
Dariya tayi, tace"kaima saimu tafi dakai to,kabani wayarka nayi game kaji"
Cikin ransa yace"kodan yarinya ce? Yanzu inashi Ina wani game a wayarsa? Kallan ta yayi a fili yace "banda game"
Cikin sauri tace "to cartoon"
Murmushi yayi yace "Shima babu"
Bakinta ta turo gaba tace "to photuna"
Daukan wayar yayi batareda tunanin komai ba yabata, saboda yasan shide babu pictures dinsa aciki, haka babu wata shaida dazata Gani ta tabbatar mata cewa shine Mahmud Wakili.