← Book details Rabo Ajali Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 43 OF 48

Sashe 43

Rabo Ajali Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Ajiyar zuciya Gaje tayi tace kwarai abun da ya faru kenan dan tana faďuwa nayi saurin janta store saboda jin muryar madam da nayi ta sakko nemanta,
munfi minti talatin a store sannan na daukota na fito da ita da sauri dan kar wani ya ganni,
ina fitowa naga wani me keke napep a kofar gidan alhj bara'u, dasauri na karasa nasata nace ya kaini dorayi gidan kawu na,
bai tsaya musun kudi ba saboda ganin halin da muke ciki,
tafiya sosai mukayi har muka iso nace ya jirani,
ďakin matar kawuna na kaita nace dan Allah su kular min da ita kafin gobe da safe,
ba musu tace ba komai saboda sunsan irin alherin da hajiya ke musu,
sai kusan goma na koma gidan,
ranar a tsorace na kwana,, washe gari ina tashi na tattara kaya na nayi ma madam karya nace mata mahaifina bashi da lafiya acan nijar,
kudi ta bani tace Allah ya bashi lafiya tare da jaddada min in dawo da zarar ya samu sauki,
amsata kawai nayi na fita daga gidan na wuce ďorayi,
a ranar muka wuce nijar ni da hajiya dan nasan acan ne zata fi samun kulawa saboda kawuna malamine,
babu irin addu'ar da ba'ayi ba amma sam babu sauki dan ko motsi batayi,
A can na barta na dawo jigawa ina wani aikin, har Allah ya hadani da wani mukayi aure,
yau kwanana biyar da zuwa gida na tarar ta farfado,
shekaran jiya ne ta matsa ita akaita can gidansu a cameroon,
bamu so mu kaita ba har saita kara samun sauki amma malam yace lallai mu kaita saboda ta samu nutsuwa,
a can cameroon da muka je ta labarta ma mahaifinta komai shine yace a shirya a taho nan kano domin a fayyace komai dan kar aja lokaci a kuma kullo wani mugun abun da zai fi na da..

Cikin tashin hankali oyizah tayi kukan kurah ta shako wuyan zeenatu tana fadin ni zakuyi ma sharri wallahy yau sai na kasheki,
da sauri Affan ya taso ya banbare mahaifiyarshi a jikin oyizah ya shiga dukanta yana haki yana fadin duk abubuwan da tayi mishi da kuma wanda tayi ma Afeeyah da kuma kisan da tayi ma jabeer,
shaketa yayi idonshi yayi jawur cikin ďaga murya yace me jabeer yayi miki kika kasheshi,
kakarin wuya oyizah keyi idonta sun firfito waje tana girgiza kanta,
babu wanda yayi yunkurin hana Affan har farida da kuka yaci karfinta saboda jin mugun alkaba'in da mahaifiyarta tayi,
zeenatu ce ta taso da sauri ta fara banbareshi a jikinta saboda kar yayi kisan kai,
dakyar ya rabu da ita yana haki idonshi cike da kwalla,
mikewa oyizah tayi ta ruga dakinta da gudu tana haki kamar zata mutu,
tana shiga ta bankade katifarta da katakon, tana dagawa taga babu komai cikin ramin sai kasa,
da sauri tasa hannu tana tone kasar ciki kamar mahaukaciya tana fadin ina kuke, waye ya kwashe ku,
wayyo Allah na shiga uku na lalace,
buga kofar ďakin taji anayi da karfi kamar za'a ballata,
a hankali ta leka ta windon don ganin ko waye,
yansanda ta gani tsaye su kusan shida da mace daya,
dariya ta saki wacce da gani kasan ta takaici ce ta jawo jakar kayan tsafinta nan da nan ta bace daga ďakin....

Mrs tijjani shattima...
[15/12 09:38] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 6⃣2⃣ By Aysha Ya'u kurah

Yan sandan sunfi minti goma a tsaye suna bugawa ba'a buďe ba,
cikin sanyin jiki alhj basheer ya taso ya dauko wani key yasa ya bude,
wayam suka gani ba oyizah ba sawunta sai katon ramin karkashin gadonta ne yayi musu sallama a idanuwansu,
alhj basheer idonshi ya kara ja yace jikina ya bani zata gudu dan shaidancinta bazai kare anan gurin ba,
da kun bar Affan ya kasheta mun huta dan yanzu wallahi bazata kyalemu ba,
malam maina ya taso yace ka kwantar da hankalinka in shaa Allahu babu abinda zai faru,
zamu toshe duk wata kafar da zata samu shigowa rayuwarku da addu'a,
alhj basheer ya sharce gumin goshinshi yace to Allah yasa, Ameen duk mutanen gurin suka ce,
Alhj basheer ya kalli Affan ya dawo kusa dashi yace Affan dama duk abinda kakeyi kana sane,
Affan ya girgiza kanshi yace ranar da mummy tayi niyyar kashe Afeeyah ranar na dawo hayyacina da taimakon Allah da taimakon Afeeyah,
nan ya kwashe duk labarin da kaka liman ya bashi na irin kokarin da Afeeyah tayi akansu ya fada musu sannan ya kuma faďa musu dalilin da yasa mummy ta kashe jabeer,,
ya share hawayen fuskarshi yace daddy dalilin da yasa kaga naki tafiya in bar Afeeyah a asibiti kenan saboda nasan muna barin gurin zata karasa ta,
doctr musah ma yasan na samu sauki saboda washe gari da mummy ta matsa sai mun tafi naje na sameshi na fada mishi komai nace ya taimakeni ya dauketa yace su zasu dinga jinyarta,
da kyar ya yarda dan a tunaninshi ban samu sauki ba shirme nake mishi,
muna tafiya yace min yaje dakin dan ya gasgata maganata sai ya tarar ta cire pillow tana kokarin kashe ta,
hankalinshi ya tashi a lokacin sai ya tabbatar naji sauki shine ya shirya plan din za'a kaita dakin hutu,
alhj basheer ya jinjina kanshi hawaye na fita a idonshi yana faďin ku yafe min, duk ni na jawo muku da na shigo da safiyya cikin iyalina,
gashi bata tsaya kai na ba har saida ta taba ya'yan makota na, dan Allah kuyi min afuwa ku dau duk wani hukuncin da ya dace a kaina,
zeenatu tace ka daina kuka alhj ba laifinka bane RABO ne ya shigo da ita rayuwarka, Rabon salma da Farida zai iya AJALIN duk wanda ya hana wannan auren a lokacin,
cikin kuka alhj basheer yace tabbas ya ko yi ajalin mahaifiyarta dan taki amincewa da zancen,
ashe safiyar ce ma ta kasheta da hannunta,
Affan yace har Anty salma itace silar mutuwarta dan jiya da mukayi waya da kaka duk ya faďa min hatsaririkan da Afeeyah ta tsallake a gidan nan,
mamakin alamarin kowa ya dinga yi haďe da ganin jarumta da jajurcewar Afeeyah,
Abida dai banda kuka babu abinda takeyi dan mutuwar jabeer ta dawo mata sabuwa fill a yau,
tabbas da an barta ita da hannunta zata kasheta ta huce takaicin rabata da nagartaccen ďanta mai cike da Haiba da tayi..,

Cikin kuka fareeda ta matso kusa da Affan tace dan Allah Affan ka yafe min abin da nayi maka wallahy sharrin shaidan ne da kuma ganin mummy nayi,
Affan ya janye kafarshi ya galla mata harara,
cikin tsawa alhj basheer yace tashi ki bamu guri yau dinnan zaki bi uwarki dan ban sani ba ko ke din ma ta tsafin ce,
fareeda ta rushe da kuka tana bashi hakuri, a hankali zeenatu tace alhj laifin wani baya shafar wani,
duk wanda yaga farida yaga jininka dan haka hannunka bazai rube ba ka yanke ka yar ba,
alhj basheer yayi saurin cewa saidai kuwa in bai isheni da wari ba,
yanzu ke kina so in zauna da jinsin matsafa a gida,
Baffa yace bashiru hakuri zakayi ya' dai taka ce dan haka dole ka riketa ku koya mata tarbiyar da addini ya koyar kuma ku aurar da ita,
nan suka cigaba tattauna maganar cikin tsananin al'ajabi....

Cikin tashin hankali oyizah ta bayyana a gurin tsafinsu,
kuka sosai takeyi a gaban chummy tana faďa mata duk yadda akayi har dawowar zeenatu da samun saukin Affan,
chummy ta kalli oyizah cikin mamaki tace ya akayi haka ta faru,
oyizah tace nima ban sani ba, komai na kayan aikina an kwasheshi a karkashin gado babu komai a gurin sai kasa,
sai kuma kwalbar nan da yan iskan yarannan suka fasa nasan shiyasa zeenatu ta farfaďo,
chummy tace na sakeyin wacce tafi tada karfi kin ganta can,
oyizah cikin mamaki tace to ya akayi haka,
chummy tace ni nafi mamakin na dakinki da wanda kika birne a bakin damo,
oyizah tayi saurin ďago kanta tace nasan wanda zaiyi min wannan aikin,
wannan yar iskar yarinyar ce zatayi min, wallahi I will not spare her,
yanzun nan zanje asibitin da take in kasheta,
chummy tayi murmushi tace daďina dake garaje,
bakya tunani kafin kiyi abu,
waye ya faďa miki suma yanzu zasu zauna,
, ai sun riga sun san sirrinmu so sai munyi da gaske ta karkashin kasa musa ki koma gidanki sai ki aiwatar da ayyukanki cikin kwanciyar hankali,
oyizah ta gyada kanta tace wallhi wannan karan mai zafin zanyi duk saina kashesu in mallake alhj da dukiyarshi muyi zaman mu tare har karshen rayuwarmu,,,
chummy tace yauwa ashe kin gane,
yau da daddare zamu fara aikin, kinsan akwai ďan tsoho da kika kawo to dashi za'ayi miki aikin, yanzu tashi muje gurin Dodo BELAH mu dawo kafin lokacin meeting yayi,
oyizah ta mike zuciyarta wasai dan a tunaninta komai nata zai koma normal tunda CHUMMY tayi assuring dinta,,,
oyizah sarkin sa'a........

Mrs tijjani shattima....
[15/12 09:38] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 6⃣3⃣ By Aysha Ya'u Kurah
Chapter 43 · 0% Book details