Sashe 14
Rabo Ajali Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ihu ya dinga ji kamar a cikin mafarki,
a hankali ya buďe idonshi yaji bugun kofar da ake ma ďakinshi yaki tsagaitawa, da sauri ya diro daga kan gado jikinshi na rawa ya bude kofar,
Salma da farida ya gani tsaye suna ihu suna kuka suka ce daddy Affan-- Da sauri ya katsesu yace me yasamu Affan din, kasa bashi amsa sukayi sunata nuna hannunsu saitin kofa, da gudu ya fita waje ya'yan hanjinshi sai kaďawa sukeyi,
turus ya tsaya ganin masu aikin gidan da oyizah tsaye kan affan suna kuka jini ko ta'ina a kasa da kanshi,
wani irin ihu alhj basheer yayi haďe da karasawa yana girgizashi yana kuka, da kyar yake iya hado sunan Affan ya kira saboda tashin hankali, daukarshi yayi bai kula da jini da fashewar da tsakiyar kanshi yayi ba ya turashi cikin mota, binshi oyizah tayi tana kuka tace alhj ina zaka kaishi, ya riga fa ya mutu,
alhj basheer ya watso mata ashariyar da baisan yadda akayi ya fadeta ba ya shiga mota yayi asibiti da affan,
likitoci kansu sun tsorata da ganin Affan, wani a cikinsu yace ranka ya dade wannan ay ya mutu,
alhj basheer yayi kanshi yace ubanka ne ya kasheshi? Doctorn yayi baya yace sorry alhj,
nan likitoci sukayi caa akan Affan duk da bawai sun sa ran yana raye ba saidai dan bala'in da alhj basheer ke musu,
Cikin ikon Allah karfe 2 na rana Affan ya fara motsa hannunshi, cikin mamaki doctor musa ya kura ma hannun ido ko gizau yake mishi, ganin ba gizau bane yasa shi fita kiran sauran likitocin cikin murna,
alhj basheer dai binsu yakeyi kamar zararre yana fadin bai mutu ba ko, dr musa ya gyada mishi kai kawai suka wuce dakin da Affan yake,
sai hudu suka fito kowa yayi hanyar office dinshi,
doctr musa ya kalli alhj basheer yace ka kwantar da hankalinka alhj muje office inyi maka bayani,,
alhj basheer ya bishi office din ba tare da ya ce uffan ba,,
Doctor musah ya kalli alhj basheer cikin damuwa yace alhj ka saurareni da kyau kuma duk abinda zan faďa maka kasani bani nayi ba kuma ba wani bane yayi Allah subhanahu wa ta'ala shine ya jarabceka kuma ya jarabci danka, saboda haka dan Allah alhj kayi tawakkali saboda cuta ba mutuwa bace,
alhj basheer ya share hawayen da ya zubo a idonshi yace faďamin komai doctor, fadamin abin da ya sami Affan,, doctor musah ya mika mishi takardun hotunan kwakwalwar da sukayi ma Affan,
ya karba hannunshi na rawa yace bazan gane komai a ciki ba doctor kayi min bayanin komai da baki,
doctor musah yayi ajiyar zuciya yace alhj, Affan ya samu "brain disorder" abin da yabamu mamakin anan shine duk girman ciwo da karfin buguwar nan bashi ya taba kwakwalwar shi ba har yasamu "mental illness" sai wani abun daban,,,,
ya mika mishi wata takarda yace wadannan sune ciwukan da kwakwalwar shi ta samu
"Psychological trauma":
wannan cutar may be triggered by P.T suffered as a child, kamar "severe emotional", physical, or sexual abuse;" abinda ke kawoshi kuma shine, "a significant early loss", kamar the loss of a parent; and neglect...
sai kuma
"Environmental stressors":
"itama ana samunta ne a shock din mutuwa ko macen da aka saka, ko kuma dysfunctional family life,
sacking 4rm jobs or schools, and substance abuse -- it can trigger a disorder in a person who may be at risk for developing a mental illness."
Kaga kenan akwai abinda ya gani ko kuma ya sameshi cikin waďannan abubuwan amma sam ciwon kanshi bai da alaka da cutar,
Alhj basheer cikin tashin hankali yace yanzu doctor kana ganin Affan zai samu lafiya nan kusa,?
doctr musah cikin tausayawa yace sauki na gurin Allah alhj, in yazo yanzu baiyi gaggawa ba sannan in baizo yanzu ba baiyi jinkiri ba saboda Allah ne kadai yake iya bada sauki a lokacin da yaso,
sannan ina tsoron sanar dakai mostly mental illnesses irin wannan are caused by a combination of factors and cannot be prevented so easily, saidai a dage da addu'a saboda babu abin da ya gagari Allah kuma babu wanda yasan gaibu sai Shi..,
da sauri oyizah da tun shigewar su office din doctor ta iso ta juya cikin jin dadin ciwon da taji ya sami Affan da kuma firgicin jin affan nada rai kuma zai iya samun sauki a koda yaushe,
kuma tasan yanzu alhj na dawowa zai fara tambayarta ina zeenatu? Kuma me ya samu Affan me ya gani har ya haddasa mishi wannan cutar,
fita tayi daga asibitin da sauri cikin tsananin tsoron abinda zai je yazo, bata zame ko ina ba sai gurin tsafinsu.....
Mrs tijjani shattima.....
[15/12 09:34] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 2⃣2⃣ By Aysha Ya'u kurah
Alhj basheer ya fito daga office din doctor Musah idonshi jajur saboda kukan da yaci, dakin da aka kwantar da Affan ya shiga ya zauna gefenshi yana zubar da hawaye yana ta tunanin yadda akayi har Affan ya faďo daga wannan saman nisan gaske, to wai ma me Affan ya gani da har ya firgita shi haka,
da sauri ya mike da ya tuno da tun asuba baisa zeenatu a idonshi ba, kuma ace har Affan baida lafiya batazo inda yake ba, girgiza kanshi yayi a fili ko dai wani abu ne ya samu zeenatu, gabanshi ya faďi sosai da ya tuno da kalaman doctor,
jikinshi ya fara rawa ya murda kofar dakin da affan yake ya fita da sauri yana fadin innalillahi a zuciyarshi,
da taimakon Allah ya isa gida, a waje yayi parking motar saboda tashin hankali,
yana shiga ya wuce dakinta,
babu inda bai duba ba a ďakin bai ganta ba, cikin kiďima ya fito yana haďa sunayen mutanen gidan yana kirah da karfi,
da gudu suka firfito, oyizah da bata fi minti 5 da dawowa daga gurin tsafinsu ba ta matso kusa dashi tace lafiya alhj,
ya nuna dakin zeenatu yace ina zeenatu take, fareeda da salma suka ce daddy tun jiya bamu ganta ba,
oyizah tace ni rabona da zeenatu ma ay tun ranar da zaka tafi mukayi maka rakiya,
cikin karaji yace to ina ta shiga,
oyizah ta dafashi tace calm down my dear muje ka huta ka kira can gida kaji ko tana can,
cikin damuwa ya kalli fuskar oyizah, nan ya tsinci kanshi da kasa yi mata musu ya bi bayanta suka wuce gurin dinning,
saida ta bashi abincin da ta haďasu da sinadaran asiri sannan ta zauna gefenshi tana matsa mishi kafa, kallonta yayi har lokacin fuskarshi dauke da damuwa yace safiya ya akayi Affan ya faďo daga wannan saman mai nisa,
sannan me ya faru a gidannan da har ya haddasa tabuwar kwakwalwarshi,
oyizah ta fara share hawayen karya tace alhj nima ban sani ba, kowa na bangarenshi ya za'ayi insan abinda ya faru,
Allah sarki Affan yanzu brain dinshi ya samu matsala,
murya a dashe alhj basheer yace eh safiya, kuma bawai fadowar da yayi bane ya taba brain dinshi, hankali tashe kamar gaske tace to me ya sameshi,
nan ya kwashe abinda doctor ya faďa mishi ya fada mata,
wani irin kuka ta fashe dashi harda zama a dirshan a kasa tana faďin mun shiga uku, yanzu shikenan Affan ya haukace,
alhj basheer ya shiga rarrashinta yana faďin addu'a zamuyi mishi safiya,
dakyar oyizah tayi shuru tace ni alhj babban tashin hankalina shine rashin ganin zeenatu,
Allah yasa ba wasu mugayen bane suka saceta suka wurgo Affan daga sama, hankalin alhj basheer ya tashi da jin furucin oyiza,
ya kalleta yace da zeenatu tayi musu me zasu saceta,
oyizah tace Alhj ka manta muna cikin zamanin da ba sai kayi ma wani komai ba zai maka mugun illah, nidai gobe kabi jirgin safe kabar kulawar Affan a gurina kaje can cameroon ka dubata dan wannan abun yafi karfin waya,
alhj basheer ya share zufar goshinshi yace kin kawo shawara mai kyau safiya, amma--- ta katseshi da sauri tace na fada maka zan kula da Affan fiye da yadda zaka kula dashi, kai dai ka tafi nemanta dan hakkinta na wuyanka,
cikin jindadin tsararrun kalaman oyizah alhj basheer yace nagode sosai safiya, Allah ya kaimu goben, tace ameen yanzu kaje ka kwanta ni zan tafi gurin Affan din in ta kama ma sai in kwana, alhj basheer yaji dadi sosai a ranshi ya dinga shi mata albarka..
Ďaki oyiza ta wuce zuciyarta wasai yanzu gida zai dawo karkashin ikonta,
wani kulli mai kyalli ta kwance ta fito da babyn "Mutum mutumi" an soke kanshi da mashi, Kallon babyn tayi hade da kwashewa da dariya tace Affan kai da warkewa har abada, haka zaka dawwama cikin hauka har ka mutu kamar yadda babyn nan take haka zaka kasance sai yadda nayi dakai,
ta mike ta daga karkashin gadonta inda ta dade da haka wani ramin sihiri ta kara tona gefen ramin ta kira sunan Affan sau uku sannan ta tura babyn ciki tana dariyar mugunta,
ta kalli wata laya ta kara saka wata dariyar tace wannan naki ne zeenatu, ba yanzu zanyi aikin ba sai an gaji da nemanki, ta mayar da layar cikin daurinta sannan ta loda magunguna hade da turarukan tsafi a jakarta ta shirya wucewa asibitin..
a hankali ya buďe idonshi yaji bugun kofar da ake ma ďakinshi yaki tsagaitawa, da sauri ya diro daga kan gado jikinshi na rawa ya bude kofar,
Salma da farida ya gani tsaye suna ihu suna kuka suka ce daddy Affan-- Da sauri ya katsesu yace me yasamu Affan din, kasa bashi amsa sukayi sunata nuna hannunsu saitin kofa, da gudu ya fita waje ya'yan hanjinshi sai kaďawa sukeyi,
turus ya tsaya ganin masu aikin gidan da oyizah tsaye kan affan suna kuka jini ko ta'ina a kasa da kanshi,
wani irin ihu alhj basheer yayi haďe da karasawa yana girgizashi yana kuka, da kyar yake iya hado sunan Affan ya kira saboda tashin hankali, daukarshi yayi bai kula da jini da fashewar da tsakiyar kanshi yayi ba ya turashi cikin mota, binshi oyizah tayi tana kuka tace alhj ina zaka kaishi, ya riga fa ya mutu,
alhj basheer ya watso mata ashariyar da baisan yadda akayi ya fadeta ba ya shiga mota yayi asibiti da affan,
likitoci kansu sun tsorata da ganin Affan, wani a cikinsu yace ranka ya dade wannan ay ya mutu,
alhj basheer yayi kanshi yace ubanka ne ya kasheshi? Doctorn yayi baya yace sorry alhj,
nan likitoci sukayi caa akan Affan duk da bawai sun sa ran yana raye ba saidai dan bala'in da alhj basheer ke musu,
Cikin ikon Allah karfe 2 na rana Affan ya fara motsa hannunshi, cikin mamaki doctor musa ya kura ma hannun ido ko gizau yake mishi, ganin ba gizau bane yasa shi fita kiran sauran likitocin cikin murna,
alhj basheer dai binsu yakeyi kamar zararre yana fadin bai mutu ba ko, dr musa ya gyada mishi kai kawai suka wuce dakin da Affan yake,
sai hudu suka fito kowa yayi hanyar office dinshi,
doctr musa ya kalli alhj basheer yace ka kwantar da hankalinka alhj muje office inyi maka bayani,,
alhj basheer ya bishi office din ba tare da ya ce uffan ba,,
Doctor musah ya kalli alhj basheer cikin damuwa yace alhj ka saurareni da kyau kuma duk abinda zan faďa maka kasani bani nayi ba kuma ba wani bane yayi Allah subhanahu wa ta'ala shine ya jarabceka kuma ya jarabci danka, saboda haka dan Allah alhj kayi tawakkali saboda cuta ba mutuwa bace,
alhj basheer ya share hawayen da ya zubo a idonshi yace faďamin komai doctor, fadamin abin da ya sami Affan,, doctor musah ya mika mishi takardun hotunan kwakwalwar da sukayi ma Affan,
ya karba hannunshi na rawa yace bazan gane komai a ciki ba doctor kayi min bayanin komai da baki,
doctor musah yayi ajiyar zuciya yace alhj, Affan ya samu "brain disorder" abin da yabamu mamakin anan shine duk girman ciwo da karfin buguwar nan bashi ya taba kwakwalwar shi ba har yasamu "mental illness" sai wani abun daban,,,,
ya mika mishi wata takarda yace wadannan sune ciwukan da kwakwalwar shi ta samu
"Psychological trauma":
wannan cutar may be triggered by P.T suffered as a child, kamar "severe emotional", physical, or sexual abuse;" abinda ke kawoshi kuma shine, "a significant early loss", kamar the loss of a parent; and neglect...
sai kuma
"Environmental stressors":
"itama ana samunta ne a shock din mutuwa ko macen da aka saka, ko kuma dysfunctional family life,
sacking 4rm jobs or schools, and substance abuse -- it can trigger a disorder in a person who may be at risk for developing a mental illness."
Kaga kenan akwai abinda ya gani ko kuma ya sameshi cikin waďannan abubuwan amma sam ciwon kanshi bai da alaka da cutar,
Alhj basheer cikin tashin hankali yace yanzu doctor kana ganin Affan zai samu lafiya nan kusa,?
doctr musah cikin tausayawa yace sauki na gurin Allah alhj, in yazo yanzu baiyi gaggawa ba sannan in baizo yanzu ba baiyi jinkiri ba saboda Allah ne kadai yake iya bada sauki a lokacin da yaso,
sannan ina tsoron sanar dakai mostly mental illnesses irin wannan are caused by a combination of factors and cannot be prevented so easily, saidai a dage da addu'a saboda babu abin da ya gagari Allah kuma babu wanda yasan gaibu sai Shi..,
da sauri oyizah da tun shigewar su office din doctor ta iso ta juya cikin jin dadin ciwon da taji ya sami Affan da kuma firgicin jin affan nada rai kuma zai iya samun sauki a koda yaushe,
kuma tasan yanzu alhj na dawowa zai fara tambayarta ina zeenatu? Kuma me ya samu Affan me ya gani har ya haddasa mishi wannan cutar,
fita tayi daga asibitin da sauri cikin tsananin tsoron abinda zai je yazo, bata zame ko ina ba sai gurin tsafinsu.....
Mrs tijjani shattima.....
[15/12 09:34] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 2⃣2⃣ By Aysha Ya'u kurah
Alhj basheer ya fito daga office din doctor Musah idonshi jajur saboda kukan da yaci, dakin da aka kwantar da Affan ya shiga ya zauna gefenshi yana zubar da hawaye yana ta tunanin yadda akayi har Affan ya faďo daga wannan saman nisan gaske, to wai ma me Affan ya gani da har ya firgita shi haka,
da sauri ya mike da ya tuno da tun asuba baisa zeenatu a idonshi ba, kuma ace har Affan baida lafiya batazo inda yake ba, girgiza kanshi yayi a fili ko dai wani abu ne ya samu zeenatu, gabanshi ya faďi sosai da ya tuno da kalaman doctor,
jikinshi ya fara rawa ya murda kofar dakin da affan yake ya fita da sauri yana fadin innalillahi a zuciyarshi,
da taimakon Allah ya isa gida, a waje yayi parking motar saboda tashin hankali,
yana shiga ya wuce dakinta,
babu inda bai duba ba a ďakin bai ganta ba, cikin kiďima ya fito yana haďa sunayen mutanen gidan yana kirah da karfi,
da gudu suka firfito, oyizah da bata fi minti 5 da dawowa daga gurin tsafinsu ba ta matso kusa dashi tace lafiya alhj,
ya nuna dakin zeenatu yace ina zeenatu take, fareeda da salma suka ce daddy tun jiya bamu ganta ba,
oyizah tace ni rabona da zeenatu ma ay tun ranar da zaka tafi mukayi maka rakiya,
cikin karaji yace to ina ta shiga,
oyizah ta dafashi tace calm down my dear muje ka huta ka kira can gida kaji ko tana can,
cikin damuwa ya kalli fuskar oyizah, nan ya tsinci kanshi da kasa yi mata musu ya bi bayanta suka wuce gurin dinning,
saida ta bashi abincin da ta haďasu da sinadaran asiri sannan ta zauna gefenshi tana matsa mishi kafa, kallonta yayi har lokacin fuskarshi dauke da damuwa yace safiya ya akayi Affan ya faďo daga wannan saman mai nisa,
sannan me ya faru a gidannan da har ya haddasa tabuwar kwakwalwarshi,
oyizah ta fara share hawayen karya tace alhj nima ban sani ba, kowa na bangarenshi ya za'ayi insan abinda ya faru,
Allah sarki Affan yanzu brain dinshi ya samu matsala,
murya a dashe alhj basheer yace eh safiya, kuma bawai fadowar da yayi bane ya taba brain dinshi, hankali tashe kamar gaske tace to me ya sameshi,
nan ya kwashe abinda doctor ya faďa mishi ya fada mata,
wani irin kuka ta fashe dashi harda zama a dirshan a kasa tana faďin mun shiga uku, yanzu shikenan Affan ya haukace,
alhj basheer ya shiga rarrashinta yana faďin addu'a zamuyi mishi safiya,
dakyar oyizah tayi shuru tace ni alhj babban tashin hankalina shine rashin ganin zeenatu,
Allah yasa ba wasu mugayen bane suka saceta suka wurgo Affan daga sama, hankalin alhj basheer ya tashi da jin furucin oyiza,
ya kalleta yace da zeenatu tayi musu me zasu saceta,
oyizah tace Alhj ka manta muna cikin zamanin da ba sai kayi ma wani komai ba zai maka mugun illah, nidai gobe kabi jirgin safe kabar kulawar Affan a gurina kaje can cameroon ka dubata dan wannan abun yafi karfin waya,
alhj basheer ya share zufar goshinshi yace kin kawo shawara mai kyau safiya, amma--- ta katseshi da sauri tace na fada maka zan kula da Affan fiye da yadda zaka kula dashi, kai dai ka tafi nemanta dan hakkinta na wuyanka,
cikin jindadin tsararrun kalaman oyizah alhj basheer yace nagode sosai safiya, Allah ya kaimu goben, tace ameen yanzu kaje ka kwanta ni zan tafi gurin Affan din in ta kama ma sai in kwana, alhj basheer yaji dadi sosai a ranshi ya dinga shi mata albarka..
Ďaki oyiza ta wuce zuciyarta wasai yanzu gida zai dawo karkashin ikonta,
wani kulli mai kyalli ta kwance ta fito da babyn "Mutum mutumi" an soke kanshi da mashi, Kallon babyn tayi hade da kwashewa da dariya tace Affan kai da warkewa har abada, haka zaka dawwama cikin hauka har ka mutu kamar yadda babyn nan take haka zaka kasance sai yadda nayi dakai,
ta mike ta daga karkashin gadonta inda ta dade da haka wani ramin sihiri ta kara tona gefen ramin ta kira sunan Affan sau uku sannan ta tura babyn ciki tana dariyar mugunta,
ta kalli wata laya ta kara saka wata dariyar tace wannan naki ne zeenatu, ba yanzu zanyi aikin ba sai an gaji da nemanki, ta mayar da layar cikin daurinta sannan ta loda magunguna hade da turarukan tsafi a jakarta ta shirya wucewa asibitin..